ABDUL JALAL

1K 46 11
                                    

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹

*ABDUL JALAL*

_Story, writing and edited _

By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞

(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A*✍️

PART 2
_PAGE 6️⃣3️⃣117

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

     

              _MY FIRST NOVEL _

Ajiye wayar Jalal yayi tare da dafe kansa yayi shiru, Jalila tace "me yake damunka ne, Ina fatan dai lafiya ko?"

Cikin damuwa yace "Mummy ce ta kirani wai lallai in koma tana son ganina, Akwai abunda taji yana shirin faruwa akan dukiya ta"

"Subhanallah Allah yasa dai lafiya? Yaushe zamu koma kenan?"

"ba inda zani" Jalal ya bata amsa

"Saboda me? Kiran mahaifiyarka ne fa"

"Nasani Jalila nasan akan abunda take magana, indai zan biye wa Mummy bazan taɓa abun Arziki a rayuwa ta ba, shiyasa bana son raɓarta komai nata na son kanta ne"

Jalila cikin sigar rarrashi tace "Jalal me yasa kake me tausasawa ga wasu can bare amma baka iya tausasa wa mahaifiyarka, duk wanda yakamata ya more ka a bayan ta yake, kayi haƙuri da yadda Allah yayi ta ka cigaba da yi mata Addu'a wataran se labari, kai ka ɗai ne ɗan da ta mallaka, be kamata a ce kana mata irin wannan halayen ba"

Kaman ze kuka cike da zuciya da ɓacin rai yace "nika ɗai take dani, kuma nika ɗai take azabtarwa"

"Jalal ya za'ayi mahaifiyar ka ta haife ka sannan kace tana azabtar da kai, baka fahimce ta bane....

" Enough Jalila kidena pretending kaman baki san komai ba mana, Jalila bana jin daɗin Alaƙata da mahaifiya ta, ina kulle kaina inyi kuka da hawaye na saboda rashin soyayya da kulawar mahaifiya, ban san jin ƙai na tsakanin ɗa da uwa ba, kullum tunanin Mummy burin ta kowa ni abu da take hange ya cika, bata tunani makoma ta, duk lokacin da nayi niyyar in shiga jikin mahaifiya ta in bata kulawar da zan iya, se ta bijiromin da wani abu da yake saɓanin tunani, me yasa yaushe Mummy za ta gane inda rayuwa ta dosa,? shi kansa Daddy yanzu bata gaban sa, shekaru talatin da uku yana haƙuri, Jalila har yanzu ina ganin lokacin da mahaifiyar Daddy ke zubar da hawaye saboda halayen mahaifiya ta yaushe Mummy zata canza tunanin ta se yaushe? Yaushe zata gane mutunci da soyayya gaba suke da dukiya? "

Jalal ya ɗau zafi sosai dan har jijiyoyin kansa sun fara miƙewa ya zuciya da yawa.
Ƙara matsowa kusa da shi Jalila tayi tace
"Jalal a duk lokacin da mutane zasu zauna da junansu ba dan Allah bato tabbas wannan zama ba shi da wani amfani, wanda suka zauna da Mummy a baya ba masu ƙaunarta bane, masu son abun hannunta ne, Baka tunanin in kayi haƙuri da ita kai mata biyayya a hankali ta shiryu? Rayuwarmu da mukayi a baya da wadda muke da kai a yanzu misali ce a gareka, Jalal baka da uzuri a gurin ubangiji idan ka mutu kana ɓatawa mahaifiyar ka rai, abubuwan da tayi tsakanin ta da Allah ne, Amma kai zaka yi aikin gyara halayen Mummy idan kaso"

Default Title - ABDUL JALAL (2020) Where stories live. Discover now