Default Title - ABDUL JALAL (...

By Ayshercool7724

56.5K 2.5K 216

Labarin wani matashi daya riga ya gurbata rayuwarsa da shaye2 da raina iyayensa, tareda wata matashiyar yarin... More

Abdul Jalal(2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 7
ABDUL JALAL (2020) 8
ABDUL JALAL (2020) 9
ABDUL JALAL (2020) 10
ABDUL JALAL (2020) 11
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 15
ABDUL JALAL (2020) 16
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 19
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 21
ABDUL JALAL (2020) 22
ABDUL JALAL (2020) 25
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 27
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 30
ABDUL JALAL (2020) 31
ABDUL JALAL (2020) 32
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 35
ABDUL JALAL (2020) 35
ABDUL JALAL (2020) 36
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 38
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 43
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 43
ABDUL JALAL (2020) 44
ABDUL JALAL (2020) 45
ABDUL JALAL (2020) 46
ABDUL JALAL (2020) 48
ABDUL JALAL (2020) 48
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 50
ABDUL JALAL (2020) 51
.ABDUL JALAL (2020) 53
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL part 2
part 2 55
ABDUL JALAL (2020) 56
ABDUL JALAL 57
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 59
ABDUL JALAL 60
ABDUL JALAL 61
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 63
ABDUL JALAL 64
ABDUL JALAL 65
ABDUL JALAL 66
ABDUL JALAL 67
ABDUL JALAL 68
ABDUL JALAL 69
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 72
ABDUL JALAL 73
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 74..
ABDUL JALAL 75
ABDUL JALAL 76
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 78
ABDUL JALAL 79
ABDUL JALAL 80
ABDUL JALAL 81
ABDUL JALAL 82
ABDUL JALAL 83
ABDUL JALAL 84
ABDUL JALAL 85
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 88
ABDUL JALAL (2020) 89
ABDUL JALAL 90
ABDUL JALAL 91
ABDUL JALAL 93
ABDUL JALAL 94
ABDUL JALAL 95
ABDUL JALAL 96
ABDUL JALAL 97
ABDUL JALAL 98
ABDUL JALAL 99
ABDUL JALAL 100
ABDUL JALAL 101
ABDUL JALAL 102
ABDUL JALAL 103
ABDUL JALAL 104
ABDUL JALAL 105
ABDUL JALAL 106
ABDUL JALAL 107
ABDUL JALAL 108
ABDUL JALAL 109
ABDUL JALAL 110
ABDUL JALAL 111
ABDUL JALAL 112
ABDUL JALAL 113
ABDUL JALAL 114
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL

ABDUL JALAL 92

402 25 1
By Ayshercool7724

..🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹


*ABDUL JALAL*

_Story and writing_
By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girls_)

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞

(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A*✍️


PART 2
_PAGE 3️⃣9️⃣92

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724




_MY FIRST NOVEL _

Jalal nagama magana yasa karwa Maama hannunta, Jawwad kam mamaki da bacin rai ya hanashi magana, Maama bata taba marinsa ba, lokacin yaji yakara tsanar Naja, juyawa Jawwad yayi ya nufi part dinsa zuciyarsa tana suya, da sauri Jalila tabi bayansa ta bar su Agurin a tsaye, Jalal ma bin bayansu yayi, ita kanta Maama jikinta yayi sanyi da marin da tayiwa Jawwad, yadda taga ya sunkuyar da kai ya tafi bece mata komaiba da kuma maganganun da Jalal yayi, Amma ta maze ta cigaba da banbami.

Jawwad na zuwa ya zauna ya dafe kansa yayi shiru yana saka abubuwa daban2 a ransa, da sauri Jalila ta karaso ta zube agabansa tana kuka amma takasa magana se sheshsheka, dagowa Jawwad yayi ya zuba mata ido amma yakasa magana, Jalal ne yakaraso ya tarar dasu a haka, yasamu guri ya zauna a kusada Jawwad, ya kalli Jalila yace

"kidena wannan kukan haka, kikoma gida komai ze wuce Insha Allah"

Shiru tayi tacigaba da kukan a hankali cikin kuka tafara kokarin furta
"Am sorry Yaya Jawwad,...."
Maganar ta sarke takasa karasawa, Jawwad yace

"Jalila ke yakamata abawa hakuri, tashi kije kidena kuka, nasan abunda kikeji akan yadda akemiki a gidan nan but am really sorry komai ze wuce kinji"
gyada masa kai kawai tayi, tace "Yaya Jawwad karka canza lokacin tafiyar nan, kayita tanada mahimmanci"

"zanyi Insha Allah"

yabata amsa jiki a sanyaye, ta mike zata fita ta juyo ta kalli Jalal tace

"Ilham! Ilham.... Sekuma tacigaba da kuka ta fice da sauri ta tafi cikin gidan da yanzu takejinsa kamar prison.

Nana bata san me akeba, tana can tana manne da Mahmud a waya, dan haka koda ta fito palour Maama ta tarar tana sababi, ita zuwa yanzu lamarin Maama har tsoro yake bata, kullum cikin fada take, takoma halin 'yar uwatta na masifa ko gajiya batayi, Nana batabi kan maganar da Maama takeba ta wuce kitchen tadora girki.

Jalila ta shigo palour, Maama na kokarin shiga dakinta se hararta takeyi tana tsaki, sannan ta shige Naja ma wani tsaki tayi tace
"hmm nida ke naga wanda ze Nasara, duk wani iyayinki da iya munafurci da kinibibi na kafirai da kuka iya sedai kiyi kigama dan nafi karfinki wallahi kar nake kallonki nafiki iya tashanci, banza 'yar Arna kawai, wadda uwarta ta yasar ta tafi gararinta"

idon Jalila yayi jawur dan kuka, cikin matukar bacin rai da masifa Jalila tace
"Naji nakuma yadda kinfini iya tashanci, tunda kin tsotsa a Nono mana, nagode Allah har mahaifina ya koma ga mahallicinsa ba'akamashi da 'yar waniba, naki uban fa? Shekararsa biyar a prison da kyar aka karboshi, tashanci gashi nan ke kinayi yayarki da ďan uwanki nayi, sannan kinfini tashanci nikuma nafiki kai da iya wasa da hankali, ki kiyayi ranar dazan miki tonon silili, kuma Aure ne da yardar Allah baza' ayi shiba, saboda nagama shirina akanki, lokaci kadan ya rage kifada tarkona"

Nana data fito daga kitchen bata taba jin wannan labarin na mahaifin Su Naja ba, ita kuma Naja daskarewa tayi a gurin dan mugun mamakine yakamata, dan ta girmi Jalila kuma tun kafin a haifeta abun yafaru bakowa yasani ba, Amma ita ya akayi tasani.

Jalila tuni ta shige daki, ta nufi bandaki ta dauro Alwala tazo ta hau sallaya tafara gabatar da sallar magariba.

Jalal yanata rarrashin Jawwad
"Jawwad tun asalinka me biyayyane da hakuri ba kamar niba, dan Allah kayi hakuri ka kwantar da hankalinka, kasan iyayenmu mata daukar ziga baya musu wahala, ka kwantar da hankalinka kayi hakuri"
Wata irin Ajiyar zuciya Jawwad yayi yace

"Jalal Abunda yafaru naji babu dadi, amma abunda yafi batamin rai halinda wannan marainiyar Allah ke ciki, Jalal hakurin Jalila yakai a yaba mata, duk fitinarta tanada kawaici da hakuri, kuma tanada biyayya, duk abunda Maama take mata bata taba nuna mata bacin ranta ba, akan Jalila nasan Abba ze iya rabuwa da Maama, amma bata taba gayamasa abunda ke faruwa ba, Jalal inajin tausayin yadda rayuwar Jalila ke kasancewa daga wannan se wannan, nasan yau kwana zatayi kuka, kuma Jalal abunda Ilham tayi bata kyauta ba, be kamata tayiwa Jalila hakaba, son zuciya ba halinta bane"

"Nasani Jawwad, komai zezo da sauki zan dau mataki akan hakan, kaji ka kwantar da hankalinka"

"Shikenan Jalal, ka shirya jibi Insha Allah zamuyi tafiyar nan"
"Allah ya kaimu"

Jawwad ya amsa masa da Ameen, Jalal ya tashi ya fito, a harabar gidan yaci karo da teddyn Jalila da sweet dinta a kasa, yasa hannu ya dauka teddyn ya tafi dashi.

Bayan Jalila ta idar da salla, Nana tace "Jalila dan Allah meya faru kikewa Naja wannan maganar? Abun yabani mamaki ni bantaba jiba fa, kodai fushi ne yasaki"?

Jalila idonta Jawur ta kalli Nana tace "Nana duk bacin raina banawa mutum kazafi, kuma bana gori yauma raina ne ya kai makura a baci, sannan ba karya nayiwa mahaifin Naja ba, kuma na fada ne kozan samu sassauci akan bakanta min da ake, kullum aka tashi gori sedai ace uwata Arniya, kawai saboda...... Kasa karasawa tayi, maganar ta sarke saboda kuka

"Am really sorry sister, i feel your pain nasan ba dadi abunda yake faruwa dake amma kiyi hakuri dan Allah"
Wayar Jalila ce tafara ringing Ahmad ne Amma bazata iya dagawa ba ta kashe wayar.

Jalal na zuwa gida ya ajiye teddyn Jalila akan gadonsa ya tafi cikin gida, a palour ya tarar da Mummy amma ya shareta ya nufi dakin Ilham, tana kwance akan gado tana chatting ya fado dakin, zumbur ta mike zaune dan tasan indai taganshi a dakinta toba Arziki, ya kureta da jajayen idonsa yace

"Tambayarki zanyi, idan kikamin karya sena shakeki, yaushe kika kaiwa Jalila kudi tabawa Maama?" hade rai tayi
"Na kaimata kudi, nace ta ajiyewa Maama inji Mummy"
"karya kikeyi"
"niba karyanake ba"
"zan tattakaki wallahi, karya kike"
"wayyo Allah mummy, kizo ki temakeni" ganin tana ihu ya harzuka Jalal jikinsa yafara rawa ya janyota daga kan gadon ya zuba mata mari
"Nizaki rainawa hankali? Ni zakiyi wa ihu uban me nayi miki?"
Mummy kam a sukwane takaraso dakin
"lafiya meye haka metamaka?"
Banza yayiwa Mummy yace

"waike wace irin dabbace ne? Ranar akan idona kike soke kudi a jikinki, naganki da idona amma saboda baki da mutunci kin dorawa yarinya kinsa se kuka take, wace irin zuciya ce dake haka?"
Se yanzu Mummy tagane inda ya dosa dan haka tace "to mara mutunci, dama saboda waccan yarinyar kazo kake wannan zare idon kake kokarin shaketa, kaji kunya wallahi ka fifita wata banza can bare akan 'yar uwarka"

"Karki kara dangantani da wannan shedaniyar niba' yar uwata bace ba, tanemi 'yan uwanta can baniba, kuma kicigaba karki fasa, indai wannan yarinyar ce you know what she's capable of doing, ba' a tabata ta hakura, kuma wallahi kika kuma yi mata wani abu makamancin haka sekin bar gidan nan tunda ba gidan ubanki baneba"

Mamakine yakama Mummy suka bude baki suna kallonsa gaba daya,
A fusace Mummy tace "kai ka kiyayeni, akan waccan banzar yarinyar zaka ci zarafin Ilham, kuma har kake nema ka gayamin bakar magana haka? Jalal kanayiwa kanka hisabi kuwa?"
"Karki kara ce mata banza, ga banza nan agabanki" ya nuna Ilham
"tayimin abunda ko raina nabata bazan biyata ba, bashida amfani yimiki wani bayani tunda son zuciyarki kawai kikasani, amma lokaci ze bayyana komai" har ya juya ze fita daga dakin idonsa ya sauka akan Alqur'ani nan a saman rio, zuwa yayi yasa hannu ya dauka ya duba tabbas Alqur'anin ne, Amma me yakawo shi hannun Ilham? Be tsaya tambayarta ba yai waje abunsa.

Yana fita Ilham ta dora hannu aka tace "Nashiga uku mummy, wannan wace irin masiface? Wace irin kiyayya yaya Jalal yakemin haka?" Mummy tace
"kinga dan Allah darene, kidena min ihu, hankalina ya karkata wani gurin, tabbas yaron nan yana sonta, kenan seta juyamin ďa, yadda yake wannan masifa kanta, har yana wannan kumfar bakin akanta ina baze yuwu ba wallahi, ba'a haifi yarinyar dazata juyamin ďa ba, koya fifitata akaina ba"
(su Mummy amanta lokacin da ake juya ďan wata🙄)
Ilham cikin kuka tace "Wallahi bawani sonta dayake, tana bashi kanta ne kawai, nikuma bazan iyaba shiyasa baya sona se ita dan Allah Mummy kiyi wani abu".

"ke rufemin bakini, yanzu ba wannan issue dinne agabana ba" ta juya tabar Ilham da sakakken baki.

Koda Abba ya dawo beji motsin yaran nasa ba, dan yasaba yazo yatarar da Nana da Jalila suna kallon ko wani abun a palour, dan haka yake tambayar Maama
"wai ina yaran nan ne? Banga kowa a cikinsu ba, Jawwad har ya rufe kofarsa, sukuma 'yan matan banga kowacce ba lafiya dai ko?"
Maama tace "lafiya kalau, sun kwanta da wurine kawai" dahaka suka bar zancen.

Washegari da safe yakasance Asabar, Jalila tana baccin dole, dan kwanakin naan bata iya bacci, ga matsanancin ciwon kai saboda kuka, wayartace tafara ringing Hanan ce dan haka ta daga, amma da mamakinta taji Hanan tana kuka, nan da nan hantar cikin Jalila ta kada tace "Hanan lafiya kuwa?"
Cikin kuka Hanan tace "Jalila dama Haidar Aure zeyi kuka boyemin?kuka kyaleni naketa masa wannan makauniyar soyayyar?"
"Haba Hanan, waya gaya miki haka?"
"ya zakice waya gayamin? Jiya muna waya da kunnena naji, muna waya dashi wata tana cewa wai ankusa bikinsu yake waya da wata, Jalila am so disappointed, meyasa kukayi min haka?"
"Hanan bazaki ganeba, yanzu haka cikin rikici muke dagani har Yaya Jawwad"
"Jalila duk rikicin da kuke ciki bekamata kumin haka ba, amma nagode"
Jalila na kokarin yimata bayani amma Hanan ta kashe wayar ta, dafe kai Jalila tayi ta marasa dame zataji, Hanan, Jalal, Jawwad kokuma wannan tashin hankalin.

Jawwad ya gayawa Abba zeje kaduna, Abba be hanashi ba, ya fuskanci Jawwad baya walwala, amma Abba yabarshi a stress ne na shirye shiryen biki da kuma tunanin rabuwa da gida ze tafi wani gurin aiki.
Jalal yakira yagayawa Abdallah cewar zasuzo,
Hanan kam tasha kuka, Abdallah yazo mata da labarin Jawwad zezo, amma sam batayi murna ba, Mummy se rarrashinta take, amma kuka kawai takeyi.

Daddyn Hanan yasan da zuwansu Jawwad dan haka befita ba yana gida.

Shabiyun rana su Jalal suka iso kaduna garin gwamna, sunsami kyakyawar tarba a gurin iyayen Hanan. Har cikin gida Abdallah ya kaisu Jawwad suka gaida Mummy, Abunda ya daurewa Mummy kai be wuce yanayin abubuwan Jawwad sak Yusuf dake bauchi, boye mamakin ta tayi suka gaisa sosai, har cikin ranta ta yaba da hankalin Jawwad, har ranata take Addu'ar Allah yasa Jawwad ya auri Hanan.

Abdallah yaje dakin Hanan yasameta a daki idon nan jawur ta sha kuka, yace mata

"to uwar kishi gashi can yazo, yakamata kije ya ganki tunda danke yazo, amma fa naga shima kaman bashida lafiya ne, naga ya rame sosai"
Da sauri ta mike zaune tace
"dan Allah bashida lafiya?"
"hmm magulamaciya, da kikace haushinsa kikeji, keda a rayuwarki ba kya uzuri, inkin ga dama kicigaba da kukan karkije" ya fice yabar mata dakin, bayansa tabi da harara, tayi zamanta taki tashi, seda Mummy ta biyo sahunta taita mata mita sannan ta mike, jallabiya tasaka baka se mayafinta ta tafi palourn da aka sauki su Jawwad.

Kallo daya zakayi mata kasan tasha kuka, tana zuwa tasamu guri ta zauna ta takalli Jalal tace "Yaya Jalal sannu da zuwa ya hanya?"
Murmushi Jalal yayi yace "lafiya kalau Hanan, ga Jawwad din na kawomiki"
Kallon Jawwad tayi kawai tafara kuka, Jalal yace

"Ikon Allah, su mata komai nasu na kukane, hakama Jalila takeyi, mikewa yayi yafita yabasu guri.

Jawwad ya tashi daga inda yake yazo gabanta ya zauna ya dan zuba mata ido sannan yace

" dama zaki iya fushi dani haka? Haba My i don't expect this from you, Hanan bakiga na rame ba, ina cikin damuwa komai yayi min zafi narasa ya zanyi" nan ya kwashe komai ya gaya mata, gaba daya tausayinsa yakamata tace
"Am sorry Haidar kishinka yasani nayi maka haka, dan Allah kayi hakuri, Amma yaya Jawwad bazan iya jure ganin ka Auri wata baniba, Jawwad zan iya hakura ka auri wata ka hadamu amma banda wannan yarinyar"
"Meyasa?"
"sister dinkace, nibazan fadi komai ba, Amma zancigaba dayi mana Addu'a"
Jawwad yaayi ta rarrashinta harta saki jikinta suka fara hira

Koda Jalal yafito Abdallah ya janye shi dakinsa suka dinga hira, bayan sunyi Sallar Azahar, suka tafi part din daddyn su Abdallah.

Daddy ya karbesu da fara'a ya kalli Jawwad yace "barka da zuwa sirikina ashe kuna tafe"
Sunkuyar da kai Jawwad yayi saboda kunya kodan karamcin nan da sukayi masa zenemi alfarmar Abbansa ya barshi ya auri Hanan.

Matasan suka zauna a kujerun dake palourn suka gaisa, ya tsaida idonsa akan Jalal ya lura da yadda bayason magana sosai, sedai in anyi abu ya danyi murmushi

Daddy yadubi Jalal yace
"My son, Kaine Jalal kenan?" Jalal yayi mamaki dan yasan daddyn Hanan besan shiba, amma ya akayi yakama sunansa haka? Jalal ya gyada kai yace "eh nine"
Daddy yace "Ai ina ganinka naganeka, ammm nace bakaga tex message da'aka turamaka ba?"
Jalal ya dan dirirce yace "Wane message?"
Daddy yace "Eh akwai hukuma dasuka turomaka message na daukar aiki mana, zakaje screening"

Shiruu Jalal yayi sannan yace

"Ammafa daddy nima ina shaye2, tayaya NDLEA zasu daukeni aiki?"
Tausayinsa ne yakama Jawwad yace "haba Jalal aiba a haka, ka amince mana, sun san kanayi suka daukeka ai"
Daddy yace

"ABDUL JALAL don't mind kaji, ai munsan kana shaye2, karka damu you are my son dukda bansanka abaya ba amma yanzu nasamu ďa, dama yaran sunmin kadan, nayi magana da daddynka ma, An riga an baka aikin, ba wani abu ai zaka iya, Jajircewarka akeso sannan kaikuma kayi kokarin denawa, zaka temakawa hukuma, ni yadda naganka din nan with good body structure aida a soja nasaka kaima"

Gaba daya sukayi murmushi tunda daddy cikin sigar zolaya ya karasa maganar banda Jalal daya shiga tunani yayi shiru,

Daddy yakuma cewa "Am sorry munmaka laifi nida diyata ko? Tasani nasa an soke maka visa, tuba muke bamuyi hakan dan bata maka ba"
Murmushi Jalal yayi ya sunkuyar da kai suka cigaba da hira, bayan Azahar suka daura haramar komawa gida, sukayi sallama dasu sannan suka nufo kano, daddyn Hanan duk ya lurada yadda Hanan take nan nan da Jawwad ya yadda ba karamin so takewa Jawwad dinba.

Bayan tafiyar su Mummyn Hanan tace "Daddy ka lurada yaron nan Jawwad kamarsa daya da Yusuf, wallahi hatta murmushinsa irin na Yusuf din Baba sagir ne"

"Na gani nima, Amma kamnin twins girl dina yafi fitowa, tun lokacin dana ganta nakeji ajikina kaman akwai alaka tsakaninmu, Amma ni yanzu abunda yake raina inason tuntubar mahaifinsu, indai Jawwad yana sonta yafito kawai, tunda naga hankalinta yafi karkata gareshi"

Kaman Mummy tayi masa bayanin yakusa Aure, amma tafasa tace "To Allah ya tabattar da alkhairi amma gaskiya ni na yaba da hankalin sa, gashi nutsatse"

Tunda suka taho hanya Jalal yayi shiru yakasa magana,

Jalila sosai take rashin lafiya, bata ko cin Abinci zuciyarta a cunkushe bata sha'awar komai, ga wani matsanancin ciwon kai dayake hanata bacci, ko makaranta bata iya zuwa, Nana tayi2 taje Asibiti tace mata ba wani matsala bane damuwa ce kawai take damunta,
Ta yunkura ta mike zata shiga toilet, kawai taji jiri gaba daya garin yayi mata baki kirin, aikuwa ta fadi a gurin tana fidda numfashi da kyar, Naja na kan gado tana kallon Jalila tace

" ahaka bakinciki da mugun abunki zasu hadu su kasheki, ki barmu a duniyar nida Jawwad muyi Aure, Allah yasa ki mutu shegiya"

Jalila tanajin Naja amma bazata iya motsa ko dan yatsanta ba Nana data dawo dauke da kofin tea ganin Jalila a kwance yasa ta jefar cup din tazo kanta da sauri tana girgizata, Jalila tasa hannu ta dafe kanta tace "Nana kaina ze fashe"
"Sannu Insha Allah ze dena ina zuwa"
Taje ta dakko youghurt a fridge tazo tana bawa Jalila danta fuskanci hada yunwa ke damun Jalila,
Naja ta kallesu tayi tsaki "Aikin banza wahalallu"

Tunda su Jawwad suka nufo kano, Jawwad yakejin faduwar gaba dan besan meze tarar ba dan shi yanzu ko zuwa gidan baya so, shikam Jalal se sakawa yake yana warwarewa, shi meye amfanin yin wani aiki, Jawwad yaji shirun yayi yawa dan haka yace "ya dai naji kayi shiru haka? Ko har yanzu baka yadda da aikinbe?"
Jalal ya danyi tsaki sannan yace "Jawwad nifa kaina yagama daurewa a ina Baban Hanan yasanni da harze bani aiki, kuma yana cewa sungama magana da daddy, yaushe akayi wannan zancen bansaniba? Tayaya zan fara hana wasu sha da fataucin miyagun kwayoyi bayan ni inayi? Ka gayamin tayaya?"

"wannan ba abun damuwa bane bafa, kaiba ruwanka da wani tone2 na meyasa aka baka aiki, kuma ai ansan kana shaye2 akabaka ko?"

Shiru Jalal yayi baya tunanin ze iya wannan aikin, tayaya za'ace me hana laifi yana aikatawa.
Haka suka cigaba da shiru kowannensu yana sakawa yana kwancewa har suka iso kano.

Jalila tunda ta danci Abinci tasha magana tasamu nannauyan bacci yayi awon gaba da ita.
Koda su Jalal suka dawo, kowa gidansu ya nufa, Jalal ya tafi gida, shima Jawwad ya tafi gidansu.
Kwana uku da zuwan su Jawwad kano, tunda suka dawo Jawwad baya shiga gidan saboda gudun fitina sam baya wuni a gidan.

Jalal yayiwa teddyn Jalila guri akan gadonsa, yana son yaganta yabata abunta sannan ya tambayeta ya akayi Alqur'ani daya bata yaje hannun Ilham? Har yayi wanka ze kwanta yaji kamar ana hura masa wuta a zuciyarsa da kansa gaba daya jikinsa ya dau zafi a sukwane ya nufi fridge dinsa ya ciki cikinsa da giya sannan yaji daidai.

Da safe Jalal yasamu daddynsa a daki yana bacci dayake saukar dare yayi, ba tunanin komai Jalal ya tasheshi, koda daddy ya tashi Jalal yafara jeramasa tambayoyi

"daddy da saninka aka samomin aiki a hukumar sha da hana fataucin miyagun kwayoyi?" daddy yace

"Dafarko dai ban saniba sedaga baya, General Abdurrashed ya kirani a waya, yacemin 'yarsa tanemi ya sama maka aiki a wannan hukumar in bazan damuba in turamasa CV dinka, shikenan na amince"

Jalal yayi saroro yana kallon Daddynsa
"Wace' yar tasa?"
"kai zan tambaya ai"
Shiru Jalal yayi, kawai ya mike ya sakko daga kan gadon daddy yafice daga dakin.

Jawwad yana dakinsa, Nana tazo tace masa Abba yana kiransa, haka ya tashi gabansa na faduwa, yana fatan Allah yasa ba wani laifin yayi ba, yana zuwa, ya tarar da 'yan gidan a palour banda Naja, Abba yayi shirin fita, Abba yace masa
"Jeka ka canza kaya, Bauchi zamuje yanzun nan"
Cikin mamaki Jawwad yace "Bauchi kuma Abba?"
"Eh bauchi mana, kayi sauri a yau nakeson mudawo"
Cikin Mamaki Maama tace "Abban Jawwad ni nakasa gane meke faruwa haka, tun jiya kake bacin rai, kaki saurarata yaukuma ba zato ba tsammani kace bauchi zaka tafi, mezakiyi a bauchi ne?"

Kallon ta ya danyi yace

"ba dole inki saurararki ba, ki shirya munyi magana da baban Jalal, ranar Lahadi shida 'yan uwansa zasu kawo kudin Auren mahmud da Nana, sannan zanje bauchi inne mawa ďana Auren' yar mutunci, sannan karki kuskura in dawo in tarar da yarinyar nan Naja a gidan nan, tabarmin gidana a yau"

"Amma meyasa?"

"in mun dawo kyaji meyasa"

Jalila dake gefe tace "Abba Allah ya kaiku lafiya, ka gaishemin dasu, kuma akwai wani albishir dana boye banyi maka ba sekaje bauchi zaka gani"
Abba yayi murmushi yace "to shikenan Baby, kema inason kafin lokacin bikin Nana ki fidda miji ku karasa karatun a dakinku" Jalila ta sunkuyar da kai tana murmushi, Abba kuma yasa kai yabar palourn.

Mummy tana zaune suna hira daddy a babban palour Jalal yashiga da sallama, suka amsa masa gaba daya, yaje kan Mummy ya tsaya fuskarnan babu alamar walwala ya jefa mata wata jarida a hannunsa yace

"ga shi nan yanada kyau ki duba Labari na uku a cikin wannan jaridar, yanada mahimmanci agareki"



Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️

What's app only 07063065680.

Continue Reading

You'll Also Like

7.2K 517 52
Labari mai saka rauni a zuciya bisa yarda aka yi watsi da zumunci aka martaba ku'di fiye da zumunci ta yarda ake gudun 'dan uwa makusanci a fi son ha...
86.6K 2.2K 32
A little AU where Lucifer and Alastor secretly loves eachother and doesn't tell anyone about it, and also Alastor has a secret identity no one else k...
709 65 13
Labarin soyayyar Aaliyah Badamasi Bulama da Sa'eed Aliyu Modibbo a shekarun 80's...
59.7K 2.7K 19
Wanan labari ne akan jarabawan ubangiji, yanason wata baiwar Allah mai suna Aisha ranan bikinsu ta mutu, bayan wani lokaci mai tsawo saiya hadu damai...