ABDUL JALAL 110

1K 21 0
                                    

 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹

*ABDUL JALAL*

_Story, writing and edited _

By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞

(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A*✍️

PART 2
_PAGE 5️⃣6️⃣109

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

     

Happy marriage lyf to you sister Amina, may yours be among the best.

              _MY FIRST NOVEL _

Mmurmushi Jalila tayi tace

"Masha Allah naji dadi gaskiya, dama bana zuwa ko'ina daga makaranta se gida, gashi an gayyaceni biki 'yar class dinmu bansaniba ko zaka barni inje?"

Dan hade rai yayi yai mata shiru,

Tace "Kace wani abu mana"

"gaskiya bazaki ba" yaba ta amsa

A shagwabe tace "meyasa?"

Jalal yace

"har yanzu baki kama da me Aure ba, kawai kifita wani ya biyoki no gaskiya ki hakura"

Kara marairacewa tayi tace

"please, Allah tunda nazo gidan nan school kawai nake zuwa, dan Allah ka barni inje"

Makale kafada yayi "yace ni dai A'a"

Ya kalli cikin idonta yace

"Allah me yadda yaso, Baby da dane nace karki fita ko kallona bazakiyi ba, ko baki niyya ba sekin fita dan ki ban haushi ko?"

Shiru tayi ba tace komai ba

Jalal yace

"naji zakije, amma ni zan rakaki kiyi minti goma mu dawo, dan bazaki dade ba, kar inje wani ya kalleki koma wani ya biyoki yace yana so, tunda har yanzu baki gama amsa sunan matar Aure ba"

Dan kallonsa tayi tace

"saboda me? A gaban mutane fa aka daura min Aure"

"eh nasani mana an daura miki Aure, har kikace ba kya son mijin da'aka baki, Amma ai bakiyi daya karatun ba daze maida ke matar Aure, ina da dauriya ko Jalila? Akwai dalilina dayasa na kyaleki kike cin karenki ba babbaka, ina jiran time ne"

Yai maganar yana kashe mata ido daya, sarai Jalila ta gane meyake nufi Amma ta maze tace

"karatu kuma? Wane irin karatu ne kuma haka?"

Jalal yace

"Au baki gane karatun da nake nufi ba?"

Mikewa yayi zaune yace

Default Title - ABDUL JALAL (2020) Where stories live. Discover now