Default Title - ABDUL JALAL (...

By Ayshercool7724

56.5K 2.5K 216

Labarin wani matashi daya riga ya gurbata rayuwarsa da shaye2 da raina iyayensa, tareda wata matashiyar yarin... More

Abdul Jalal(2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 7
ABDUL JALAL (2020) 8
ABDUL JALAL (2020) 9
ABDUL JALAL (2020) 10
ABDUL JALAL (2020) 11
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 15
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 19
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 21
ABDUL JALAL (2020) 22
ABDUL JALAL (2020) 25
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 27
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 30
ABDUL JALAL (2020) 31
ABDUL JALAL (2020) 32
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 35
ABDUL JALAL (2020) 35
ABDUL JALAL (2020) 36
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 38
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 43
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 43
ABDUL JALAL (2020) 44
ABDUL JALAL (2020) 45
ABDUL JALAL (2020) 46
ABDUL JALAL (2020) 48
ABDUL JALAL (2020) 48
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 50
ABDUL JALAL (2020) 51
.ABDUL JALAL (2020) 53
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL part 2
part 2 55
ABDUL JALAL (2020) 56
ABDUL JALAL 57
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 59
ABDUL JALAL 60
ABDUL JALAL 61
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 63
ABDUL JALAL 64
ABDUL JALAL 65
ABDUL JALAL 66
ABDUL JALAL 67
ABDUL JALAL 68
ABDUL JALAL 69
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 72
ABDUL JALAL 73
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 74..
ABDUL JALAL 75
ABDUL JALAL 76
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 78
ABDUL JALAL 79
ABDUL JALAL 80
ABDUL JALAL 81
ABDUL JALAL 82
ABDUL JALAL 83
ABDUL JALAL 84
ABDUL JALAL 85
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 88
ABDUL JALAL (2020) 89
ABDUL JALAL 90
ABDUL JALAL 91
ABDUL JALAL 92
ABDUL JALAL 93
ABDUL JALAL 94
ABDUL JALAL 95
ABDUL JALAL 96
ABDUL JALAL 97
ABDUL JALAL 98
ABDUL JALAL 99
ABDUL JALAL 100
ABDUL JALAL 101
ABDUL JALAL 102
ABDUL JALAL 103
ABDUL JALAL 104
ABDUL JALAL 105
ABDUL JALAL 106
ABDUL JALAL 107
ABDUL JALAL 108
ABDUL JALAL 109
ABDUL JALAL 110
ABDUL JALAL 111
ABDUL JALAL 112
ABDUL JALAL 113
ABDUL JALAL 114
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL

ABDUL JALAL (2020) 16

310 24 0
By Ayshercool7724

.🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

    _ABDUL  JALAL_
           (2020)

      _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
    (Daddy's girl)

               PAGE-  16&17

PART 1

  _Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa,  ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta  wannan littafin yi magana ta what's app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

🌹https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

I want comments not stickers or just thanks😢😢😢😢
Your comments give me courage

Aimin afuwa the page is not edited
         -my first Novel-

Innalillahi wa inna ilaihi raji'un shine abinda Jalila ta fada jikinta a sanyaye
A hankali ta sauke wayar daga kunnenta ta kashe wayar
Takalli siyama
"Aminiya ya tafi"
Yasalam shine abinda siyama ta furta

"Kwantar da hankalinki har yanzu da sauran lokaci ai"
"Kwanciyar hankalifa babu shi Aminiya dan bakiji yadda zuciyata take min bane
Bari in tafi Gida uumi tace kar in dade kuma kinga nabata lokaci bari in tafi kawai"
Har gate Siyama ta rakota tana bata kwarin gwiwa, tare da bata shawarar cigaba da addu'oi
Sannan ta mata alkawarin zatazo har gidan taji yadda akayi
Haka Jalila ta tafi Gida jikinta a mace
Yanayin fuskar Ummi ya nuna mata tayi fushi da ita
Dan se basar da ita take Jalila ta rasa meyake mata dadi

Jeje ne a tare da wani mutum a cikin mota me tint glass yasaka wando three quarter da wata Yar Riga Mara hannu suman nan tayi tsage²
Kai daka ganshi ka ga dan iska

"Katabbatar kayi abinda yakamata in kukaje kasan abinda ya dace kayi shima wannan aikin naka akwai kaso me tsoka ka tabattar da aikin nan ya tafi dai² "
Mutumin yayiwa jeje maganar

"Considered it done my boss zan tabbatar da aikin nan ya tabbatat"
Jeje yafada yana dan risinar da kai
"Good"
mutumin yafada cikin Isa
Sannan jeje ya bude kofar motar ya fita ya dauki akwatinsa
Inda sukayi zasu hadu da Jalal yaje ya tsaya ya kirashi a waya yan mintuna kadan sega Jalal ya karaso
Shima
"hmm yau kayi abun arziki ka cika alkawari"
Murmushi Jeje yayi
"ba dole ba my boss ina ciki farin ciki"
"Good yanzu se mu tafi ko"
Gaban Jalal ne yai mummunar faduwa
Meyake damuna ne haka, menake shirin yine"
Jalal yake maganar a zuciyarta

"Yanaga kana tafiya kuma a hankali yanzu ko akwai abunda yake damunka" Jeje ya tambayeshi
Girgiza kai Jalal yayi
Jeje ne yafara mika passport dinsa aka duba aka bashi ya danyi gaba yana jiran a duba na Jalal,
Jiki a sanyaye Jalal ya mika passport dinsa

(Karka kara kirana dan uwanka Jalal niba dan uwanka bane, tunda zaka iya manta soyayya da shakuwar dake tsakaninmu ka tsallake ka barni,
Tun tasowata bani da dan uwa namiji ban budi ido da kowa ba a matsayin aboki dan uwa sekai,!!!!!)

Maganganun Jawwad ne suke dawo masa dakuma tsantsar damuwa da hawaye da ya gani kwance a idon Jawwad su yake tunowa se yaji zuciyarsa ta cunkushe bakin ciki ya ziyarci zuciyarsa, gaskiya ba karamin kauna Jawwa yake masa ba in ya tafi beyiwa kansa adalci ba Jawwad wani bangarene me mahimmanci a rayuwarsa ga kuma mahaifinsa, anya inyayi tafiyar nan yayiwa kansa adalci
jikinsa ne yayi matukar yin sanyi, hannu yasa ya karbi passport dinsa ya juya dabaya yafara tafiya
"Jalal ya haka lokaci fa inazaka jene"
Jeje ya tambayeshi
Bebashi amsa ba yacigaba da tafiya da gudu Jeje ya taho ya sha gabansa
"Man wai meyafaru ne ?
Ina zakaje yanzu fa jirginmu ze ta shi"
  "Zaka iya tafiya nikam na fasa"
Zaro ido Jeje yayi "why meyasa zaka fasa"
"Saboda haka naga dama nace in zaka ka tafi ni na fasa"
Ya bashi amsa
JALAL yayi maganar a tsawace

Wayarsa ya dakko ya kira Jawwad, amma be daga ba taita ringing
Jawwad yana kallon kiran yaki ya amsa seda takusa katsewa sannan ya daga wayar
"Kazo ka daukeni a airport"
"Kamar ya?"
Jawwad ya tambayeshi
"Ina airport nafasa tafiyar kazo ka daukeni"
"Bazan zo ba dacan ni na kaika"
"Idan bakazoba zan tafi u know I mean what I said"
"Ohh sorry gani nan zuwa"
Wai dagaske ya fasa tafiyar Jawwad ya tambayi kansa da sauri ya mike ya dau mota ya nufi airport

Ummice take lazimi akan dadduma gidan shiru kaman ba me rai a cikinsa
Jalila tana can dakinta tana duniyar tunani
Ummi ce ta dinga kiranta takirata ya kai sau uku sannan taji ta amsa
"Jalila zonan"

"To Ummi gani nan zuwa"
Mikewa tayi ta nufi dakin Ummi taje gabanta ta zauna
"Ummi gani"

"Naganki ai, Jalila wai meyake damunkine kwata² yan kwanakin nan kaman baki da lafiya baki da walwala Sam
Meyake damunkune baki da Wanda zaki gayawa matsalar ki fiye dani baki da aiki se tunani
My dear tell me what's actually wrong with you bana jin dadin ganinki a haka"
Tausayin ummine yakamata taji kaman ta gayamata gaskiya amma seta fasa
"Ummina babu abunda yake damuna kawai surutan danake da daddare ne da mafarkai bana so"
"Eyyah sorry my dear kinji tunani baze hana faruwar komai ba addu'a zaki dingayi nima inayimiki Komene Allah zemiki maganinsa"
Haknan se Jalila taji hankalinta ya Dan kwanta
Zame jikinta tayi a hankali ta kwanta akan cinyar ummi
Tanata ambaton Allah a zuciyarta domin tasamu zuciyarta ta rage bugun da take

Ba a dau dogon lokaci ba Jawwad ya karasa airport Jalal ya hango a zaune jeje yanata lallaba shi
"Tir da wannan dan iskan bawan, mtseeww"
Jawwad yafada a hankali

Jalal yana hango Jawwad ya mike
"Dan uwa dagaske ka fasa tafiya"
"Nafasa Jawwad kona tafi bazan samu nutsuwa ba zuciyarta tana Nigeria tare da Dan uwana"
Rungume juna sukayi kaman zasu shige jikin juna
Wani mugun kallo Jeje yayiwa Jawwad
"Wai dagaske fasawar zakayi?"
Jeje ya tambayeshi a fusace

"Jeje nafasa tafiya bazan juri ganin kwalla da bacin rai a idon Jawwad kamar yadda nafada maka kona tafi dubai zuciyata tana Nigeria"
Jawwad ne yaja trolley Jalal yasaka a boot, ya bude masa motar ya shiga
Jeje ne ya zagayo gaban Jawwad yai masa magana kasa²
"Yadda ka bakantamin yau ka rubuta ka ajiye komai Daren dadewa se na bakanta maka fiye da yadda kayimin"
"Allah ya fika"
Shine amsar da Jawwad ya bashi
Ya shiga ya kunna mortar suka tafi Jeje kaman yayi hauka gaba daya shirunsu ya rushe shi beasan meze gayawa boss dinsa ba
Naushi ya kai cikin iska kamar mahaukaci
"Fuck you Jawwad, indai muna raye sena kuntata maka kamar yadda kayimin "

A hankali wani bacci me dadi ya dauke Jalila akan cinyar Ummi se ajiyar zuciya take kaman wadda ta wuni tana kuka
A hankali Ummi ta shafa kanta Allah yayi miki maganin abunda yake damunki baby na
Duk da yamma tayi Ummi bata tashe ta ba ta kyaleta saboda in tayi wannan farkawar cikin dare bata komawa bacci
Se gefin magariba Jalila ta farka tana farkawa da bugun zuciyar nan ta farka
"Ya salam"
ta fada a hankali
"To dagani tunda kin tashi"
"Ummi ki Dan kyaleni mana in gama hutawa ni dama xaki goyani"
Ture kanta Ummi tayi ta mike ta tafi dauro alwala
A hankali taji bugun zuciyarta tana komawa normal
Ringing din wayarta ta jiyo a dakin ta da sauri ta mike ta tafi ta daga wayar lambar siyama CE
"Aminiya ya ake ciki kuwa ?"
"Oho"
"Kaman ya oho ya tafin ne? Kinkuma tambayar Yaya Jawwad?"
"Aminiya mezan tambayeshi ne ?ya rigada yacemin ya tafi se dai kuma addu'a kawai"

" banji dadi ba aminiya
Allah ya kiyaye ya tsare se mucigaba da addu'a amma ina ji a jikina kaman betafi ba"

"Tab wannan uban taurin kan to Allah yasa amma tunda ya furta seya tafi"

"Insha Allah be tafiba gobe in Allah ya kaimu ki shirya da wuri mutafi islamiyya karki jamana dukan makara"

"Insha Allah aminiya"

"Wani irin sha³ ne kai jeje why do you failed this mission, after all u know na Dora burina akan wannan tafiyar dazukuyi meyasa?'
a wannan tafiyar naso dawwamar da bakin ciki a zukatan ahalinsa na har abada"?
Mutumin dazune da ya kai jeje airport a motarsa yake maganar cikin fada

"Am sorry sir amma ba laifina bane wannan abokinnasa ne ya hana shi"
"Wa kenan"
Mutumin ya fada cikin fada
"Wannan mayen nasa Jawwad, saboda shi ya fasa tafiyar"

"Jawwad ko? Yayi kyau zan tabbatar masa da ba a shiga hanyata semun bar masa mummunan tabo a cikin zuciyarsa Wanda har gaban abada baze goge ba, dama shine yakemana karan katsaye a al'amuranmu zamuyi maganinsa"
"Hakan shine mafita ayi maganinsa kawai"
Jeje yayi maganar da sauri

Har cikin Gida Jawwad Yakama hannun Jalal yashiga dashi yan gidan duk suna parlour ILHAM.tana zaune  tayi shiru tana tunani
Yayinda mummy keta rusa kuka daddy yana rarrashinta
Jawwad ne yayi sallama gaba daya suka daga kai domin amsa sallamar
Kawai sesuka ga Jawwad tare da Jalal
Jawwad ya janyo hannunsa zuwa cikin palour
"Gashi nan ya fasa tafiyar hankalinku ya kwanta, mummy kukan ya isa gashi ya dawo"
Jawwad ya fada yana kallon mummy
To Alhamdilillah nima ba a son raina ya tafi ba, ba yadda zanyi ne tunda ya dawo se muyiwa Allah godiya
Ita kam Ilham bakinta ne yaki rufuwa
Mummy da gudu ta mike taje ta rungume Jalal tana cigaba da kuka hada sheshsheka

Kunsan d'a da uwa karo na farko bayan lalacewar Jalal da yaji kukanta ba dadi a zuciyarsa
"Kukan ya isa ai tunda gani na dawo
Ki godewa Allah ki godewa Jawwad Bazan iya tafiya in barshi da kewata ba"
Jalal yai maganr yana kallon Jawwad

Mummy kasa magana tayi se daddy da yake kokarin godewa Jawwad
"Haba daddy kar kasa inji kunya mana bakomai "
Nima Jalila ce takara fargar dani abu me mahimmanci Dana kusa mantawa thank you sweetheart Yayi maganar a zuciyarsa

Sannan ya mike yai musu sallama ya tafi Gida
yana zuwa ya dau wayarsa Layin Jalila ya kira domin ya gaya mata Jalal ya fasa tafiyar amma bata dauka ba

ILHAM tana Shiga daki tayi wani tsalle tare da jefa hannunta sama tace yes key tasaka wa kofar dakin ta sannan ta dawo ta dauki wayarta ta kira layin mahaifiyarta
"Hello Mami"
"Na'am ya ake cikine?"
"Albishirinki"
"Goro"
"Yafasa tafiyar nan dazu Jawwad ya kawo shi Gida yafasa"
"Ke dan Allah dagaske koda wasa"
"Wallahi mami ya dawo"
"Kai amma Jawwad din nan ya kyauta, ya saukaka mana aiki"
"Wallahi kuwa mami"
"To yanxu dai ba sanya zamuyi ba, ki kara dagewa Ilham duk randa burinmu ya cika sekin fini amfana"
"Insha Allah mami zan dage"
"Yawwa yarinyar kirki se na jiki"
"To mami ki gaida mutan gidan"
"Yawwa zasuji"

"Jalila kinga gidan Maman annur ta haihu ban samu na shiga naga babynba zo muje,
Muyi mata barka"
"Ummi wai ita barkan nan dole ce tunda dai bata mutu ba da ranta"
"Ohh ni maryam Jalila mutum ya dau ciki wata Tara ya sauke lafiya tsakanin mutuwa da rayuwa ai aje acemasa barka"

"Ummi naje gobe in Allah ya kaimu yanzu bana jin dadin jikina"
"To Allah ya sawwake miki zo ki rufe kofar gidan"
Jalila tabi Ummi ta rufe gidan sannan dawo cikin Gida ta dakko wayarta ta dawo palour ta Missed call din Jawwad ta gani
"Yasalam yaushe Yaya Jawwad ya kirani ban Sani ba"
Kiransa tayi ya katse kiran sannan ya kirata
"Abunda zan gaya miki ya Riga ya wuceki tunda baki daga wayar ba, se yanzu"
Cike da shagwaba Jalila ta fara magana
"Haba yayana na kaina bangani ba ne se yanzu amma tuba nake ranka ya Dade"
Murmushi yayi
"Sisyna ta wa ni kadai"
"Nanan fa?"
"A'a banda ita"
"Sena gaya mata"
Dariya sukayi gaba daya
"Yayana me yasaka farinciki hakane labarta min"

"Kece Jalila"
"Nikuma"
"Eh mana"
"Ya akayi nasaka farincki"
"Saboda kin tunatar dani abu me mahimmanci
Jalal wani abokinsa ne ya zigashi yayi tafiyar nan Wanda ni da Sam banyi tunanin hakan ba kuma nasan da wata manufar ya zigashi, kuma wai tare zasu tafi
Yanzu dai zancen danake miki Jalal yana Gida yafasa tafiyar ya dawo"
Wata nannauyar ajiyar zuciya Jalila tayi
"Alhamdilillah am glad to hear this from you Allah yakara kiyayewa ya shiryeshi"
"Ameen sisyna muna godiya da gudunmuwarki
Allah yasaka da mafificin Alkhairi ya jikan Abeenmu"
"Ameen dan uwan da babu irinsa"
"Ki gaida ummina"
"Zataji insha Allah na gaida maama,"
Sukayi sallamaa Jalila tace Alhamdilillah
Siyama ta kira ta labarta mata sukayi ta murna tare bakin Jalila yaki rufuwa

Bayan Ummi ta dawo ne ta lura da farin cikin da Jalila take sewani walwala take
"Waime ya farune naga kinata wannan farincikin haka baby gayamin mana"
Dariya Jalila tayi
"Hajiya Ummi ba komai kawai tsintar kaina  nayi cikin farin ciki Mara misaltuwa"
"To Allah yasa alkhairine"
"Ameen ummina"
Haka Jalila tayi kwanan farin ciki Allah ya temaketa yau batayi mafarkan ba balle a tsorata ta
Lokacin tafiya islamiyya yayi yan matan sun dau guga a cikin dogayen hijjaban makaranta suna tafe suna hira yau fuskar Jalila fes ba wata damuwa Dan haka yau ajinsu suka tabbatar ta dawo banda hira da surutu ba abinda sukeyi ana hirar yaushe gamo wasu na mata tambayar meyasa randa tazo bata walwala kwanakin nan sunyi missing dinta
Hayaniyar ce ta ishi malam Naziru ya fito Dan ya tsawatar musu
Yana zuwa Jalila yayiwa kashedi
"Yau malam baya nan balle ya ceceki wallahi naji surutu a ajin nan babu ruwana ke zan zanewa jikinki"
Befi yan mintuna da tafiya ba Jalila tabasu sabon topic suka barke da hira hada shewa itakuma ta silale ta gudu ta bar ajin ta nufi babban aji
Malam Naxeeru ne yakuma komawa domin casa yan ajin kuma ya kudiri takan Jalila ze fara
Yana zuwa ajin ya nemeta yarasa ya tambayi tana ina sukace basu saniba aikuwa suka sha jibga yayinda uwar gayya ta fece sun daku ragwaye na kuka, yayinda masu karfin hali kena zuci Dan malam Naziru ya iya bulala,

"Tsinanniyar yarinya ta jamana duka ta gudu shegiya azzaluma wallahi ban yafe ba"
Cewar wata daliba aikuwa a fusace siyama ta juyo

"Allah ya isanki ta biki haba lubabatu ai ba matsa bakinki tayi tace kiyi magana ba kuma Jalila ba shegiya bace"

"Nafada wallahi ban yafe ba"
Lubabatu ta maimaita
"Ke nima ba yafewar nayi ba wallahi wannan azabar dukaa itakuma ta gudu"
Wata dalibar tayi magana Siyama na kokarin tarewa Jalila wasu suka hayayyako mata ana haka Sega Jalila ta dawo gaba daya sukayi tsit saboda sunsan hali indai bakine Jalila akwai baki
Ba'a kada ita a fanni surutu
"Yanaji ana surutu amma ina shigowa naji anyi tsit"
"Aminiya ba komai hira kawai mukeyi,
Amma fa malam Naziru yace yau in yakamaki kashinkj ya bushe"
Siyama ta fada tana dariya
"Hh base ya ganni ba ai bazan bari mu haduba indai yaune"

Ilham ce ta sha kwalliya kaman ka saceta ka gudu se karairaya take ta shirya abinci a Warmer's ta nufi part din
Jalal ba kowa a parlour dan haka ta aje a parlour ta karasa bedroom dinsa
Dogon wando ne ajikinsa se vest ya na gefen gadonsa yana ta busa shisha
Sallama tayi da mamakinta taji ya amsa, a hankali ta tako gabansa cikin iyayi tafara magana
"Yaya dama mummy ce tayi girki tace in kawo maka"
"Ina abincin"?
Yai maganar kaman ba yaso
"Yana parlour"
Gyada kai yayi
"Thank you"
"Amma zakaci ko?"
"Maybe"
Shine kawai abinda yace seda ta juya zata tafi ya daga kai ya kalleta
Ganinta yayi kamar wata balbela, gashi se wani kariraya takeyi sam bata da wani shape se tsawo amma fara ce tas
Murmushi yayi a ransa yarinya Karama amma ta iya wannan shirmen ya Dan ja tsaki
Itakam fita tayi tana addu'ar Allah yasa yaci abincin nan

Kamar yadda Jalila tafada har aka tashi bata hadu da malam Naziru ba sunyo ayari guda yan ajin su daba yan ajinsu ba kowa na kokarin bin hanyar gidansu,
Anzo layinsu lubabatu suka tarar da yayan lubabatu a bakin hanya da abokansa se shan sigari suke ga tarin karnuka a gabansu kaida kagansu kaga yan daba
Jalila tare suke tafiya da su lubabatu seda sukazo dai² inda matasan nan suke Jalila secewa tayi
"Tab Siyama kinsan wani abu
ga irinsu Jalal da gayyar abokanan Sa baki kullum cikin hayaki, kalli yadda bakin yayan lubaba yayi saboda zukar taba lebensa duk ya zazzage,
Ni bansan ya akayi bakin Jalal bezama haka ba wai shantu"

Wata ashar yayan lubaba yasaki yayo kan su shida abokanansa tareda karnukan kankace meye wannan ayarin yan makaranta sun watse ba kowa a hanyar
Jalila ta dinga dariya yan mata manya da kanana sun zage sun kwashi gudu
Sukace gaskiya gobe insha Allah se mun kai karar yarinyar nan gurin malam aja mata kunne
"Jalila lafiya kike ta haki haka ?"
"Bakomai Ummi karnukan bakin anguwane suka biyomu"

Jalal ya bude Warmer's dinda Ilham ta kawo yaga cous² tsaki ya ja lallai ma yarinyar nan tasan bayacin wannan abun amma shine aka kawo masa rufewa yayi ya tafi gidansu Jawwad Dan samun abinda zeci a can
Ya tarar Jawwad yatafi masallaci dan haka ya nemi guri ya zauna yana jiran dawowarsa

Wayar Jawwad ce ta dinga ringing ta cikawa Jalal kunne Dan haka yaje ya dauka da nufin fadawa me kiran me wayar baya nan
Ya daga wayar yasaka a kunnensa

"Hello yayana "
Shiru yayi be amsa ba
"Yaya Jawwad yanaji kayi shiru bakajine?"
"Bashi bane"
Ya bata amsa a takaice
"Au Ashe Kaine ya akayi kafasa tafiyar,
Kacigaba da rashin ji kana biyewa abokan banza wataran se sun jaka inda zasu kasheka"

Share please
More comments more typing........

🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️

Continue Reading

You'll Also Like

1.2M 37.1K 100
Matar shi ce ta farko bata san haihuwa, idan ta samu ciki sai ta zubar, as ending yake yin auren sirri da mai aikin gidan
86.2K 2.2K 32
A little AU where Lucifer and Alastor secretly loves eachother and doesn't tell anyone about it, and also Alastor has a secret identity no one else k...
13.7K 450 56
labari ne data kafu aka kadara🙇🙇 Kubiyoni ku ji yanda LabariDr. Essha Ahmad zata Kaya da Young Tycoon Namji Mai ji dankashi Aliyu Umar Tycooon 💃...
31.4K 1.4K 9
Story of a young blind Fulani girl👸🏻