Default Title - ABDUL JALAL (...

By Ayshercool7724

56.5K 2.5K 216

Labarin wani matashi daya riga ya gurbata rayuwarsa da shaye2 da raina iyayensa, tareda wata matashiyar yarin... More

Abdul Jalal(2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 7
ABDUL JALAL (2020) 8
ABDUL JALAL (2020) 9
ABDUL JALAL (2020) 10
ABDUL JALAL (2020) 11
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 15
ABDUL JALAL (2020) 16
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 19
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 21
ABDUL JALAL (2020) 22
ABDUL JALAL (2020) 25
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 27
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 30
ABDUL JALAL (2020) 31
ABDUL JALAL (2020) 32
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 35
ABDUL JALAL (2020) 35
ABDUL JALAL (2020) 36
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 38
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 43
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 43
ABDUL JALAL (2020) 44
ABDUL JALAL (2020) 45
ABDUL JALAL (2020) 46
ABDUL JALAL (2020) 48
ABDUL JALAL (2020) 48
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 50
ABDUL JALAL (2020) 51
.ABDUL JALAL (2020) 53
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL part 2
part 2 55
ABDUL JALAL (2020) 56
ABDUL JALAL 57
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 59
ABDUL JALAL 60
ABDUL JALAL 61
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 63
ABDUL JALAL 64
ABDUL JALAL 65
ABDUL JALAL 66
ABDUL JALAL 67
ABDUL JALAL 68
ABDUL JALAL 69
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 72
ABDUL JALAL 73
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 74..
ABDUL JALAL 75
ABDUL JALAL 76
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 78
ABDUL JALAL 79
ABDUL JALAL 80
ABDUL JALAL 81
ABDUL JALAL 82
ABDUL JALAL 83
ABDUL JALAL 84
ABDUL JALAL 85
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 88
ABDUL JALAL (2020) 89
ABDUL JALAL 90
ABDUL JALAL 91
ABDUL JALAL 92
ABDUL JALAL 93
ABDUL JALAL 94
ABDUL JALAL 95
ABDUL JALAL 96
ABDUL JALAL 97
ABDUL JALAL 99
ABDUL JALAL 100
ABDUL JALAL 101
ABDUL JALAL 102
ABDUL JALAL 103
ABDUL JALAL 104
ABDUL JALAL 105
ABDUL JALAL 106
ABDUL JALAL 107
ABDUL JALAL 108
ABDUL JALAL 109
ABDUL JALAL 110
ABDUL JALAL 111
ABDUL JALAL 112
ABDUL JALAL 113
ABDUL JALAL 114
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL

ABDUL JALAL 98

336 21 3
By Ayshercool7724

. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

*ABDUL JALAL*

_Story, writing and edited _

By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞

(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A*✍️

PART 2
_PAGE 4️⃣5️⃣98

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

_MY FIRST NOVEL _

A hankali Jalila ta cigaba da bin bayan Hannah, ba tareda ita Hannah ta sani ba, Hannah ta bude kofar babban palourn ta shiga, Jalila ta biyo bayanta amma ta tsaya a corridor yadda ba wanda ze ganta, Hannah ba karamin mamakin kyau da tsaruwar gidansu Jalal tayi ba, an kashe masa dukiya matuka, tun daga harabar gidan zaka gane mzauna gidan na cikin ni'imar ubangiji ta dukiya da yake bada ita ga wanda yaso a lokacin da yaga dama.

Koda ta shiga palourn ba kowa, seda ta tsaya ta karewa tangamemen palourn kallo, sannan ta jinjina kai tareda yin ajiyar zuciya, ta fara sallama, Mummy dake kitchen ta amsa tareda fitowa da jug a hannunta, suka gaisa da Hannah, Mummy na mata kallon rashin sani,
Mummy tace
"bari in kira miki Ilham din, dan a zatonta kawarta ce" Hannah tace "A'a ba gurinta nazo ba, Mummy dan Allah Jalal fa?"

Mamakine yakama Mummy amma ta dake tace
"Ai kusan watansa guda baya gari, yana lagos"
Hannah tace "Ai dole ya lallaba ya gudu lagos mana, Ina fatan mahaifinsa yana nan"

Mummy tace "lafiya kuwa?"

"Ina fa lafiya, ina son ganin mahaifinsa tunda shi baya nan"

"me mahaifinsa ze miki ne? Ki gayamin menene?" hakan yayi daidai da fitowar Ilham da alama fita zatayi, kawai taga Hannah, take gabanta yayi mummunar faduwa, kirjinta yafara dukan goma2, ta wani hade rai, ta karaso palourn cikin kasaita kaman gidan father dinta, tazo ta tsaya tareda kama kugu tanawa Hannah kallon da wacce kika zo?.

Kallo daya Hannah tayi mata ta dauke kai, tareda yin murmushi a ranta ta kalli Mummy tace

"Gara in gayawa mahaifin Sa abunda ake ciki, na gaya masa wancan karon be dau mataki ba, shi namjine ke ba lallai ki iya daukar abunda zan fada ba"

"ki Fadamin bakomai ni mahaifiyarsa ce ai"
Hannah ta gyara zama, sannan ta kalli Mummy tace

"wancan karon da nazo nayiwa mahaifinsa magana, nace yayi yadda zeyi a hadu mu rufawa juna asiri amma ba'ace min komai ba, nikuma asirina yana daf da tonuwa, Ina dauke da cikin Jalal na watanni uku a yanzu"

Da sauri Jalila tasa hannu ta toshe bakinta tana zare ido, gaba daya taji kafafuwanta suna rawa.

Hannah ta cigaba da cewa "muna haduwa da Jalal a hotels, kokuma idan yake night clubs, yasaba yimin ciki yace in zubar, wannan karon likita yace rayuwata na shirin fadawa hatsari muddin na zubar da cikin nan, ga iyayena na kokarin ganewa, soyayyar Jalal ce tasa na bashi kaina, wallahi koya aureni ko nayi kararsa ya kula dani da dansa"

Hannah ta karasa maganar cikin kukan kisisina, kasa magana Ilham tayi saboda mamaki.
Hatta Mummy kasa motsawa tayi daga inda take, se ido da take bin Hanna dashi
Hakan yayi dai2 da fitowar Daddy sakamakon jin hayaniya sama2
"lafiya me yake faruwa haka?"
Kafin su bashi amsa, ya sauke idonsa akan Hannah, be manta ta ba, ya kalleta yace "yarinya lafiya kuwa?
Cikeda karfin hali Hannah ta korawa daddy bayani kamar yadda tayi wa Mummy
"Karya kikeyi, Wallahi Jalal baya neman mata, mata basa gaban shi, yana shaye2 amma be yadda da neman mata ba, Jalal ba mazinaci bane ba" Ilham tayi maganar ilahirin jikinta yana rawa

"Masha Allah, dukkan yabo ya tabatta ga Allah, kin fadi magana kuma kin karyata kanki Ilham, tunda kinsan Jalal ba mazinaci bane, ta yaya kika san ina bashi kaina?"

Jalila ce ke maganar cike da kwarin gwiwa, gaba daya suka juyo inda Jalila take, kanta tsaye ta tako har gaban Ilham ta Kalle ta ido cikin ido tace

"Nagode Allah, kinyiwa Jalal kyakyawar sheda, yadda baya neman mata nima ba'a haifi namijin da Jalila zata bashi kanta a titi ba, Wallahi Ilham kinji kunya, tun wuri ki canza hali, tun kafin ki kaini bango in miki abunda se kin kasa shiga mutane"
Ta juya ta kalli Hannah tace

"Ni na manta da ke a doron kasa, in ban manta ba haduwar mu ta karshe yafi shekara, katsam jiya kika fadomin a rai, da irin abubuwan da kike aikatawa, haka nan naji kasa sakewa, zuciya ta tanata bani wani abu zai faru, katsam akan hanyata naga motarki na kokarin shigowa layinmu, shiyasa na biyoki dan duk inda kikaje babu Alkhairi Hannah "
Gaba daya kan Hannah ya kwance bata taba tunanin zata hadu da Jalila a wannan lokacin da take shirin hurawa Jalal wutar da babu me iya kashe masa ba.

Jalila ta kalli daddy tace
"Wallahi daddy karya take yiwa Jalal, ba wani abu dayake tsakanin ta dashi, sema ita da take kokarin cutar da shi"

With full confidence Hannah tace

"Karya kike inyiwa Jalal karya, ina dauke da cikinsa ne, kuma wallahi wannan karon bazan zubar ba, kamar yadda yasaba sani ina zubarwa"

Cikin tashin hankali daddy yace "Jalal din nawa ne yai miki ciki? Kiji tsoron Allah, bana tunanin hakan ze faru, wancan karon akan wannan maganar yayi fushi har ya nemi ya bar kasar nan, narasa waye me gaskiya a tsakaninku"

Jalila tace "Daddy ka kyale ta taje ta kai duk inda zata kai, Kai ka haifi Jalal kasan abunda ze iya da wanda baze iya ba, kasan baya shakkar kowa, idan ya aikata baze ji tsoron gaya maka ba, Daddy karya takeyi wallahi, I dan ba haka ba, taje ta shigar da karar"

Sosai Jalila take kokarin kare Jalal, abunda yabawa daddy mamaki, dan agabansa ya sha ganin irin artabun da sukeyi da Jalal, amma wani tabbaci take da shi akan Jalal haka, kuma y'a kayi tasan Hannah?
Ilham kam harar Jalila kawai takeyi ji take tamkar taje ta maketa a gurin, sekace Jalal din ubanta ne, ita so take tayi amfani da wannan damar, a tirsasawa Jalal yin Aure, amma Jalila nata karewa.

Mummy tace "Waike meye haka? Ban hanaki shiga duk wani shirgi daya shafi dana ba, banda munafunci da son jin kwakwaf hada biyo ta kizo kiji me ze faru, kina.......

"Rufe min baki khadija, Kinsan meyasa take kokarin kareshi, meye da dannaki da kike wani kumfar bakin adena shiga harkarsa"?
Daddy ya kalli Jalila yace "Jalila a ina kika san wannan yarinyar?"
Jalila ta kalli Hannah tace "daddy nasanta a gurin birthday din Jalal ne, Kuma sannan"
Sekuma tayi shiru, "Sannan kuma me?"
Daddy ya tambayeta, Jalila tace "bakomai daddy, amma makaryaciya ce"
Hannah ta fashe da kuka tace "Shikenan tunda ba 'yar kuce niba kun zabi zubewar mutuncina, wallahi mutuncina baze zube ni kadai ba, ku saurari sammaci, wallahi karar Jalal zanyi"
"Karki fasa sekin dawo, Amma idan har karya kike abunda ya faru da iyayen gidanki ze faru dake, idan har kin iya makirci za' a nuna miki ranar dukiya, ki fice kibar gidan nan da kafafuwanki kafin insa akama min ke"
Hannah ta tsorata da gadar zaren da Jalila tayiwa su Jeje suka rufta, dan haka ba kunya ta juya zata fice, daddy yace "Amma ta tafi ba'a gano bakin zaren ba"
Jalila tace "daddy ka rabu da ita, ko ta kai kara, kota bari ya dawo ayi maganar amma babu dalilin da zesa ta dinga maka karya tana bata maka rai akan danka"
Ta juya ta kalli Mummy tace "Mummy Allah ya huci zuciyarki, ban biyo Hannah dan shiga cikin lamarin iyalinki ba, sedan sanin hatsarin Hannah ga rayuwar Jalal, Amma Insha Allah kome ze faru bazan kuma shiga lamarin ba, in dai ya shafi gidan nan"
Ta juya zata fice, daddy yace "Jalila ita wannan yarinyar wacece? Sannan meye hatsarin ta ga Jalal? Menen alakarsu?"
Jalila tace "Daddy ba a bakina yakamata kaji ba, amma dai nasan babu wata alaka ta kusa dake tsakaninsu, na tafi se an jima" ta juya ta fice zuciyarta cike da bacin rai.

Maama ta dubi Yaya mairo tace "Yaya wannan jinin kuwa na lafiya ne?"

"Al'adace haka yake zuwar mata"

"haba Yaya, kalli guda gudan dayake zuba kice min Al'adace, yakama tunda nazo da mota mu kaita Asibiti"

"ba wani Asibiti da zamu kaita" yaya mairo ta bata amsa tana kokarin temakawa Naja ta mike zaune, amma tana tabata taga bata motsi, numfashinta da kyar yake fita, ga jini se cigaba da fita yake daga jikin Naja, ba shiri Yaya mairo ta mike, Maama ta temaka mata suka gyara Naja, suka sata a mota se Asibiti,
Sunkai awa biyu suna jira, Yaya mairo takira Naja a waya, tazo suka hadu a Asibiti, likita ya fito ya tambayesu alakarsu da Naja, sukayi masa bayani, yace su bishi office dinsa, haka suka bishi sukaje suka zazzauna suka zubawa likita ido, ya danyi gyaran murya sannan ya kallesu yace
"To kun san duk abunda yasamu bawa mu kaddarine daga Allah, kuma Allah yana jarrabar bayinsa ta ko ina, kuma dukkan musulmi se yayu Imani da kaddara sannan Imaninsa ze cika, Hakikanin gaskiya mara lafiyar ku tana dauke da ciki karami, kuma tayi Amfani da miyagun kwayoyi wanda hakan yayi sanadiyar zubewar cikin jikinta da kuma lalacewar mahaifarta"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji un" shine abunda suka dinga nanatawa, gaba daya Maama taji jikinta yafara rawa, Yaya mairo ta dora hannu aka tafara ihu, likita yace "Haba baiwar Allah kamar ba yanzu nagama yi miki nasiha ba, ba wannan bama, yarinyar nan ta zubar da jini da yawa, Akwai bukatar a sama ta jini, kuma a bincike da mukayi tana da cutar Hepatitis B, (ciwon Hanta), dan haka ku gaggauta nemo Jini, a duba a 'yan uwa wanda jininsu yayi dai2 se a samata"

Haka suka fiti office din nan suna salallami, jiki a sanyaye Yaya mairo tace "bari a kira yayanta a waya, Zainab kira Jawwad suzo a duba in jininsu zeyi a samata"
Da sauri Maama tace "Wane Jawwad din? Jawwad yana Abuja ya samu Aiki ai, nikam Yaya mairo ga wannan" tasa hannu a Aljihu ta dakko kudi tabata sannan tace "ga wannan ku sai magani, zan koma gida magariba tayi, se na dawo dubiya, Amma yakamata kunemo wanda yake da alhakin cikin nan, yazo ya dauki nauyin ta, se anjimanku"
Maama ta juya ta fito daga ward din, tana ta tunani tareda mamaki, da kyar Maama ta kai kanta gida, saboda tunani da Mamaki, da tuno marin da tayiwa Jawwad saboda Naja se taji gaba daya jikinta yayi sanyi.

Haka ta koma gida jiki a sanyaye, tunda ta koma take tunani, Nana ta lura da Yadda Maama jikinta yake a sanyaye dan haka taje ta sameta a daki take tambayar ta "Maama wai me yake damunki ne? Tukuna ma ina kikaje?"
Dan shiruu Maama tayi, sannan tace "Nana naso inyi ganganci da rayuwar dana"
"gangancin menene?"

Nan ta kwashe komai ta gayawa Nana, Nana tayi murmushi tace

"Allah sarki Rayuwa, Maama kinga wannan abun to izina ne a gareki, Allah yasa kar alhakin marainiyar Allah ya kamaku, kunsaka Jalila kuka ta zubda hawaye ba a dadi, ku zageta ku mata cin mutunci, ku mata gori amma se gashi su sunyi Abun kunyar da 'yar arnan ba tayi ba, Maama lokaci yayi da yakamata ki gane su waye ke kaunar ki, Yaya mairo' yar uwakki ce amma abun hannun ki takeso, ki duba irin biyayya da Jalila tayi miki tsawon lokaci, duk fitsararta da kuke fada, ke dai bata taba yimiki ba, se dai Yaya mairo, Maama a ci zarafin iyayen mutum dacin abun ya wuce yadda kike tunani, kun cutar da ita gaskiya, fatan Allah ya yafe muku, yanzu seki gane, Ummi da take ba musulma ba da farko, tayiwa 'yarta tarbiyar da wanda aka haifa a musulinci bata yiwa' yatta ba, Allah yasa hakan ya zama izina a gareku"
Maama kasa cewa komai tayi, se jujjuya maganganun Nana da takeyi, tabbas Maganganun Nana gaskiya ne,
Nana tace "Maama bari inje daki inada Assignment da zanyi"
Gyada mata kai kawai Maama tayi, Nana kuma ta fice, koda taje dakinsu Jalila tana kwance idonta a rufe, kaman me bacci, amma ba baccin take ba, tunanin abubuwa da dama ne ke zagayawa a cikin kwakwalwarta.

Daddy yakasa samun sukunibda abunda ya faru, gaba daya hankalin sa yaki daidaituwa, yarasa maganar wa zebi, ta Jalila kokuma ta Wannan yarinyar, Amma yakasa bawa kansa amsar wani tabacci Jalila take da shi akan Jalal, Mummy ta lura da yadda daddy ya dami kansa dan haka tace

"Ni dai a ganina wannan yarinyar da gaske take, ba'a shedar mutum, shiyasa nake son mu aurar da Jalal, shekarunsa ya kai ya ajiye iyali, ita kuma wannan yarinyar da tazo da wannan maganar, indai da gaske take, a lallabata abata kudi tayi hakuri"

"bana tunanin Jalal ze aikata haka, kuma tunda Jalila ta bada sheda akan Jalal, abun dubawa ne, amma yazama dole in bincika, lamarin yaron nan na ma rasa yazanyi, Allah ya shiryamana zuri'a"
Dadd yasa hannu ya dau wayarsa ya kira Jalal a waya, seda ta kusa katsewa sannan Jalal ya daga, koda ya daga ma beyi magana ba, shiru ya gudana na wani dan lokaci sannan daddy yace "Jalal kana jina?"
"Ina jinka daddy"
"ya kake ya aikin kuma?"
"lafiya kalau Alhamdilillah daddy, kana Nigeria kenan?"
"Eh ina nan, nakira ka ne, ina so muyi magana"
"ina jinka"
"Wace ce Hannah?"
Gaba daya Jalal ya manta da wata Hannah a rayuwarsa, Amma ya maze yace "Ban Santa ba"
"Jalal ban sanka da karya ba, wannan yarinyar itace kwanaki tazo min da waccan maganar, wannan karon tazo min da maganar wai tana dauke da ciki kuma nakane, Amma Jalila ta karyata ta, sannan tacemin Yarinyar tana da matukar hatsari ga rayuwarka, kamin bayani "
Ba abunda ya farantawa Jalal rai sama da jin batun Jalila ta kare shi, duk da furucin da tayi na bashi ba ita, daddy yace" Jalal ya naji kayi shiru? "
"to me zance maka daddy? Duk hukuncin daka ga dauka akaina dai2 ne, inma ka yadda gaske ne ko karya, dan Allah ni ku kyaleni hankali na ya kwanta, ina jin dadin zamana a inda nake karku daga min hankali"
"Amma Jalal meye hadinka da yarinyar nan har take bibiyar ka? Tana ikrarin zata kai kararka"
"Daddy in dai har bana nan, a bayan idona yarinyar data tsaneni zata bada shedar kirki akaina me kake so ince maka, kana so inta rantsuwa ne seka yadda dani? Kasan ba haka nake ba, Idan bata kai karata ba ni zan dau mataki akanta"

"Amma meye hatsarin yarinyar ga Rayuwar ka? Kamar yadda Jalila ta fada?"
"ka tambaye ta mana, tunda a bakinta kaji"
"Jalal yaushe zaka dawo?"
"ba yanzu ba, se nan gaba, nifa zamana anan yafi min zaman gidan nan, da za'adinga takura min"
"to shikenan tunda haka kace"
Haka sukayi sallama ya kashe wayar.

Mummy tace "wai nifa nakasa gane wannan maganar, ita Jalila wacece dinsa da za ta fadi abu ka yadda, ya akayi tasan abunda mu bamu sani ba akan danmu, haka akeyi?"
Murmushi daddy yayi ya dan kashe mata ido yace "haba deejat to meye a ciki? Kin samu me kulamiki da son, you have to thank her, har gida tazo dan kare shi"
Kara kunna Mummy yayi, dan haka ta tashi fuuu ta bar masa dakin.

Ilham tayi safa da marwa yafi sau Ashirin a dakinta, tana son ta tabbatar da Hannah dagaske take koda wasa, yanzu abun ya kuma kwabe mata, da ta manta da batun Hannah, amma yanzu yakin ya kuma zame mata biyu, ga Jalila ga Hannah, da tana tunanin tayi maganin Jalila, tunda tayi mata makirci a gurin Mummy, "Amma Jalila nan naci ne da ita bata da zuciya, shegiya se nayi maganin ta, sena kuma kunna mata wata wutar, to amma in dagaske Jalal yayiwa Hannah ciki fa? Da sauri tace" kai karyane, da Jalila yayiwa Hannah ciki da yanzu wani zancen ake ba wannan ba, karya takeyi"
Ilham ta fito daga dakinta har tana tuntube ta tafi daki Mummy, tana zuwa ta tarar Mummy ta cika tayi fam, fuskarta sam babu walwala, Ilham taje ta zauna a kusa da Mummy tace
"Mummy lafiya kuwa?"
"ke rabu dani, ni zancen wannan yarinyar mana, gaba daya daga Jalal din har ubansa naga hankalin su ya karkata kan wannan yarinyar Jalila, ga itama wannan wadda tazo din da wannan maganar cikin"
"mhmm wallahi Mummy in bakiyi wasa ba yarinyar nan se ta hana Jalal din ma shigowa gurinki, ta ne Santa shi dake, meye nata na sawa anema masa aiki a nesa? Kuma ga daddy yafara biyewa maganganun ta, wallahi Mummy da sannu zata janye miki shi gaba daya"
Mummy ta numfasa tace "ni Ilham gaba daya kaina ya kwance akan lamarin Yaron nan, narasa yadda zanyi"
"to Mummy kiyiwa daddy maganar, ayi mana Auren mana, saboda ayi maganin abun, tunda har ya fara bin mata"
"
A fusace Mummy tace" Ke dan Allah ki rabu dani, kina gani ba irin kokarin da banyi ba, Amma abu ya ga gara, ni ki kyaleni nace ki bani lokaci, sena fara shawo kan matsalar, ni na miki alkawarin Auren nan, ki karamin lokaci in gama da wannan matsalar mana"
Ilham ba tace komai ba ta mike ta bar dakin, tana fita tayi kwafa tace "Wallahi zaki gane kuskuren ki Mummy, zanyi maganinki, sena Auri Jalal din na mallake shi, ke da shi sedai kallo"

Amin Afuwa nayi busy sosai,
Gashi nan ba editing

Continue Reading

You'll Also Like

27.9K 544 33
"I thought we were friends, Azriel. I was caught off-guard but you have to know it was forgiven the day it happened." The priestess looked back up to...
15.4K 804 71
'Ammi ya zan yi da rayuwata? Ya kuke so in yi da zuciyata? Ban taba ba...daidai da rana daya ban taba mafarkin yin rayuwar aure ba tare da Ameer ba...
81.8K 5K 58
Dr.TAHEER labari ne mai cikeda soyayya mai tsuma zuciya...labarin wani matashin likita daya kamu da matsananciyar soyayyar yarinyar da ya raineta a h...