Default Title - ABDUL JALAL (...

By Ayshercool7724

56.5K 2.5K 216

Labarin wani matashi daya riga ya gurbata rayuwarsa da shaye2 da raina iyayensa, tareda wata matashiyar yarin... More

Abdul Jalal(2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 7
ABDUL JALAL (2020) 8
ABDUL JALAL (2020) 9
ABDUL JALAL (2020) 10
ABDUL JALAL (2020) 11
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 15
ABDUL JALAL (2020) 16
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 19
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 21
ABDUL JALAL (2020) 22
ABDUL JALAL (2020) 25
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 27
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 30
ABDUL JALAL (2020) 31
ABDUL JALAL (2020) 32
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 35
ABDUL JALAL (2020) 35
ABDUL JALAL (2020) 36
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 38
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 43
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 43
ABDUL JALAL (2020) 44
ABDUL JALAL (2020) 45
ABDUL JALAL (2020) 46
ABDUL JALAL (2020) 48
ABDUL JALAL (2020) 48
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 50
ABDUL JALAL (2020) 51
.ABDUL JALAL (2020) 53
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL part 2
part 2 55
ABDUL JALAL (2020) 56
ABDUL JALAL 57
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 59
ABDUL JALAL 60
ABDUL JALAL 61
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 63
ABDUL JALAL 64
ABDUL JALAL 65
ABDUL JALAL 66
ABDUL JALAL 67
ABDUL JALAL 68
ABDUL JALAL 69
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 72
ABDUL JALAL 73
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 74..
ABDUL JALAL 75
ABDUL JALAL 76
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 78
ABDUL JALAL 79
ABDUL JALAL 80
ABDUL JALAL 81
ABDUL JALAL 82
ABDUL JALAL 83
ABDUL JALAL 84
ABDUL JALAL 85
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 88
ABDUL JALAL (2020) 89
ABDUL JALAL 90
ABDUL JALAL 91
ABDUL JALAL 92
ABDUL JALAL 93
ABDUL JALAL 94
ABDUL JALAL 95
ABDUL JALAL 96
ABDUL JALAL 97
ABDUL JALAL 98
ABDUL JALAL 99
ABDUL JALAL 100
ABDUL JALAL 101
ABDUL JALAL 102
ABDUL JALAL 103
ABDUL JALAL 104
ABDUL JALAL 105
ABDUL JALAL 106
ABDUL JALAL 107
ABDUL JALAL 108
ABDUL JALAL 109
ABDUL JALAL 110
ABDUL JALAL 112
ABDUL JALAL 113
ABDUL JALAL 114
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL

ABDUL JALAL 111

1.1K 28 2
By Ayshercool7724

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹

*ABDUL JALAL*

_Story, writing and edited _

By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞

(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A*✍️

PART 2
_PAGE 5️⃣7️⃣110

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

_MY FIRST NOVEL _

Washegari tun safe Jalila take shiri tana murnar zata je gida, gefe guda tana tunanin in taje dole ne taje ta gaida iyayen Jalal, ko wane tarba Mummy zatayi mata oho? Ga abunda ya faru da su Sa'adah har yanzu abun yana damun ta sosai, karfe goma na safe ta kammala shiryawa tsaf, ta hada kayanta, tun dare ta hadawa Jalal nasa kayan shima wanda zeyi tafiya dasu Lagos.

Jalal ma ya fito tsaf da shi, Jalila ta kulle ko ina, Jalal kuma yafita da akwatunan su, a mota taje ta tarar da shi ita kawai yake jira, ta bude ta shiga ta zauna, ya kalleta yace

"Baby ya dai naga duk jikinki a sanyaye?"

"bakomai fa" ta bashi amsa

"shikenan tunda bazaki gayamin ba"

Ya kunna motar suka tafi, koda yaje unguwar su yayi parking kin fitowa tayi daga motar, ya kalleta yace

"Fito mana, ni nakasa gane meyake damunki ne?"

Jiki ba kwari ta fito daga motar, Jalal yace

"muje in gaida su Abba, daga baya sekije ki gaida Daddy"

jinjina masa kai kawai tayi tabi shi, suna shiga cikin gidan kofar parloun a rufe take, Jalila ta dakko wayarta ta kira Maama, bugu daya Maama ta dauka Jalila tace

"Maama ina kika tafine, ina gida amma kofan parlor a rufe"

Maama tace

"ya salam, ai ban dauka da wuri zakuzo ba, kinga mun dan fita da Abba ne, yanzun nan zamu dawo insha Allah"

"shikenan se kun dawo" ta kashe wayar ta kalli Jalal tace

"basa nan wai yanzu zasu dawo"

Jalal yace "shikenan zomuje gida seki jira su"

Dan shiru Jalila tayi tana kallon Jalal.

"kina tsoron Mummy ne? Karki damu ba abunda ze faru muna tare, muje"

Jiki a sanyaye tabi bayansa danji take kaman tace bazata ba, tasan bazeji dadi ba idan tayi hakan, gabanta nata faduwa tana karanta addu'oi daban2, tun daga harabar gidan har cikin parlor ba kowa part din daddy ya nufa tana biye da shi, suna shiga suka tarar da Daddy na zaune na kallon labarai su Jalal sukayi sallama, ya amsa tare da waigowa, yana ganin su ya fadada murmushinsa tare da dan bude baki, ganin Yadda Jalal yazama wani babban mutum.

Jalal yana zuwa ya zauna kusa da Daddy, yayin da Jalila ta zube a gurin tana gaida Daddy, Daddy yace

"Haba Jalila zauna mana semu gaisa, yazaki zauna a kasa"

Cike da kunya da girmamawa Jalila ta dan zauna tana kuma gaida Daddy, ya amsa mata yana tambayarta ya gida. bayan sun gama gaisawa da Daddy ne Jalal ya dan risina yace

"barka da warhaka father, ya hanya?"

Daddy yace "lafiya kalau, ya gidan naka kuma? Ya 'yartawa take? "

"lafiya kalau, ba gata nan kana gani tana lafiya ba"
Daddy yai murmushi dan tabbas inka kallesu zaka gane suna cikin farinciki

Suka zauna sukayi ta hira da Daddy, Jalila se kunya takeji tana sunkuyar da kai, yayinda Jalal kam se zuba yake yana hira, daddy yaji dadin ganin Jalal, yadda yake magana yanzu ya sha banban da yadda yake yi da babu respect a maganganunsa a baya cikin gadara yake yinsu, amma yanzu gashi yasaki jiki yana hira babu hade rai da masifa.

Daddy yace

"gaskiya Son naji dadin ganinka, kaga yadda kayi kiba kuwa, ka wani zama babban mutum"

Jalal ya kalli kansa yace

"Allah Daddy thank God, and thank my wife efforts, she's behind the changes you saw on me, behind any successful man their must be a woman, da baku aura min ita ba ban san ya zanyi ba"

Jalila ji tayi kaman kasa ta tsage ta shige dan kunya, daddy yace

"tabbas Jalal matarka ta cancanci yabo da godiya, ubangiji Allah ya kara hada kanku, ya wanzar da zaman lafiya da kaunar juna a tsakaninku, Allah yasaka miki da alkhairi Jalila"

Jalila ba tace komai ba, Jalal yace "Ameen ya Allah Daddy"

Jalila tace "Daddy ina Mummy ne?"

"bata jin dadi ne, ta sha magani ta kwanta bacci"

Jalila tace "Daddy meyasa meta?"

"kawai dai jikin nata ne bata jin dadi, gashi bata son zuwa Asibiti, likita yazo ya duba ta yabata magani"

"Allah ya bata lafiya"

Daddy yace "Ameen" yayin da Jalal ya basar kaman besan zancen da suke ba.

Daddy yace

"to nima zan dan fita ne, inada meeting dazan shiga karfe daya"

Jalal yace "shikenan Daddy seka dawo, nima daga nan karfe hudu Insha Allah zanbi jirgi zan koma Lagos"

Daddy yace "to Allah ya kaika lafiya, kafin in koma zan biyo ta Lagos din in ganka"

Sukayi Sallama da Daddy ya shirya ya fita.

Babban parlor suka dawo suka zauna suka cigaba da hirarsu kaman a gidansu dayake babu kowa a parlor.

Jalal ya kalli Jalila yace

"nifa yunwa nakeji"
Dan zare ido tayi tana kallonsa

"yunwa kuma? A yanzun"?

"Eh ni yunwa nakeji"

Jalila tace

"to yanzu meye abunyi ga mutan gidan basa nan? Gashi ban fito da komai naci ba tunda ka zama jariri"

Murmushi yayi yace

"tashi muje kitchen mu duba seki dafa mana wani abun"

Jalila tace

"kana ganin babu matsala idan mukayi hakan?"

Jalal yace "matsala kuma? Tashi muje ba wata matsala"

Ta mike suka tafi kitchen.

Ilham juyi take kawai akan gado, tarasa me zatayi taji dadi a ranta, tunda Jalal yayi aure ko bisa kuskure basu hadu da Jalal ba, gashi kaman masifa haka wutar son Jalal ke ruruwa a zuciyar ta ba dare ba rana, gaba daya ta rame tayi baki, idan ta tuna artabun da suka dingayi da Jalila a baya akan Jalal ta tuna yanzu ita ya aura, kuma har yake gaya mata wai yana son matarsa, setaji duniyar ta kara mata zafi taji kaman ta samu wuka taje gidan ta kashe Jalila, gashi yanzu fafutukar Ummanta akan ta dauki fansa ne kawai, gashi ta gaji da zigar da takeyiwa Mummy, ga ciwon so na neman halaka ta, ko Abincin kirki bata iya ci, bata taba zaton radadin ciwon so ya kai haka ba, ko da wasa batayi tunanin son Jalal ze juye ya koma mata gaske ba, ta yanke shawarar zuwa gidansu yaseera taji wace shawara zata bata, yunwa ta isheta dan haka ta sakko daga kan gadon dan neman abunda zata zubawa cikin ta.

Kunun gyada Jalal yasa ta dama masa, ta soya masa irish potatoes, ta zuba sugar da madara ta na juya masa, yasa hannu ya karba, Jalila tace

"kai zaujee se'a zata bana baka Abinci ai kabari ya huce in ka sha zaka kona baki ne"

A dan shagwabe Jalal yace

"ai ba kya bani in koshi duk na rame"

"A hakan ne ka rame, kalli ka fara tumbi fa kalli kumatunka ma"

Dariya yayi ya shafa cikinsa yace

"bafa wata yunwa nake ji ba, kawai zanyi missing delicious food dinki, shiyasa nake so inci kafin in tafi"

Murmushi tayi ta juya tana gyara gurin da ta bata tana tattare kwanukan.

Ilham da kusan mintunan ta biyar a tsaye a kofar kitchen din ba tareda sun san tana gurin ba, taka sa daga Koda karamin yatsanta, sedai ji da tayi kaman an kunna gobara a kirjinta. Abun mamaki Jalal se dariya yake shida matarsa, cike da kulawa, yasha kayansa na mutunci sabanin a baya,wanda ganin dariyar Jalal seka shafe wata baka ga yayi dariya ko sau daya ba.

Jalal ya dau cup din kunun ya kai bakinsa, aiko yana sha ya kona harshe saboda akwai zafi sosai, aje kofin yayi yana rintse ido, tareda zukar iska cikin bakinsa. da sauri Jalila ta juyo

Tace

"subhanallah sannu wai sha kayi?, dama na Gaya maka da zafi fa amma ka sha a haka"

Janyota yayi da sauri ya hade bakinsu ya fara kissing dinta, Jalila ta tsorata sosai gaba daya jikinta yake rawa, sunyi kusan three minutes a haka sannan ya cikata ta ja da baya tana zare ido kaman mara gaskiya, ya dan kashe mata ido ya juya ya nufi fridge ze bude ya hangi Ilham ta gefen idonsa, a kofar kitchen tana hawaye basarwa yayi ya dau ruwa a fridge ya sha, ya janyo kujera dake dining din kitchen din ya zauna.

Kallon Jalila yayi ya ga yadda take rarraba ido kaman wadda aka kama tana aikata wani zunibi, ya dan kashe mata ido yace

"inkin gama zare idon kizo ki bani Abinci, lokaci yana kurewa, zanje inyi salla inyi haramar tafiya"

Kan table din dake gabansa ta aje Abincin, tana debo kunu tana hurawa tana bashi a baki.

Ilham da tayi kaman ta juya ta fasa shiga kitchen din, amma ta dake ta shiga, ko kallon inda suke batayi ba, suma basu kulata ba, Jalila ce tace

"Ilham ya kike ya gida, ranar me gadi yace kinje bama nan"

Wata uwar harara Ilham ta jefawa Jalila tare da jan uban tsaki, ita kuma Jalila tayi kaman bata gani ba, ta cigaba da bawa Jalal Abinci.

Jalal yace

"Baby badan nayi sauri nai kissing dinki ba, da tuni harshena ya kone gaba daya fa"

Dan murguda baki Jalila tayi tace

"seda na gaya maka da zafi ai amma ka sha da zafin"

"na matsu in sha ne shiyasa"

"ai gashi nan ka kone, kayi shiru kuma karka kware dai"

Shiru yayi yaci gaba da karbar Abinci kaman wani karamin yaro, yayinda Ilham keta kokawa da tukunya tana kokarin dora tukunya amma tarasa ta ina zata fara dora tukunyar saboda bakin ciki, kafarta se rawa take, saboda wani azababben kishi da taji yana taso mata.

Jalal kaman ba kowa a gurin haka ya cigaba dayiwa Jalila shagwaba tana bashi Abinci har ya gama ci.

Jalila ta kalleshi tace

"dan Allah meyasa kace in ka tafi kar in kira ka for two weeks"?

Dan murmushi yayi yace

"inda zanje aiki babu network ko kin kira baze shiga ba"

A shagwabe tace "Amma meyasa?"

Kafin yayi magana Ilham ta jefowa Jalila tukunyar dake hannun ta, da sauri Jalila ta rike Jalal tana fadin

"subhanallah"

huci Ilham takeyi tana kuka tare da fadin

"Allah ya isa ban yafe miki ba, wallahi sekinga abunda zanyi miki, sena hanaki sukuni da jin dadin rayuwa makira Azzaluma, kika dinga nuna ba wanda kika tsana sama da Jalal dan mugunta kin aure shi, wallahi ciwon son Jalal baze kasheni ba sekin dandani abunda nakeji"

Ta kuma rarumo food flask ta jefowa Jalila, da sauri Jalila ta shige bayan Jalal ta rirrike shi.

A fusace Jalal yace

"ke wace irin mahaukaciya ce haka? Wallahi kika illatamin mata se na daureki"

Daga bayan Jalal, Jalila tayiwa Ilham wani irn gwalo passionately tareda kashe ido cike da neman tsokana tace

"ni nace miki na tsaneshi? in ma na fada a da yanzu na janye ina son abuna"

Wani farinciki ne ya ratsa zuciyar Jalal tun daga sama har kasa da jin abunda Jalila ta fada akansa.

Hannun ta ya rike suka fice suka bar mata kitchen din.
Jalal yace

"kidena biye mata dan Allah, lokaci nake jira itama seta girbi abunda ta shuka, samunki a rayuwata yafi komai dadi a rayuwa ta"

Murmushi Jalila tayi tace

"nikam muje in duba in Maama ta dawo, dan bazan zauna ta nakasta ni a banza ba"

Jin hayaniya ne yasa Mummy ta Farka daga baccin da take ta fito dan ganin meke faruwa, tana fitowa parlor taga Jalal da Jalila yana gyara mata mayafinta, Ilham ta fito daga kitchen ido duk hawaye da katon muciya a hannun ta tana ihu tana

"wallahi sena ga bayanki muguwa makira, yadda kika kunsa min bakin ciki sekin kunshi wanda yafi nawa, saboda makircin ki burin mahaifiyata be cika ba, nikuma ciwon so ya kamani ina ta azabtuwa, wallahi sena tozarta ki"

"wallahi ba'a haifi 'yar da zata tozarta ni ba, ko ta wulakantani ba, kuma ni makirci ai uwarsa ce ni, nina haifeshi na yanke masa cibi, na goya shi a bayana, ke bari in gaya miki har yanzu ina nan a Jalila na da kika sanni ba abunda ya canza, kuma sedai ciwon son ya kasheki, zan bar Jalal ya auri duk macen da yake so a fadin duniya amma banda irinki, tunda na shiga baki isa ki shigoba wallahi, a baya ma bakiyi nasara ba balle yanzu"

Yadda Jalila ta hakikance yafi komai yiwa Jalal dadi, In dai hakane Jalila ba yanzu ta fara sonshi ba, tunda ba yau ta fara fada saboda shi ba, Jalal yace

"Baby keep quiet, kar ranki ya baci a banza" ya hade rai ya kalli Ilham, gaba daya ya koma Jalal dinsa yace

"idan baki taba ta ba bakya kaunar Allah, mahaukaciya wadda bata san darajar kanta ba"

"Ai babu babban mahaukaci sama da kai, bakaji kunyar yadda kake zakewa saboda mace ba, akan wannan shedaniyar yarinyar, Jalal kayi asara kaji kunya, ka fifita mace akaina, shine kake ciwa Ilham mutunci saboda kake kiranta mahaukaciya, shekara da shekaru tana sonka amma babu tausayin ta a zuciyar ka, kaje ka auri wannan me soyayyen idon" Mummy ce take kumfar baki tana masifa

Wani irin murmushi na rainin hankali yayi, yayin da Jalila ta tsakure guri daya takasa cewa uffan, Jalal ya kalli Mummy yace

"Inason Jalila sosai, kuma kamar yadda ta fada, tunda ta riga ta shiga babu wadda zata biyo bayan ta, wallahi ko Ilham zata haukace bazan aureta ba na tsane ta, tarihi na shirin maimaita kansa Mummy, dama nazo ne dan kiga namijin kokarin da sirikarki keyi akan danki, kuma nason kin gani sedai son zuciyar ki"

"Jalal you have to watch what you are saying, Mummy ce fa, be kamata ka daga mata murya ba, balle ka fadi abunda ze bata mata rai"

"Ohh Sorry dear zan gyara insha Allah" be bar Jalila ta kuma magana ba ya janyeta sukayi waje, yayinda Mummy ta daskare a gurin, Ilham kuwa dora hannu tayi a kanta tana rusa uban ihu.

Suna fita Jalila tace "Jalal meyasa kakemin haka a gaban Mummy, hakan ze kara sawa ta tsaneni ne"

"Jalila wallahi bazanji kunyar nuna miki soyayya ko agaban waye ba, ai ba haramun nayi ba, kuma ina so Mummy taji abunda Hajiyar Daddy taji lokacin da baya sauraren kowa se ita.

"Amma ai ba kai yakamata ka yi ba, komai ya wuce ai, dan Allah Jalal ka dena yiwa Mummy haka mahaifiyarka ce fa, ita ta haifeka, ko yaya she deserves to be respected as a mother"

Jalila kenan dukda abunda yake wa mahaifiyarsa yana jin dadin yadda take nuna damuwarta akan iyayensa

"shikenan naji, amma bazan iya boye soyayyar da nake miki ba ko a gaban waye, muje ki dau trolley dinki, zan tafi airport yanzu"

Koda ta dau trolley seda ya rakata har cikin gidan, yace shi baze shiga ba yasan yanzu suka dawo karya takura musu. Memakon ta tafi tsayawa tayi tana kallonsa
Yace

"ya dai, ki shiga mana"

Dawowa tayi Ta dan langabe kai ta rike hannunsa tace

"bakomai, Allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya, Allah ya tsare gabanka da bayanka, Allah yabaka abunda kaje nema ya daukaka a harkar aikinka, Allah ya azirtaka da halal ya tsareka da haram, Allah ya wadata ka ya karfafi imaninka, ka kula da kanka kaji, ka dinga cin Abincinka, ka dinga adhkar da sallolinka akan lokaci kaji zaujee na"

Takarasa maganar tareda dan jan dogon hancinsa, Jalal kallonta kawai yake yi, komai nata a nutse ga Addu'oi, yasan da Ilham ya aura baze taba samun haka ba.

Hugging dinta yayi ya kai bakinsa daidai kunnenta yace

"Ameen ya Allah, thank you very much my love, na miki Alkawarin zan kula da kaina, zanyi azkar da sallolina akan lokaci, Kema Allah ya kaiku lafiya ya dawo da ku, Alhamdilillah for having you as my wife, jin wannan Addu'oi seda ga bakin mace tagari, Allah yayi miki tukuici da gidan Aljanna"

Murmushi tayi ta shafa kansa tace "Ameen Zaujee, kaje kayiwa Mummy sallama, sannan kayi hakuri kome zatayi maka, karka fadi abunda ze bata mata rai" jinjina kai yayi ya cikata, taja trolley dinta ta shige.

Tana shiga ta tarar da Nana a parlor, ai da gudu suka rungume juna, Jalila tace

"My Nana kece? Saukar yaushe"?

"Saukar yau mana, dazu Maama sukaje suka dakkoni a airport"

Kara rungume juna sukayi, Jalila tace

"Maama shine baki gayamin zatazo ba"

Maama tace "ai gata nan kin ganta ai"

Jalila tace

"Nana kinga yadda kika zama lukuta kuwa, me kikeci haka wai"

Maama tace

"ku zauna mana se kace kun shekara baku hadu ba"

Ai basu tsaya a parlor ba suka wuce dakinsu na gidan, komai yana nan, tsaf da shi ana gyara dakin, suna zuwa Nana ta cire hijjabin jikinta tace

"ga abunda yasani kiba nan, se naga na zama mummuna ko Baby?"

dariya Jalila ta sha cikin Nana ya fito sosai tace

"Allah sarki rayuwa, kaman ba tare muke shiririta a dakin nan ba wai Nana ce da ciki, wallahi ba wani muni da kikayi, kinma fi kyau a haka"

Nana tace "wallahi Habibi ma cewa yake cikin yamin kyau"

Dan ya mutse fuska Jalila tayi tace

"waye kuma Habibi?"

"mijina mana, ko an gayamiki kowa irinkune? Ana so ana kaiwa kasuwa"

Dariya Jalila tayi tace

"ina wane mu, wannan abu ai se su Hajiya Nana manya, to ya Yaya Mahmud da Anty Salma? Ya kuma England da masu jajayen kunnuwa"

Nana tace "suna lafiya, wannan tambayoyi haka"

Jalila tai murmushi tace

"masha Allah, Nana cikin nan da nauyi kuwa, wallahi yayi miki kyau sosai?"

Hararta Nana tayi tace

"ki bari in yazo kanki seki ji"

Haka Jalila taita tsokanar Nana, Abba yayi murna ganin yadda yaga Yaran nasa kowacce cikin nutsuwarta.

Da daddare ma hira sukaita yi, Jalila ta kunna data taga Jalal online, nan ta manta da batun Nana suka dinga chatting da Jalal har Nana tayi bacci

Jalila ta turawa Jalal "bakajin baccine?"

"banaji, nakasa baccin ma gaba daya?"

"me yasa?"

"Am missing your body warm, that make me fall asleep"

"hmm, Performe Ablution, recite qur'an, and hug your pillow, goodnight 😘"

Murmushi ya dinga yi, ya duba agogonsa karfe biyu da rabi na dare, ya tura mata

"ni kike cewa in rungume pillow ko? Zan kamaki ne, let's meet in your dreams" ya rufe data ya kwanta.

Washegari bayan sun kammala breakfast suka dau haramar tafiya bauchi, tunda gari ya waye take trying lambar Jalal amma taki shiga, har suka tafi bauchi layinsa ya dena shiga.

Har sukaje garin bauchi Jalila ji take kaman bata da lafiya saboda takasa samun Jalal a waya,

"dama da gaske yake semunyi sati biyu ba muyi waya ba?"
A status dinta ta rubuta

"I miss you zaujee"

Se la'asar suka isa, sun gaji sosai, musamman Nana ga tsohon ciki ga gajiyar tafiya, suna fitowa daga Mota taga Yaya Jawwad
"Yaya Jawwad i miss you wallahi, dama zakuzo kuma wannan surprise haka ba wanda ya gayamin"

Jawwad yayi murmushi yace "Ai gara da mukayi surprising dinki, Jalal yasan zamuzo ai shine yayi miki lefi"

Jalila tace "yaya ina Hanan?"
"muje kya gani"

suka rankaya zuwa ciki abunda yayiwa Jalila dadi be wuce tozali da Hanan da tayi ba da nata katon cikin itama da gudu ta rungume Hanan Jawwad yace

"A'a Baby ayi a hankali kar aimana barna mun kara yawa"

Nana ta bude baki tana jinjina kai yaushe Yaya Jawwad yazama mara kunya?

Jalila tace "Allah yabada hakuri, zan kula"

Nan gidan yau dau shewa, hatta Mummy Hanan da daddynta sunzo, Daddy yayi mamaki yadda yaga Jalila tayi kalau da ita, kaman ba ita aka dinga fama da ita tana kukan bata son Jalal ba.

Jalila tace "bari inje inga Innata"

Anty fiddo tace "Inna tana lazimi bata son aje dakinta in tana lazimi se dai anjima" daga nan suka baje suna ta hira.

Nana tace

"ni Yaya Jawwad yabani mamaki, ga yadda yake salihi ga kunya, amma waishi ke cewa za'a musu barna, tab matar Yaya Jawwad da ciki abun mamaki"

Dundu Haanan tayi mata tace

"Nana zan miki rashin mutunci akan mijina, ina ruwanki damu"

Jalila dariya take musu

Yusuf ne ya shigo shima dan gaisawa da su Abba, ya tarar da su Nana a parlor suna ta hira, yaga Jalila tsaf da ita ta dan kara kiba ma, Hanan da take dan danna waya ta dago tace

"waike Jalila daga rabuwarku jiya hada wani status wai you miss him, sarkin gulma ashe kun jone? Kamar bake kika dinga kuka kina ba kya so ba"

Jalila ta Harare ta tace

"da kika ce yanzu ina son abuna ai mutu ka raba" shewa sukayi gaba daya
Nana tace "dan bakiga hotunan da sukeyi a wayar ta ba, soyayya suke sha abunsu, ahh komai lokaci ne hakuri me tadda rabo"

Yaya Yusuf yayi gyaran murya, suka nutsu gaba daya sukayi tsit suka gaisheshi ya wuce.

Anty fiddo tafito tace

"ku taho dakin Daddy akwai magana"

Jalila taji dam "Allah yasa lafiya"

Suka mike suka nufi part din Daddy, Jalila na gwada yadda su Nana ke tafiya.

Suka shiga da sallama, gaba daya iyayen nasu sun hallara, Jalila kanta a kasa ta nemi guri zata zauna daga kan da zatayi ta sauke su cikin idanuwan Ummi da ta kura mata ido.

Zumbur ta mike ta fasa zamana tana kuma zaro idon ta waje.

Maama tace "Jalila ki zauna mana"

Wani irin yawu Jalila ta hadiye tana nuna Ummi tareda dan ja da baya zatayi magana Amma taji numfashin ta na sauka da kyar cikin huhunta ta dena ganin komai se duhu.

Da sauri Ummi ta mike ta karasa inda Jalila take, kafin tayi wani yunkuri Jalila ta silale kasa sumammiya a gurin





Vote, Comment and
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️

Continue Reading

You'll Also Like

7.2K 517 52
Labari mai saka rauni a zuciya bisa yarda aka yi watsi da zumunci aka martaba ku'di fiye da zumunci ta yarda ake gudun 'dan uwa makusanci a fi son ha...
59.7K 2.7K 19
Wanan labari ne akan jarabawan ubangiji, yanason wata baiwar Allah mai suna Aisha ranan bikinsu ta mutu, bayan wani lokaci mai tsawo saiya hadu damai...
47.7K 2.9K 47
Na kasa fahimta da gasgata abinda zuciyata ke ayyana mini a kansa, SO ne ko BIRGEWA?. Komai nasa birgeni yake, ban taɓa ji ko ganin wanda ya haɗa abu...
221K 11.1K 90
Being flat broke is hard. To overcome these hardships sometimes take extreme measures, such as choosing to become a manager for the worst team in Blu...