ABDUL JALAL (2020)

Magsimula sa umpisa
                                    

Daga office dinsa ya dinga jiyo hayaniyar  Jalila ta dawo daga ajin dake gaban office dinsa
Tsaki ya ja ya kalli dayan malamin
"Aifa bismillahi wannan baki abun maganar ta dawo yanzu bamu da sakat saboda surutun dalibai"
Daya malamin ne ya kalleshi
"Lallai kam malam naziru indai Jalilace baki abun magana, ga surutu ga Neman magana, inda take birgeni kwakwalwarta tana Ja sosai, kuma duk tsiwarta intai laifi akwai bada hakuri"

"Hmm kaidai bari kawai idan nafara lissafo maka halin yarinyar nan ai se dai addu'a"
Murmushi daya malamin yayi sukayi musabiha ya bar office din
Mamakine ya cika shi kodai kunnensa beji dai² ba yaji ana Jalila ta dawo amma yaji ajin shiru kaman an cinyesu se Dan surutu da suke kasa²
  Har yayi gaba ya dawo ya leka Ajin aikuwa itance amma fuskarta Sam ba walwala ta koma gefe tayi shiru se Siyama dake gefenta tana mata magana
Kai tsaye ya dawo kofa ya shiga ajin gaba daya suka nutsu
"Baku San me yakawoku nan bane Ku dakko Qur'anin Ku kufara tilawa,"
Ya kai dubansa kan Jalila
"Ke yau kwananki kusan goma bakizo makaranta ba, kuma baki bada wani uzuri ba"
Siyama tai saurin cewa
"Malam Naziru nafa gaya maka.."
"Ke rufemin baki marasa da'a ina magana zaki katseni"

Ya maida dubansa ga Jalila
"in anjima zanzo karbar hadda duk na kwanna Goman nan sekin bani haddasu
Kukama Ku dakko Qur'anin Ku nace"
Kowacce kokarin dakko Qur'anin Sa yake banda Jalila wadda kamar an dasata
"Ke ina naki Al Qur'anin"?
Ya dakamata tsawa
Qur'anin hannun Siyama ta nuna masa
Ya kalli siyama " ke ina naki?"
Itama Qur'anin ta nuna masa "rainamin hankali zakuyi kenan?"

Fita yayi be dade ba se gashi da wata katuwar dorina yana zuwa ya fara takan Siyama ya zaneta sannan ya nufo inda Jalila take
Zumbur ta mike ta fara ja da baya
"Dawo nan ki tsaya, fara bani haddar yanzu zan karba"
Yafada yana muzurai yana nuna mata gabansa
"Ni wallahi banyi haddan nan ba kuma in kada keni da wannan bulalan suma zanyi"
  "Ai ko mutuwa zakiyi yau sena zaneki Dan kun rainamin hankali wai Qur'anin Ku daya Ku biyu"
Aikuwa Jalila ta dage ta kwala ihu tare da fadin
"Malam babba kazo ka temakeni, danka ze kasheni, za a daki amanarka Dan Allah kazo"

Daga ajin da dattijon yake zaune yana biyawa dalibai karatu ya jiyo ihunta tana kiran sunansa
Malam babba shine mamallakin makarantar malam, Naziru kuma dansa ne dabasa jituwa da Jalila
Wataran ya daketa tayi suman karya, aka kaita Gida lokacin Abban su Jawwad yazo, hankalinsa ya tashi sosai yazo har makarantar ya samu malam  babba akan dukan da akayiwa Jalila yayi yawa, malam babba yaita bashi hakuri, shine Abban Jawwad   "yace malam ga yata nan Amana dan Allah a hannunka marainiya CE adinga hakuri da halinta"
shikuma yace ya karba, indai za a daketa har cikin zuciyarsa yakeji bayason kukanta
Itakuma Allah be hada jininta da malam Naziru ba, kusan kullum Seya nemi abinda zesa ya daketa

Tashi yayi da sauri ya taho ajin dayake jiyo ihunta yaganta ta makale a lungun ajin tanata kuka ga kuma malam Naziru a tsaye da bulala
"Naziru lafiya nakejin kukan 'yata"
Nan malam Naziru ya shiga gayamasa abunda akayi da Wanda ba ayiba
"To ina nema mata afuwa bana son ana samun ita kuka dukda Yar tawa tafiye Jan magana"

Gyada kai malam Naziru yayi ya fita daga ajin zuciyarsa fal bakin cikin rashin Zane yarinyar nan.
Malam babba ya hada litattafan makaranta yabawa Jalila sannan yace ze aikomata da Jakar makaranta

Itakam siyama har aka tashi daga Islamiyya kukan dukan da akayi mata take Dan tana tsoron bulala, mafi akasari in Jalila tai lefi akanta abun yake karewa.
Da aka tashi Har Gida Jalila ta  raka siyama tana ta bata hakuri

Kwana biyu  Jalila tacigaba da harkokinta hankalinta kwance amma data tuna mafarkin nan se ta ji jikinta yayi sanyi
Tana kwance a dakinta gidan bakowa tanata tunani bacci ya kwasheta Ummi bata nan ta tafi kasuwa

Jeje ne zaune yana ta busa shisha, shikuma Jalal yasaka Bluetooth a kunnensa ya jingina da kujerar da yake kai
Jeje yadan taba shi alamar yanason zeyi magana da shi cire Bluetooth din kunnensa yayi yana kallon Jeje alamun ina jinka
Jeje yai gyaran murya
"Man wai ya batun tafiyarmu Dubai ne naji ka shiru"

Default Title - ABDUL JALAL (2020) Tahanan ng mga kuwento. Tumuklas ngayon