ABDUL JALAL 74..

289 8 1
                                    

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹

_ABDUL JALAL (2020)_

_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)

PART 2
_PAGE 2️⃣1️⃣74

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com



_MY FIRST NOVEL_

"haba khadija, yanzu dan sunnan zakice zaki zubarmin, ina son yara sosai, ki haifamin ko dayane seki tafi karatunki bazan hanakiba, mama tana matukar son yara, tanason jikoki, dan Allah kibari ki haifamin"
Mikewa tayi ta shige toilet tabarshi a gurin a zaune. Tana shiga bandaki tayi tsaki tace "in maman nason yara, se itama ta haifa aiba abun kunya bane, aikin banza nibahakane yakawoni ba"
"ikon Allah Salma nata nema ido rufe tana Addu'a, itakuma Allah yabata zata zubar"
Haka Habib yaita fama da Khadija, a haka har yakoma Dubai, ta shirya ta tafi gidansu sunyi murna sosai da ganinta, khadija tanada kyauta tanayu musu aike sosai, kama daga Abinci sutura da kudi, amma idan Habib yayi niyyar yiwa yan uwansa kona Salma wani abu, indai tasani seta hanashi, amma itakuma ta nayiwa yan gidansu.
Ranar dataje gida seda ta tsorata dataga Saudat tayi rama matuka, tayu duhu duk wannan kwalisar babu, har cikin ranta taji babu dadi yanayin dataga Saudat, dan haka ta dan damu, daki tabi Saudat tacewa sauran kanensu sufita subasu guri, b musu kowa ya watse, tazo kusada Saudat ta zauna ta kalleta tace "yar uwata, meyake damunki haka? Saudat kinga yadda kikakoma kuwa?"
Tsaki Saudat tayi, ta juya mata baya
"Saudat nasan ban kyauta mikiba, amma rayuwa bazata tafi a hakaba, kisani dama can Allah be rubuta Habib mijinki baneba, idan kika cigaba da wannan rayuwar tozaki kashe kanki a banza ne, tunda kinsan Bazaki samu Habib ba, Saudat inaso mucigaba da zumuncinmu, kimanta da abunda yafaru ki karbi kaddararki, Allah yafito miki da miji, indai kudine Saudat duk abunda kikeso zanmikishi Insha Allah" mikewa zaune Saudat tayi ta kalli Khadija
"Zumunci nidake har abada wallahi, kin riga kin rusa alakar dake tsakanina dake, ke kinama yaudarar kanki ne da kike cewa wai mukoma kaman da, naji tawa kaddarar kenan da tasameni a sanadinki, kema ki saurari taki kaddarar, malama ki tashi kibaani guri, ficemin a daki"
"Saudat nikike kora haka?"
"na korekin ko uwata ce tamin abunda kikayi min sena rama, dalla malama fita munafuka"
"shikenan tunda haka kika ce, inkika dawo hayyacinki zaki gane me nake nufi" khadija ta mike ta bar dakin.

Bayan tafiyar Habib da yan kwanaki khadija Taje chemist tace subata maganin abortion, me chemist din yace shi gaskiya baya irin wannan harkar, take ta zube masa uwar kudi, take jiki na rawa yabata magani da yadda zata bi cikin ya zube, ta dauki maganinta ta tafi gida, yadda yace mata haka tayi amfani dashi, aikuwa ba adau wani lokaci ba mararta ta dinga ciwo wuni tayi tana murkususu a haka har seda cikin nan ya fita, tasha wahala matuka, gashi ba wanda tagayawa, ko Salma da suke zaune gida daya bata mata magana, haka tai wahalarta ita kadai ta gama.
Saboda daukin cikin da Habib yakeyi, sati uku yayi ya dawo gida, gurin khadija yafara sauka, se wani sabon kalan soyayya yake nuna mata sabida duk zatonsa cikin yana nan.
Da daddare yana cin Abinci shida khadija, ya kalleta yace "cwt Deejah, Wani suna kikeso musakawa babynmu inkin haihu, ina son in sanarwa su yaya hajjo, cewar munsamu rabo, ko baby" dan ya tsina baki tayi
"mhmm kaga dakabar wannan batun gayawa mutane ansamu rabo, bayan tafiyarka na fadi a toilet cikin ya zube, ban gayamaka bane saboda kar hankalinka ya tashi"
Abincin daya hadiya ne yaji ya makale masa a makogwaro yaki wucewa,
"kin zubarmin da ciki ko khadija?"
"niba zubarwa nayi ba zu.....
" Shut up!!! "
Yafada cikin tsawa da sedata razana
" saboda kin rainamin hankali kike cewa zubewa yayi, wato baki hakura ba shine kika zubarmin da ciki, dan kinga ina lallaba ki ko? Nikikayiwa haka ko? Har innuna miki abunda nakeso amma ki shure kiyi son ranki, kin zubar Minda ciki nagode "
"Ahhh Hayatee wallahi.....
" yimin shiru"
Ya katseta, ya tashi ya dau wayoyinsa yabar palourn, dafe kai tayi bata taba tunanin Habib ya iya fada haka ba, saboda gaba dayansa silent ne, bashida hayaniya sam. Amma fushinsa baze hanata cinma burinta na rayuwa ba.
Wasa2 tunda yabar part dinta seda yai sati guda bata ganshi ba, ko ta waya, dan haka ta shirya ta nufi part din Salma, tana zuwa ta tarar Salma na kitchen tana girki batabi takan Salma ba ta nufi palour na biyu,
"lafiya zaki shigomin ba sallama ki wucemin daki?"
"ba ruwanki ba gurinki nazo ba" ta shige tabar Salma a gurin, tana shiga kuwa ta tarar da Habib a palourn yana karanta jarida, karasawa tayi ta zauna kusada shi
"Hayatee kwana bakwai banganka ba, meyasa dana gayamaka abunda yafaru baka yadda daniba" shiru yayi yaki dagowa ya kalleta, hannunsa ta riko ya dago a fusace
Amma seyaga fuskarta sharkaf da hawaye, nan take jikinsa yayi sanyi
"Hayatee, duk lokacin danakiraka Hayatee i mean it har cikin raina kai rayuwata ne, meyasa ka karyatani baka yadda bani na zubar maka da ciki ba, inason abunda kakeso tsautsayine ya gifta cikin ya zube dan Allah kayi hakuri" ta zube akan gwiwoyinta tana kuka, hannu yasa ya dagota ya rungumeta yana share mata hawaye
"is ok am sorry my deejat, ya wuce kidena kuka" a hankali tace "I miss you Hayatee, dan Allah karka kara fushi dani haka"
"I miss you too baby, bazan kuma ba"
Khadija yar duniya ce yanzu kana zaune zata siyeka.
ganin shirun yayi yawa yasa a fusace Salma tanufo palourn, Amma abunda idonta ya gane mata yasata ja da baya da sauri, jitayi kaman andoramata dutse a zuciyarta, kitchen takoma ta toshe bakinta tana kuka, tanaji tana gani anzo har cikin gidanta an kwace mata miji.

Default Title - ABDUL JALAL (2020) Where stories live. Discover now