ABDUL JALAL 111

1.1K 28 2
                                    

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹

*ABDUL JALAL*

_Story, writing and edited _

By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞

(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A*✍️

PART 2
_PAGE 5️⃣7️⃣110

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

_MY FIRST NOVEL _

Washegari tun safe Jalila take shiri tana murnar zata je gida, gefe guda tana tunanin in taje dole ne taje ta gaida iyayen Jalal, ko wane tarba Mummy zatayi mata oho? Ga abunda ya faru da su Sa'adah har yanzu abun yana damun ta sosai, karfe goma na safe ta kammala shiryawa tsaf, ta hada kayanta, tun dare ta hadawa Jalal nasa kayan shima wanda zeyi tafiya dasu Lagos.

Jalal ma ya fito tsaf da shi, Jalila ta kulle ko ina, Jalal kuma yafita da akwatunan su, a mota taje ta tarar da shi ita kawai yake jira, ta bude ta shiga ta zauna, ya kalleta yace

"Baby ya dai naga duk jikinki a sanyaye?"

"bakomai fa" ta bashi amsa

"shikenan tunda bazaki gayamin ba"

Ya kunna motar suka tafi, koda yaje unguwar su yayi parking kin fitowa tayi daga motar, ya kalleta yace

"Fito mana, ni nakasa gane meyake damunki ne?"

Jiki ba kwari ta fito daga motar, Jalal yace

"muje in gaida su Abba, daga baya sekije ki gaida Daddy"

jinjina masa kai kawai tayi tabi shi, suna shiga cikin gidan kofar parloun a rufe take, Jalila ta dakko wayarta ta kira Maama, bugu daya Maama ta dauka Jalila tace

"Maama ina kika tafine, ina gida amma kofan parlor a rufe"

Maama tace

"ya salam, ai ban dauka da wuri zakuzo ba, kinga mun dan fita da Abba ne, yanzun nan zamu dawo insha Allah"

"shikenan se kun dawo" ta kashe wayar ta kalli Jalal tace

"basa nan wai yanzu zasu dawo"

Jalal yace "shikenan zomuje gida seki jira su"

Dan shiru Jalila tayi tana kallon Jalal.

"kina tsoron Mummy ne? Karki damu ba abunda ze faru muna tare, muje"

Jiki a sanyaye tabi bayansa danji take kaman tace bazata ba, tasan bazeji dadi ba idan tayi hakan, gabanta nata faduwa tana karanta addu'oi daban2, tun daga harabar gidan har cikin parlor ba kowa part din daddy ya nufa tana biye da shi, suna shiga suka tarar da Daddy na zaune na kallon labarai su Jalal sukayi sallama, ya amsa tare da waigowa, yana ganin su ya fadada murmushinsa tare da dan bude baki, ganin Yadda Jalal yazama wani babban mutum.

Default Title - ABDUL JALAL (2020) Donde viven las historias. Descúbrelo ahora