Default Title - ABDUL JALAL (...

By Ayshercool7724

56.5K 2.5K 216

Labarin wani matashi daya riga ya gurbata rayuwarsa da shaye2 da raina iyayensa, tareda wata matashiyar yarin... More

Abdul Jalal(2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 7
ABDUL JALAL (2020) 8
ABDUL JALAL (2020) 9
ABDUL JALAL (2020) 10
ABDUL JALAL (2020) 11
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 15
ABDUL JALAL (2020) 16
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 19
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 21
ABDUL JALAL (2020) 22
ABDUL JALAL (2020) 25
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 27
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 30
ABDUL JALAL (2020) 31
ABDUL JALAL (2020) 32
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 35
ABDUL JALAL (2020) 35
ABDUL JALAL (2020) 36
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 38
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 43
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 43
ABDUL JALAL (2020) 44
ABDUL JALAL (2020) 45
ABDUL JALAL (2020) 46
ABDUL JALAL (2020) 48
ABDUL JALAL (2020) 48
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 50
ABDUL JALAL (2020) 51
.ABDUL JALAL (2020) 53
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL part 2
part 2 55
ABDUL JALAL (2020) 56
ABDUL JALAL 57
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 59
ABDUL JALAL 60
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 63
ABDUL JALAL 64
ABDUL JALAL 65
ABDUL JALAL 66
ABDUL JALAL 67
ABDUL JALAL 68
ABDUL JALAL 69
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 72
ABDUL JALAL 73
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 74..
ABDUL JALAL 75
ABDUL JALAL 76
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 78
ABDUL JALAL 79
ABDUL JALAL 80
ABDUL JALAL 81
ABDUL JALAL 82
ABDUL JALAL 83
ABDUL JALAL 84
ABDUL JALAL 85
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 88
ABDUL JALAL (2020) 89
ABDUL JALAL 90
ABDUL JALAL 91
ABDUL JALAL 92
ABDUL JALAL 93
ABDUL JALAL 94
ABDUL JALAL 95
ABDUL JALAL 96
ABDUL JALAL 97
ABDUL JALAL 98
ABDUL JALAL 99
ABDUL JALAL 100
ABDUL JALAL 101
ABDUL JALAL 102
ABDUL JALAL 103
ABDUL JALAL 104
ABDUL JALAL 105
ABDUL JALAL 106
ABDUL JALAL 107
ABDUL JALAL 108
ABDUL JALAL 109
ABDUL JALAL 110
ABDUL JALAL 111
ABDUL JALAL 112
ABDUL JALAL 113
ABDUL JALAL 114
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL

ABDUL JALAL 61

355 20 4
By Ayshercool7724

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

_ABDUL JALAL (2020)_

_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)

PART 2
_PAGE 8️⃣/61_

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com

_MY FIRST NOVEL _

Wani irin Kallo Mum tayiwa Hanan

"I don't think you are in your senses, Hanan, kawartaki dukda yarinyar ba wani yimin tayiba, amma son da kike mata yasa na kyaleku tare, amma hakan bazesa inkasa gayamiki gaskiya ba, Hanan inkikayi haka baki kyautaba, hakan ba daidai bane, Jalila taana kaunarki meyasa zakiyi mata haka"
kwalla ce ta taru a idon Hanan

"Mummy ki fuskanceni banyi haka dan cin amanar Jalila ba, Mum wallahi makauniyar soyayya nakewa Jawwad, Mummy he is very nice and gentle, gashi salihi, Mum soyayyata da Jawwad mafita ce kuma ceton Jalila ne, inajinta a zuciyata kamar yar uwata ta jini, dan haka bazan iya cutar da itaba all i know is that inason Jawwad "
"Kamar yaya kenan, tayaya kike son maida karya gaskiya"
Labarin abunda ke tsakanin Jalal da Jalila tabawa Mummy, ta nisa tace

"Mum ko bankuma cewa komai ba kinsan Jalal is her e destiny, ita kadaice zata iya sadaukarwa domin ceton sa, Mum mahimmanci Jalal a rayuwarta ne yasa ake mata nuni da halin dayake ciki a mafarki, Mum kibani karfin gwiwa, zanyi meyuwuwa in dauke hankalinta daga kan Jawwad, sannan zan temaketa akan rayuwar Jalal" Jikin Mum ba karamin sanyi yayiba dajin labarin da Hanan tabata,
"Shikenan Auta, zancigaba dayimuku Addu'a Allah ya zaba abunda yafi Alkhairi".

Jalal cikin gida ya tafi domin samun yin hira da daddy, yana zuwa ya tarar da Ilham a babban palour da waya a hanunta tana waya, kota kanta bebi ba yanufi part din daddy, bayansa Ilham tabi da kallo

"muje zuwa Jalal zakaga tsiya" Jalal yana zuwa ya tarar da daddy a palour dinsa suna hira da mummy, daddy na ganinsa yai murmushi "dan halak kaki ambato, zancenka nakeyi a a raina karaso Dama inason ganinka dan gidan daddy"

"to gani mezaka bani, Jalal yafada yana zama akan kusa da daddy"

"Jalal magana nakeso muyi da kai, Mum dinka tazomin da magana nayi murna da jin hakan shine nakeson ji bakinka" Mummy tai farat tace
"Ba dai maganar da mukayi dazu bane, ai mungama magana dakai, meye kuma na tada wannan zancen, kayi abunda yakamata kawai" daddy yace
"A a Madam karmuyi gaggawa, dole mubi komai a sannu sannan inji ta bakin kowannensu" "A'a fa ai mungama magana wannan kawai maida hannun agogo baya zakayi"
Jalila da sallama ta shigo palourn, Ilham na palourn amma tai mirsisi taki amsawa, "Aminiya Ilham amsa sallamar ma seyazamo miki aiki, amsa sallama dabi ace ta kyakkyawan musulmi, karki zama irin yayanki nan mana" tsaki Ilham tayi tareda fadin
"meye hakane wai? Ke kullum in baki shiga sabgata ba bakyajin dadi ko? Ina ruwanki da nida danuwanane mayya"
"Aini indai a irin sha'anin nan ne to nafi uwar mayya naci, mayya in akayi magani ana samun nasara nikuwa babu abunda zakiyi kiyi nasara akaina, sannan duk abunda ba'aso ni shinakeyi dan aji haushi, and the most craziest part of me is that bana riko, yanzu zamuyi fada yanzu zan manta, duk abunda na rike a zuciyata nake fushi akansa to yanada mahimmanci a gurina, dan haka nibana gaba dake Ilham dan bakikai inyi hakan ba dake, sannan kuma bazan fasa bata miki raiba in har kikayi abunda yaci karo da Ra'ayina sedai kiyi hakuri "
Lallai Jalila tacika yar rainin hankali, wulakanci goma da ashirin.
Duk yada Mummy tayi a wayance kar Jalal yaji zancen nemamasa auren Ilham daddy yaki, karshe a fusace Jalal yace" waini meye hakane daddy, afadamin komene mana, inbaza ayiba meye na dakko maganar agabana, nibanason irin haka fa"
"Ohh ka kwantar da hankalinka yaron kirki, aiba abun tashin hankali bane, maganane me dadi akanka, maganane nacika maka burin rayuwarka, Mummy dinka tagama yimin bayani akan komai, nagame da abunda ke tsakaninka da Kanwarka Ilham, dan haka zanje muyi magana da mahaifinta asa rana, nayi farinciki da har kafara tunanin aure Jalal, cigaba yafara zuwa a rayuwarka kaga......

"Enough daddy" Jalal yai maganar a fusace, "Wannan maganar daga ina? Duk matan duniya in rasa wadda zan aura se wannan, in har farinciki kake nafara maganar aure, to da saurana, wait wai wama yagaya maka wannan maganar, kodayake base ka gayamin ba nasani," ya kalli mummy "Ke kika gaya masa nasan haka, nidake na taba cemiki ina son wannan yarinyar ne? Meyasa kikemin hakane, meyasa kikeson kuma rusa al'amuran rayuwata, ke a ganinki Ilham ta dace da zama matata, kimin adalci kiyiwa kanki mana, akoda yaushe kidena duba maslahar kanki kawai, kuma Ilham tunda Ubanta na raye se ta bar gidan nan, ai ba gidan ubanta bane ba, akanme za a dinga batamin rai haka, wallahi sena kakkarya yarinyar nan inga uban da ze tsayamata" daddy yai gaggawar mikewa da nufin tare Jalal amma Jalal ya kauce ya nufo hanyar fita,
Ilham taiwa Jalila wani mummunar kallo

"ai dama da ganinki base an fada ba ke mayyace, bari inkuma jadadda miki, duk maitarki kurwata data Jalal tafi karfinki haka kika ganmu haka zaki kyalemu, nidashi mutu ka raba"

Jalila tace
"to dan kincemin mayya ai ba haushi zanji ba, ko ina cin kurwa bazanci taki data Jalal ba saboda bazanci kazamar kurwa ba, kuma kina bani mamaki, dakikancinki yayi yawa Ilham bansan lokacin dazaki gane cewa niba abunda zanyi da wannan dan giyar ba, kuma kema dakike ta wahala akan se ya aureki don cikar burinki, ABDUL JALAL baze taba aurenki ba Ilham, tunda yace baya sonki baze sokiba, kuma kinsan daddyn sa yana goyon bayansa, nasan hanya dayace dake dazakibi ki aureshi hanyar sihiri kuma wannan hanyar bata bullewa"

da sauri Ilham ta kalli Jalila tanaso tayi magana amma takasa,

"Karya kikeyi, Yaya Jalal yana sona kuma bani da wani mugun nufi akansa, ubanwa yagaya miki saboda wani dalili nakesonshi, munafuka duk masifarki wallahi haka zaki kyalemu, dan banga uban daya isa ya hanani auren Jalal ba"
"Eh kinyi mamaki ko? Ya akayi nasani, da bakinki kika fada, ba a gurin wani naji ba sannan.....

" A gidan ubanwa na taba gayamiki ina sonki meyasa ba kya ganewa, sa'anki neni, mahaukaciyar inace ke dakike tunanin zan aureki? Yau zaki tattara kibar gidan nan tunda bana ubanki bane, akanme zaki dage cewar nikikeso nace bana sonki bana sonki meye haka wai, mekike nema a gurina ne Ilham"

Jalal ne yakewa Ilham magana cikin fada, da sauri daddy ya fito tareda Mummy, daddy ya karaso inda Jalal yake "haba Jalal ai duk abun be kai hakaba, koba komai kanwarkace, kayi hakuri"
"

" Daddy wace irin magana kakeyi hakane, seta bar gidan nan koni inbar muku gidan, akan me za a takurawa rayuwata, for what reason dad, ace kullum mahaifiyata batada buri se ganin bacin raina" Jalila rasa abun cewa tayi, ta kalli wannan ta kalli wannan,

"Haba Jalal ya ina matsayin mahaifiyarka zakace bana son cigabanka, Aurenka da Ilham alherine ni banga aibun Ilham ba, a tunanina komai ya wuce" wani mugun kallo Jalal yaiwa Mummy duk ya birkice idonsa yai jawur "Kikace komai yawuce, karki yaudari kanki mana, kodayake son zuciya baze barki kidinga ganin gaskiya ba, nayi dana sanin kasancewarki mahaifiyata, kullum bakida burin daya wuce gayyato matsala cikin rayuwar dan dakika haifa, haka sauran iyaye sukeyi"

Jalila kasa jure abunda Jalal yake tayi , wanda hakan yasa ta mike ta fice daga palourn jikinta a sanyaye, tafito ta jingina da bango tai shiru tana tunani "meyake damun Jalal ne? Dole nasan dalilinsa na cin zarafin iyayensa musamman mahaifiyarsa, ina tausayawa Jalal ya mutu yana sabawa iyayensa, zanso inji dalilin hakan kozan iya temakamasa, wulakanta iyaye ba abune me sauki ba"
Ilham se kuka take, duk yadda daddy yaso ya shawo kan Jalal ya kasa, seda yai me isarsa sannan ya bude palourn ya fito a fusace, yana fitowa Jalila tana gurin a tsaye akan hanyar daze wuce, hannu yasa ya hankadeta gefe yai gaba abunsa ya nufi part dinsa, mamakine yacikata, kodayake ba abun mamaki bane kadan daga aikin giya.

Jiki a sanyaye ta baro gidan, sedai me tana fitowa taga motar Hannah a kofar gidan, ta fito tana ta kiran lambar Jalal amma yaki dagawa. Jalila a ranta tace "lallai Jalal kana cikin iftila'i" dayake duhun magariba yafara yi, Hannah bata gane wacece ba, dan haka tace "Dan Allah baiwar Allah naga kaman daga gidan kika fito Jalal na ciki ne?"
Karasawa Jalila tayi gabanta

"kalli da kyau baki gane wacece bane?" se yanzu Hannah taganeta "dama kece?
" Eh nice, meyasa bakyajin kunyar zuwa neman Jalal ne? Mace da aji akasanta abunda kike zubarda mata kike"

"Ke kome nakeyi beshafeki ba kingane bana son surutu, Jalal yana nan ne?"

"Eh Jalal yana nan, amma kaman yanda nagaya miki kwanaki yauma hakanne baze zoba, huwaila kike kowa, ni mamaki kike bani meyasa bakida kunya ne, me yayi miki haka kika uzzurawa rayuwarsa"
"Ke dakata, ba abunda yadameki, Ko agaban uban waye zan fada son Jalal nake, nan da kankanin lokaci ze aureni" murmushi Jalila tayi "to Ilham dinfa? Kokina tunanin zuba miki ido zatayi ki aureshi, naga kaman tafiki sonshi dan tafiki himma ina tunanin za'asa sa ranar aurensu" zare ido Hannah tayi "dagaske kike?" "nasankine dazan tsaya ina miki wasa"
"Ni Jalal zewa haka wallahi basu isaba dagashi har kanwar tasa, Nikadai zan aure Jalal in rayu dashi sena lalata komai, in bahakaba sena masa sharrin da nan duniya babu wanda ya isa ya fiddashi, nayi wannan alkawarin" "kaman ba yanzu kika gama cewa kina son aurensa ba, kin dade kina cutar da rayuwarsa, ranar birthday dinsa kun shirya yimasa wani abu, ni nasaka aka dauke shi daga gurin bayan kin bashi kwaya kin bugar dashi, a wannan lokacin nakara tabattar da bakinku daya da da wannan dan iskan, sannan kisani babu wani sharri dazakiyi masa yayi tasiri akansa Allah yana tareda shi, dan haka wannan ba soyayya bace, ba kyasonsa dan Allah, ku saurari yadda karshenku ze kasance " Jalila ta juya tai gaba, da sauri Hanna tabi bayan Jalila tana mata magana akan dan Allah ta tsaya, amma Jalila taimata banza tai wucewarta zuciyarta cike da tunani. Ba karamin mamaki Hannah tayiba, gaskiya Jalila tabata mamaki ya akayi haka, dama ita tasaka aka dauke Jalal, ita ta turasa wannan shirin da suka dade sunayi, to meye manufar Jalila akan Jalal.
Jalila kam Tana zuwa gida ta tarar da Nana ta dawo daga gidan Yaya mairo, ta tarar dasu a palour Nana tana kuka, Maama tana rarrashinta, kaman ta wuce seta fasa ta tsaya "Nana lafiya kuwa"

"ke bana son gulma ina ruwanki, wuce kitafi inda zaki, uwar tsegumi kawai" ba Jalila ba hatta Nana seda taji babu dadi abunda Maama tayi.
Dakinsu ta wuce taje tai alwala tai sallar magariba, tafara tilawar al'qur'ani, wayarta se ringing takeyi amma bata dauka ba harseda ta idar da karatunta, tana duba wayar bakuwar lamba ce da akayi ta kiranta da ita ranan, dan haka ta ajiye tacigaba da sabgoginta, har bayan sallar isha'i Nana bata shigo dakin ba Jalila kuma bata nemeta ba, wayarta ce takuma daukar ringing, a fusace Jalila ta dauka

"Wai ya hakane ankira ban daga ba kuma se kuma kira ake, haba inkuma ina wani uzurinne fa?"
"Tuba nake, adon gari, nakasa samun sukuni ne amin afuwa"
"waima wake magana?"
"Suleman ne" "waye kuma Sulaiman ni bansan wani suleiman ba" "yi hakuri, wanda kuka hadu shekaran jiya kika bashi lambarki" seda Jalila ta dan yamutsa fuska dan ita ta manta dashi,
"ohh nagane sannu yakake?" "lafiya amma ba lauba, nakira nakira baki daga ba, inata kewar muryar nan taki" "Hmm to ai yanzu gashi kaji" "Hakane nayi farinciki fatan kina lafiya" "eh lafiyata kalau" haka sukayi waya da Jalila kaman ammata dole, ita kunya ma yake bata da haushi inyayi wani abun tsoho dashi se wani tabara yake mata.
Nana ce ta shigo jikinta a sanyaye, Jalila bata kulata ba taje tazubo abincin dare tanaci, bayan tagama tai shirin bacci ta haye gado tana chatting dinta, Hanan tana online, suka fara hira kaman abun arziki, har Jalila take bata labarin Alhaji Kabiru, dakuma wannan dansandan, Hanan tabata shawarwari, Jalila tagaya mata abunda yafaru yau agidansu Jalal, Hanan ta fara kunna Jalila "queen gaskiya Jalal is destined to be in your life, dan haka ki kauda wata Ilham da Hannah gefe kisa kai dan kun dace sosai, ke kadaice zakiso shi tsakani da Allah ki temaki rayuwarsa"
"Ke bana son shirme Allah ya kiyaye meye abunso a gurinsa, meye abun birgewa a gurin mashayin giya"
"A'a adena zakewa dai, kar nan gaba azo a gigice akan sa ehee dan bazan bawa mutum shawara ba"

"Narasa meyasa kike likamin wannan sakaran, inada Yaya Jawwad ba abunda zanyi da wani Jalal"

"Ke dakata, Jawwad nawane kuma ni kadai, gara ki rungumi Jalal tun lokaci be kuremiki ba, Jawwad baze aureki ba nina gayamiki" rufe data Jalila tayi, dan hartaji wani bacin rai yana tasomata"

Nana ta kalli Jalila tace
"Jalila bazaki tambayi meyasameni bako? Kina kallo ina cikin wani yanayi" tashi Jalila tayi takoma kusada Nana "Nana hawayen nan naki jinake kaman ni nake zubar dashi, kinji abunda Maama tace dazu, shiyasa ban takuramiki inji meyasaki kuka ba bansaniba kobe shafeniba"
"haba Jalila har akwai abunda ze sameni dabe shafekiba?" "to yanzu kiyi hakuri gayamin meya faru?" Nana ta share hawayenta sannan tace
"Jalila wai kiran da yaya mairo tayimin, waiso take ta hadani da Nura waiya aureni"
"Waye kuma Nura" "babban danta ne, wallahi Jalila inda abunda natsani na bude ido ingani be wuce wannan Jakinba" "Amma Nana meyasa?"
Wasu hawayen ne suka kuma zubowa Nana "Jalila dan dabane fa, mugun tantirine har prison yayi, ga shaye shaye na masifa, ba ilimin addini bokon ma secondary ya tsaya, wai dan zalunci shi takeso ta hadani aure dashi, wallahi akace sena aureshi sena kashe kaina, inkuwa aka kaini gidansa sena ksheshi na kashe kaina"
Da sauri Jalila ta rufemata baki tareda fadi "subhanallah, Nana karki kara fadin hakan, wannan maganar tayi tsauri, amma me Maama tace?" "cewa tayi inyi hakuri, zatasan matakin dazata dauka, nikam hakan beminba kawai ajanye wannan maganar, inbahakaba gara in bar gidan nan" "Nana nace kidena irin wannan zantukan mana, kiyi amfani da kwakwalwarki, kina tunanin Abba ze yaddane, baze yadda ba dan haka kiyi hakuri, ba abunda zesa ki aureshi Insha Allah mutumin kirki zaki aura, zan tayaki addu'a kinji My Nana kidena kuka, banaso" gyada kai Nana tayi sannan tace "Saboda tsabar son zuciya irin na matar nan waishi kuma Yaya Jawwad da Naja za'a hadasu, wallahi inshi ya yadda nibazan yadda da auren dan daba ba, gara in kashe tsinanne in huta"

Comments nakeso ba sticker ba, kokuma just thanks,
A kullum ina alfahari daku masoya wannan novel
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
07063065680

Continue Reading

You'll Also Like

1.4M 117K 110
Kalmar QADDARA kalma ce dake rataye bisa wuyan kowanne bawa,haka rayuwa ta gada,tafe take da QADDARORI kala kala,masu zaqi da akasin haka...
709 65 13
Labarin soyayyar Aaliyah Badamasi Bulama da Sa'eed Aliyu Modibbo a shekarun 80's...
86.3K 2.2K 32
A little AU where Lucifer and Alastor secretly loves eachother and doesn't tell anyone about it, and also Alastor has a secret identity no one else k...