ABDUL JALAL 102

1.4K 18 1
                                    

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹

*ABDUL JALAL*

_Story, writing and edited _

By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞

(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A*✍️

PART 2
_PAGE 4️⃣9️⃣102

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

_MY FIRST NOVEL _

Jalal ya dago yana kallon Jalila, cikin kuka Jalila tace

"Innalillahi wa inna ilaihi raji un, Abba me yasa? Laifin me nayi a kayimin haka?"

Abba yace
"kwantar da hankalinki, nasan bazaki watsa min kasa a ido ba, ba laifin da kikayi, ganin da cewar hakan mukayi shiyasa muka yanke wannan hukuncin"

Girgiza kai ta shiga yi tana kuka, daddyn Hanan yace

"Calm down my daughter, kinga bakida lafiya, meye abun damuwa? Jalal ne kin sanshi ba wani aka Aura miki wanda baki sani ba, bakomai kiyi hakuri, Allah yabaku zaman lafiya, Kuma nasan kina sonshi ai ko?"
Girgiza kai tayi da sauri tace

"Ni wallahi bana sonshi, Allah bana sonshi haba daddy, duk 'yan uwana ba wanda akayiwa haka seni, daddy Why? Wallahi ni ba son Jalal nake ba tausayin sa kawai nakeji"
Abba yace

"ba cinya ba kafar baya"
Daddy yace
"to wa kike so"?

"Ni Ahmad nakeso" ta fada kanta tsaye tana kuka.

Jalal yasan za' a rina, yasan setayi daru, Amma be taba zaton Jalila zata iya furta bata sonsa ba agabansa haka"
Mummy tace

"Ke rufewa mutane baki, kaunar da'ake miki yasa aka zaba miki Jalal din, in kun zauna zakiji son, kar in kara jin wannan maganar a bakinki, Ahmad yana da mata, ko yanzu yaga dama ze iya neman wadda yakeso a bashi, kamar yadda kikace tausayin Jalal kike, to kiyi hakuri kicigaba da tausayin sa"

Maama kanta jikinta yayi sanyi, seda ta bada shawarar a ji ta bakin Jalila kafin a yanke wannan hukuncin amma basu bi shawarar ta ba..

Jalila ta mike da sauri ta fice daga palourn tana kuka.
Baban Hanan yace

"Jalal sekayi hakuri, kasan yarinya ce karama, kuma an shammace ta, ba zato ba tsammani aka daura mata Aure, kuma tana ganin duk 'yan uwanta su suka kawo wanda suke so, kayi hakuri da abubuwan dazata yi maka ze wuce kamar ba'ayi ba, gata nan Amana ka rike ta da amana"

Sallamar Hajiya Salma, da kannen Mahifin Jalal, da shi kansa daddyn Jalal, ya katse wa Daddyn Hanan maganar da yakeyi, suka amsa musu sallamar.
Suka karaso suka zauna, daddy yafara magana
"Dukkan yabo da godiya da jinjina da kirari sun tabatta ga ubangiji ma daukakin sarki, me kowa komai, Alhamdilillah anyi taro lafiya an gama lafiya, muna fatan Allah yasa anyi kenan, Allah yabasu zaman lafiya, sannan Alhaji Usman, bazan gaza gurin kuma nuna godiya ga dawainiyar da iyalanka suka dingayi da ďana ba har kawo wannan lokacin da kukayi masa ko ince kuka yimana wannan karamcin, iyalanka sun Rungumeshi lokacin da mutane kowa ke gudun sa, Mungode mungode Allah yasaka da alkhairi, Allah yabiya ku da gidan Aljannah ya jikan magabata, Kuma Insha Allah bazamu baku kunya ba"

Default Title - ABDUL JALAL (2020) Where stories live. Discover now