Default Title - ABDUL JALAL (...

بواسطة Ayshercool7724

56.5K 2.5K 216

Labarin wani matashi daya riga ya gurbata rayuwarsa da shaye2 da raina iyayensa, tareda wata matashiyar yarin... المزيد

Abdul Jalal(2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 7
ABDUL JALAL (2020) 8
ABDUL JALAL (2020) 9
ABDUL JALAL (2020) 10
ABDUL JALAL (2020) 11
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 15
ABDUL JALAL (2020) 16
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 19
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 21
ABDUL JALAL (2020) 22
ABDUL JALAL (2020) 25
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 27
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 30
ABDUL JALAL (2020) 31
ABDUL JALAL (2020) 32
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 35
ABDUL JALAL (2020) 35
ABDUL JALAL (2020) 36
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 38
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 43
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 43
ABDUL JALAL (2020) 44
ABDUL JALAL (2020) 46
ABDUL JALAL (2020) 48
ABDUL JALAL (2020) 48
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL (2020) 50
ABDUL JALAL (2020) 51
.ABDUL JALAL (2020) 53
ABDUL JALAL (2020)
ABDUL JALAL part 2
part 2 55
ABDUL JALAL (2020) 56
ABDUL JALAL 57
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 59
ABDUL JALAL 60
ABDUL JALAL 61
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 63
ABDUL JALAL 64
ABDUL JALAL 65
ABDUL JALAL 66
ABDUL JALAL 67
ABDUL JALAL 68
ABDUL JALAL 69
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 72
ABDUL JALAL 73
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 74..
ABDUL JALAL 75
ABDUL JALAL 76
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 78
ABDUL JALAL 79
ABDUL JALAL 80
ABDUL JALAL 81
ABDUL JALAL 82
ABDUL JALAL 83
ABDUL JALAL 84
ABDUL JALAL 85
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL 88
ABDUL JALAL (2020) 89
ABDUL JALAL 90
ABDUL JALAL 91
ABDUL JALAL 92
ABDUL JALAL 93
ABDUL JALAL 94
ABDUL JALAL 95
ABDUL JALAL 96
ABDUL JALAL 97
ABDUL JALAL 98
ABDUL JALAL 99
ABDUL JALAL 100
ABDUL JALAL 101
ABDUL JALAL 102
ABDUL JALAL 103
ABDUL JALAL 104
ABDUL JALAL 105
ABDUL JALAL 106
ABDUL JALAL 107
ABDUL JALAL 108
ABDUL JALAL 109
ABDUL JALAL 110
ABDUL JALAL 111
ABDUL JALAL 112
ABDUL JALAL 113
ABDUL JALAL 114
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL
ABDUL JALAL

ABDUL JALAL (2020) 45

374 18 0
بواسطة Ayshercool7724

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

_ABDUL JALAL_

_WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

PAGE- 45
PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.

A har kullum ina jinjina da godiya ga masoya wannan novel nawa, comments dinku da addu oinku ina jin dainsu matuka, ina godiya kwarai dagaske,
Domin sharhi, gyara, kokuma shawara a nemeni ta what's app akan wannan lambar wayar
07063065680
Ina godiya matuka Allah yabar kauna

_My first novel_

Abba ne yasa hannu ya janye Jalila daga hannun Jawwad, yana jijjigata amma idonta a kakkafe, hannu Abba yasa ya rufe idon Jalila babu alamar tana numfashi, Jawwad ya kalli Abba
"Abba wai mekake nufine, ba dai ta mutu ba," shiru Abba yayi bece komai ba, Jawwad yakuma cewa "Abba kayi magana mana," Nana ce ta shigo palourn Abba, "lafiya kuwa Maama inajin hayaniya tundaga palour" hankalinta ya kai kan Jalila dake kwance a jikin Abba, Jawwad kuma, kaman baya hayyacinsa, da sauri takarasa inda suke "Abba meyafarune"
Maama ta kalleta "Ke meye haka ki nutsu mana, mutuwa tayi" zarewa Maama ido Nana tayi, "wallahi karyane" ta cacimo Jalila daga jikin Abba "Yaya Jawwad dagaske Jalila ta mutu, meyasameta, wallahi bata mutuba Abba kajifa ta janyo hannun Abba ta dora a wuyan Jalila, jiyayi alamun jijiyar gurin tana motsawa a hankali, ya kalli Jawwad sannan yace
" tashi maza ka fito da mota, mu tafi Asibiti, da sauri Jawwad ya fita, mintuna kadan ya dawo, ya dauki Jalila kamar gawa yayi waje da ita, kafar Nana bako takalmi tabi bayan Jawwad da gudu, Halima da ba tasan me akeba ganin an wuce da Jalila rai a hannun Allah yasa ta firgice, ga Abba ya fito da sauri shida Maama, Halima ta nufi Maama tana fadin "Na shiga uku meyasami, Jalila ne, Hajiya dan Allah meyasameta?"
"Ke dallah rabu dani, ina ruwanki dame yasameta zakiyi mata maganine, Abba yace" Halima kwantar da hankalinki, suma tayine batajin dadi, amma asibiti zamuje"
Halima a rikice tace "Allah yabata lafiya, dan Allah ku tafi dani Asibitin"
Abba yace "karki damu Halima, kiyi mata Addu a zataji sauki" daga haka yayi waje, itakuwa Maama tasamu guri tai zamanta a palour,
Asibitin doctor salis suka nufa, ba karamin gudu Jawwad yakeba, se kace ze tashi sama, Jalila na kwance akan cinyar Nana, ga sanyin AC amma tana nan yadda take ba wani canji, ko motsi batayi, suna zuwa Asibiti Jawwad ya fita da sauri ya shiga cikin Asibitin ba a dadeba segashi ya taho da doctor salis, Nurses sun turo gado, Abba na tsaye a jikin motar, Jawwad ya karaso ya bude motar ya dakko Jalila, ba wanda zece ba gawa bace, aka dorata akan gadon aka turata, zuwa cikin Asibitin, su Abba suka bi bayansu, suna zuwa kofar emergency suka tsaya, aka shiga da Jalila, su Abba da Nana suka dinga sintiri a kofar emergency tunda aka shiga da Jalila ba wanda ya fito balle su tambayeshi me ake ciki, Nana se kuka take, Abba ya kalleta "Nana kiyi shiru kinji muyi mata addu a zata samu lafiya Insha Allah" Jawwad kam yarasa meyake masa dadi, sam besan mezeyi yaji dadiba, Maama ce ta kira Jawwad "ya akayine naga har yanzu baku dawoba ta mutune"
" A a Maama bamu saniba, sun shiga da ita emergency tunda mukaje ba wanda yace mana komai"
Daga haka ta kashe wayarta, Halima se addu oi take, tana yi wa Jalila adduar samun sauki, sun shafe awanni a gurin nan kafin doctor salis ya fito, yana share Gumi gaba daya suka nufi inda yake
Abba cikin zakuwa yace "Ya ake ciki" ya kalli Abba sannan ya kalli Jawwad
Jawwad yace "Dan Allah kayi magana mana"
Doctor salis ya nisa sannan yace
"ku kwantar da hankalinku, Alhamdilillah mun samu nasarar ceto rayuwarta cikin ikon Allah, Blood pressure dinta yayi high fiye da tunani, wanda yasa tasamu stroke, yanzu Alhamdilillah tana iya numfashi, kuma bugun zuciyarta yazama normal, sedai har yanzu bata farfadoba, zamu ajiyeta a ICU tukuna muga abunda hali zeyi,
Dan murmurshi Nana tayi tareda fadin "Alhamdilillah, Allah yabaki lafiya Jalila"
Doctor salis yace "Abba kubiyoni office akwai magunguna dazan rubuta" Abba yace to shikenan muje, suka bi doctor salis office dinsa, akace Nana ta tsaya a waje, Abba da Jawwad suka shiga, doctor salis ya kalli Abba
"Muna bukatar Jini koda leda dayane zuwa gobe insha Allah , zamu kara mata, mun gwada PCV dinta shima yayi kasa, kaman ta dade tana rashin lafiya, ya akai condition dinta ya zama worst haka lokaci daya,? Jawwad ya gaya masa komai, yayi rubuce2 yabasu magungunan da ake bukata su siyo,
Jawwad yace "doctor zamu samu ganinta kuwa"
Doctor salis yadan girgiza kai "No bazaku iya ganinta yauba gaskiya, zaku iya tafiya, in yaso gobe in Allah ya kaimu seku dawo, daga nan a duba Jinin da za asamata," Abba yace "Kana ganin ba komai in an barta anan"
"Eh Abba ba wani matsala, za a kula da ita Insha Allah, ko wani ya zaunama bata hayyacinta bacci take, ba lallai ta farfado a yauba"
Sukayi sallama da doctor, sukaje suka biya bill dinsu, daga nan suka taho gida, a palour suka tarar da Halima, ta sha kuka, tana ganinsu tafara tambayar Abba, "Ya jikin nata"
"Ki kwantar da hankalinki ta farfado, tana baccine, an kwantar da ita"
"Allah yabata lafiya"
Abba ya amsa da Ameen, dama Nana bata tsaya ba dakinsu ta wuce, jin dakin tayi babu dadi, ta kalli gurin kwanciyar Jalila, da yanzu ta kwanta kokuma tana salla, Hawaye yazubowa Nana, "Allah yabaki lafiya Yar uwa"daga nan taje tayo alwala, tai sallar Isha'i, ko kayan jikinta bata canzaba ta haye kan gado tayi shiru tana tunani, har bacci ya dauketa,
Koda Abba ya shiga part dinsa Maama tayi dai2 akan gado tana baccinta, ko a jikinta, wanda da yartace da bataga tayin bacciba, shigewa yayi yai wanka, yafito ya dakko sallayarsa ya dawo palour dukda ya gaji matuka yau, wuni sukayi yawon neman bayanin inda zasu samu Ummi, ga wannan abu daya samu Jalila,
Bangaren Jawwad ya dakko wayarsa ya kira Jalal amma bata shigaba, dan haka ya tashi yatafi gidansu Jalal, da mamakin Jawwad, Jalala baya nan, yasan baze wuce yana mashaya ba, dan haka ya hakura, ya koma gida ya rama sallolinsa ya kwanta, se dai bacci ya kauracewa idonsa, se tunani

Doctor salis ya koma inda aka kwantar da Jalila, ya dan tsura mata ido, ta rame sosai akan lokacin daya fara ganinta, idonta a rufe ga oxygen da aka samata, a hankali numfashinta yake sauka, sedai bugun zuciyarta ne har yanzu be daidaita ba, kallonta ya cigaba dayi, dukda ta rame amma setayi kyau, goshinta kwance da gashi, ga girarta itama a cike take da bakin gashi, doctor salis y shagala sosai da kallonta, tareda tunani2 daban2 akan Jalila, yaji an taba shi waigowa yayi, yaga Abokin aikinsane, wanda zeyi night, suka gaisa
"Salis har yanzu baka tafi ba? ai nazata katafi tun dazu"
"A a doctor ban tafi ba,"
"Dare yayi sosai fa, yakamata ace ka tafi"
"eh anan zan kwana" doctor Khalid ya kalleshi
"naga kai kayi dutyn yamma"
"Eh, ina da patient ta mussaman" Salis ya nunamasa Jalila
Gyada kai doctor Khalid yayi, yai gaba abunsa
Da sassafe Nana ta tashi ta kintsa, Halima ta dama kunun gyada dan Jalila na matukar sonsa, har Abba ya tashi ya shirya Maama bacci takeyi, suka kintsa suka tafi Asibiti, Jawwad ya kira lambar Jalal har ya gaji amma Jalal be daga ba, yaso yaje ya kuma dubawa ko yadawo, amma da wuri suka fito, dan gari da sauran duhu, dan haka be samu damar komawa yaduba ko Jalal ya dawoba,
Suna zuwa asibiti, Jawwad ya nemo doctor salis, doctor salis yace su kara hakuri har yanzu bata farfado ba, amma za a gwada Jinin Abba kona Jawwad wanda yayi zasu dauka, domin sakawa Jalila, aka duba jinin Jalila da nasu, amma babu wanda yazo daya dana Jalila, cikin damuwa Jawwad yace "to yanzu meye abunyi?"
Doctor Salis yace " A yanzj gaskiya mu a lap dinmu bamu da irin Jinin ta, sedai inmaka kwatancen Asibiti wani abokina kaje can, in akwai kace nina turoka sesu baka,"
Abba yace "to hakan yayi kyau," doctor salis ya dakko wani takadda yayi rubutu, yabawa Jawwad, Abba yace "

salis, baze yiwu muganta ba ne?"
Doctor yace "Abba ka kara hakuri tana, karkashin kulawa ta mussaman bazaka samu ganinta ba amma insha Allah zuwa anjima in akasamata Jinin zamu fito da ita"
Abba yace "to shikenan, Jawwad muje ka ajiyeni, zan yi wani abunne, kai seka wuce ka karbo jinin, insha Allah anjima kadan zan dawo"
Suka tashi suka fito, Jawwad yace Nana tazo su tafi tare ba yanzu za a fito da Jalila ba,
Maama ta tashi, ta duba bataga Abba ba, taji gidan tsit, ta fito palour taga halima tana aiki, "Ke halima Abban Jawwad ya fitane"
Halima ta dan risina
"Eh hajiya sun fita gaba dayansu, sun tafi asibiti"
Wani dogon tsaki Maama tayi, ta koma dakinta
Halima tabi bayanta da kallon mamaki, tacigaba da aikinta,
Karfe tara Jalal yai parking motarsa a kofar gidansu Jawwad ko daga ina yake oho, da sauri ya nufi part din Jawwad, amma yaje ya tarar Jawwad baya nan, gashi kuma wayarsa ba caji balle ya kirashi, yana fitowa yaga halima tana gyaran harabar gidan
"ina Jawwad ya tafi" ya tambayeta, cikin isa
"Suna Asibiti an kwantar da Jalila"
Kallonta yayi sannan yace "me yasameta"
"Nima bansaniba amma a asibiti ta kwana"
Daga haka yafita waje ya hau motarsa, ya nufi asibitin, dan yasan asibitin dasu Jawwad ke zuwa, yana zuwa ya tafi office din doctor salis, Jalal yayi sa a, doctor salis yana nan be tafiba,
Ya mika masa hannu suka gaisa, Jalal ya kalli doctor salis
"Wani patient su Jawwad suka kawo?"
"haba kacemin baka saniba? Kanwarku ce fa, wadda Jawwad ya hanani ce Baby"
"me yasameta?"
Jalal ya kuma tambayar sa
Doctor salis ya gyara zama, ya zayyanewa Jalal rashin lafiyar ta ta, Jalal yace "Yanzu ina Jawwad din yake"?
"eh sun tafi neman jinin da za a saka mata, daana Abba dana Jawwad duk beyiba, nima nawa baze mataba dana wa zansaka mata," Jalal ya kalleshi ya dan tabe baki, sannan yace "Meye blood group dinta? "
"Meyasa kake tambaya"
Hade rai Jalal yayi,
"Meye kuma na tambayata, kaima kasani patient din Jawwad nawane"
Doctor salis yace "Allah yabaka hakuri, O+ ne"
Jalal yace "irin nawane, a dibi nawa akai lap, inba matsala a saka mata" doctor salis yace "to shikenan muje lap din"
Sukaje aka duba, jinin Jalal, irin natane, kuma anyi gwaje2 amma jininsa lafiya kalau,
Kafin a dibi Jinin ya kalli salis yace "Wannan sirrine tsakanina da kai, ko Jawwad bana son yasan nina bada jinin, dukda nayine saboda Allah, kuma saboda Jawwad, amma bana son yasani, kace masa kawai wanine yazo yabada jininsa sadaka"
"To shikenan, bazan gaya masa ba Insha Allah, yanzu ka zauna se su diba"
Jalal ya zauna aka dibi jininsa, suna gamawa ya mike, aikuwa jiri ya debeshi, yakusa faduwa, lap attendants dinne suka rirrike shi, aka maidashi ya zauna wani ya tambayeshi
"Kaci Abinci kuwa?"
Jalal ya girgiza kai, dan rabonsa da Abinci tun jiya da safe, youghurt akasamo aka bashi ya dan yasha, ya dan huta sannan ya mike, shi yanzu so yake ya tafi, bayason Jawwad yazo ya tarar dashi anan, Doctor salis se sannu yake jerawa Jalal, Jalal ya kalleshi "Muje ka kaini inganta"
Doctor salis yace "A a Jalal tana karkashin kulawa ta musamman, baze yuwu ka gantaba"
"kamar yaya, ganinta zanyi nace ba wani abuba" Jalal ya fada a tsawace, ba shiri salis yayi masa Jagora zuwa inda Jalila take,
Jalal ya dan tsorata da ganinta, ta rame sosai, ga oxygen a hancinta, gefe kuma ga drip, a hankali numfashinta yake fita, dan girgiza kai Jalal yayi, yai waje dan ko sallama beyiwa Salis ba yayi waje abunsa, motarsa ya nufa ya hau ya tafi gida,
Jawwad suka dawo Asibiti shida Nana, sun samo Jinin amma doctor yasanar dasu an samu Jinin, wani yabada nasa sadaka, kuma yayi dai2 dana Jalila an samata, Cikin damuwa Nana tace "wai har yanzu bata tashiba?"
Doctor Salis yace, "kiyi hakuri zata tashi ne, ana samata jininne, Insha Allah, zuwa magariba zaku iya ganinta"
Ajiyar zuciya Jawwad yayi yace "to shikenan, magungunan ban samosu duka ba, sedai in nafita inkuma dubawa"
Doctor yace ba matsala, daga nan su Nana suka tafi gida,
Jalal kam kwanciya yayi, ya kama bacci, dan ya gaji matuka, dukda yunwar da yakeji, gajiya ta hanashi neman Abinci, baccinsa yake sosai, Jawwad ya shigo yaje part dinsa ya tarar Jalal na bacci, se yazata ko giyar ya sha, ya nemi guri a dakin Jalal yayi sallar azahar.
Nana koda ta koma gida, batabi takan Maama ba ta shige tayi wanka tai sallar azahar, sannan ta nufi kitchen, ta dakko Abinci, tana zuwa palour ta tarar da Maama zata fita unguwa, Nana ta kalleta "Maama fita zakiyine?"
"Eh zanje kasuwane zan karbo kaya,"
"Adawo lafiya"
Daga nan Maama bata kuma cewa komai ba balle ta tambayi yame jiki, ita kanta Nana abun setaji ba dadi, taga Sam Maama bata kyauta ba, haka ta wuce ta zauna ta fara cin Abincinta a palour, Halima ta fito daga dakinta tace "Nana ya jikin Jalila kuwa" Nana tace mata da sauki, daga nan tacigaba da abunda take.
Jawwad yana nan yana zaune, har Jalal ya tashi daga bacci, becemasa komaiba shima be kulashiba, ya shiga toilet yai wanka, sannan ya zo ya zauna ya kalli Jawwad
"ya akayine ina ka tafi, da sassafe?"
Jawwad yace "kai zan tambaya ina ka tafi, tun jiya ban ganka ba, wayarka kuma bata shiga"
Jalal ya gyara zama "mmmm to na danje wani gurine,?"
"wani gurine, bashi da suna"
"Eh bashi da shi" Jalal ya bashi amsa,
Jawwad yace "Shikenan"
Jalal yace "Kai yunwa nakeji, zomuje inci Abinci, ban karyaba, ga rana tayi banci abincin rana ba, nasan gidanku an gama Abinci"
Jawwad ya kelleshi
"Can inda kaje basu baka abincin ba"
"Eh basu banba, dan Allah ka tashi inajin yunwa sosai fa"
"Me dafawar an kwantar da ita a asibiti"
"Wa kenan?" Jalal ya tambayeshi kaman besan meyafaruba
"Baby mana an kwantar da ita a asibiti, a can ta kwana"
"Allah ya sawwake, ya labarin Ummi fa?"
Jawwad yai ajiyar zuciya, "shine dalilin dayasa ta kwanta a asibiti, Abba aka kira, aka gaya masa wanine ya bige Ummi, kuna ya dauketa ya tafi da ita, tunda taji haka ta fadi, mu mundauka ma ta mutu a jiyan nan"
Jalal ya gyara zama, ya dakko sigarinsa ya kunna, ya busa hayakin sannan yace "waye ya kira Abban yagaya masa?"
"nima bansaniba ina tunanin, ko daga tashane da yabada lambarsa yace in ansamu bayani a kirashi"
Jalal yace "Hmmm" yacigaba da shan sigarinsa, Jawwad ya kalleshi
"anjima kadan zan koma semuje tare ka ganta,"
"inga wa?"
"ka duba Jalila mana,"
"da kyar ne, inje ai nace Allah ya sawwake"
"haka zakace?" Jawwad ya tambayeshi
"yeah" yafada tareda busa hayakinsa sama Jawwad yaji haushi, dan Jalal ko a jikinsa, ya mike ya fice ya barwa Jalal dakin, yana fita Jalal yai murmushi
Jawwad kenan dan uwana na kaina,
Jawwad yakoma gida, yasamu abinci yaci, ya tambayi Nana wai ina Maama, ta gaya masa ai ta fita kasuwa, abun yabatawa Jawwad rai amma yai shiru bece komai ba.
Seda akayi sallar magariba sannan Maama ta dawo, lokacin Abba ma yadawo, yakuma bibiyar report din daya kai gurin yansanda, ko ansamu wani labari akan wanda ya bige Ummi, amma wunin ranar yagama yawonsa ba wani labari,
Maama salla tayi kawai, taje ta dauki Abincin Abba ta kaimasa part dinsa, taje ta ajiye masa, amma bece mata komai ta kalleshi
"Abban Jawwad ka dawo bana nan ko? Wallahi fita ce ta kamani"
A fusace Abba ya dago "dole fita ta kamaki Zainab, tunda ba yarki ce a kwance a Asibiti ba, yarinyar nan tun jiya an kwantar da ita a Asibiti, babu tabbacin zata farka daga suman da tayi, amma koda wasa baki taka kafa inda take ba, ina sane da duk abunda kikeyi, ni bazanci amana ba, dan uwana ya nunamin soyayya, bazan iya wulakanta masa yaba, amma kema kin haifa, Wallhi zainab akan Jalila zan iya rabuwa da kowaye, bakeba har yayan cikina, ita nake kallo inji dadi, Aliyu baya raye amma har yanzu Alkhairinsa muke mora, kije kiyi harkarki inyi tawa, ko kije ko karkije dubata hakan baze sauya komai ba, ki dauke Abincin ki, ki fita karki kara zuwa inda nake!!! "
Jawwad yai sallar isha i ya koma Asibiti yasamu, doctor salis yana tambayarsa ya jikin Jalila, ya gayamasa sunfito da ita, an bata daki, yagaya masa lambar dakin yana zuwa dakin da mamakinsa yaga Jalal a zaune, a can gefe yana shan sigarinsa, gefe kuma ga Jalila a kan gado ana samata ruwa, tana kwance.
Jalal ya kalleshi yai murmushi
"Sarkin fushi, ya akai na rigaka, zuwa"

Share please
More Comments More Typing...............................................

واصل القراءة

ستعجبك أيضاً

85.9K 2.2K 32
A little AU where Lucifer and Alastor secretly loves eachother and doesn't tell anyone about it, and also Alastor has a secret identity no one else k...
81.8K 5K 58
Dr.TAHEER labari ne mai cikeda soyayya mai tsuma zuciya...labarin wani matashin likita daya kamu da matsananciyar soyayyar yarinyar da ya raineta a h...
1.2M 37.1K 100
Matar shi ce ta farko bata san haihuwa, idan ta samu ciki sai ta zubar, as ending yake yin auren sirri da mai aikin gidan