P90

137 14 10
                                    

💕 *BINTEE*💕
        *( 'Yata ce)*

*Wattpad@*
_Serlmerh-md_

🅿️ *...90*

               ......Kuka sosai na sanya daga cikin 'dakin Inna ta..harga Allah ni banaso kowa ya rabani da ita, yini 'daya tak da nayi da yarinyar sai naji ta 'kara shiga raina sosai.

Bansan ya 'karshen tattaunawar tasu ta 'kare ba saboda kukan da nake yi.
Hamma na nagani tsaye daga bakin 'kofa yana fa'din" Tashi mu wuce gida kafin gobe a maida ta inda yafi dacewa da ita".

Simi- simi na tashi na nufo 'kofar batare da na 'dauki yarinyar ba, sai yace" 'dauko ta mana..ai bazaki barwa Inna wahalar ta ba tunda ke ce kika jaji6o ta".

Ni dama hakan yafi min har a zucia ta, nafi so in tafi da itan..hakan yasa naji dadin kalamin sa wani sanyi ya ratsa zucia ta.

'Dauko ta nayi na rungume ta cikin hijabi na kamar 'dazun na bishi abaya har muka je gida.

Yau kam kowa na gida Baffah ma tuni ya dawo saboda tashin hankalin da ake ciki..ga Goni ma da ya auna sa'a duk bani da labari sai yanzu da na dawo gidan.

Garin nemana da kadan ya rage a harbe sa badan suna tare da Yah Bukar da yy saurin ankarar da shi suka zube 'kasa hakan yasa harbin yabi iska ya wuce, basu mike ba kuwa har sai da 'yan ta'addan suka karasa wucewa.

Kaina 'akasa dama na shiga gidan a bayan Hamma Bukar shi da Salele...a hanya naji suke tattauna batun su biyu.

Tsoro ya sake kamani, sbd jin auna sa'ar da 'yan uwana suka suka yi..yau da ace an harbi dayan su ta dalili na da bansan inda zan tsoma rayuwa ta, banda ma Iyami da sai ta kusan yin dambu da namana.

Gefen tabarmar Abban mu suka zauna inda ya tashi daga kihsingidan da yayi yace" Aww Bukar ka samo ta ne?"

Sam banyi mamaki ba, dan na jima da fahimtar irin mahaifin da Allah ya bani, yafa san bana gidan tun safe amma amadadin a fita da shi a duba ni sai ma zama da yyi a gida ya mi'ke 'kafafu ko alamr damuwa babu tattare da shi, na dawo ko kar na dawo ruwa na, in mutu ko in dawo a raye duk ba damuwar sa bace.

Hamma Bukar ka'dai ya damu dani a gidan na kuma shika'dai ne ya damu da rashin ganin nawa sai Goni da shima isowar sa kenan da safiyar ranar.

Shima din na tabbata da bai dade da dawowa bane da ko kallo ban ishe shi ba, shi dama haka yake, babu ruwan sa da duk wata sabgar da ya san bazata kare shi ba, baya shiga sabgar kowa balle kace ga abinda yayi maka na 6acin rai..'kyaliya ce da shi na masifa.

Ban yi mamakin jin furucin mahaifi na ba sai lokacin da Iyami ta fito daga 'dakin ta tana 'ko'karin 'daura zani naga ta bini da wani mugun kallo..." Ashe zaki dawo na 'dauka ai gawar ki za'a kawo min tunda ke hankali bai gama isan ki ba har yanzun, kina ji gari bb lafiya amma dan iya shege bazaki dawo gida ba sai kin bawa mutane wahala...?"
Ta 'karashe da yanayi na tambaya.
" Wato gawa ta?..to gani ai na dawo da 'kafafu na".
Abinda na fa'di cikin zuciya ta kenan..a zahiri kuma gyara ri'kon yarinyar hannu na kawai nayi.
" Wlh da kin kuskura sanadin ki lafiyar 'ya'ya na ya samu gi6i da sai kin sha mamakin abinda zan aikata agare ki...a ina kk tsaya tun safiyar da baki dawo gida ba....?"
Shiru nayi na ma rasa amsar bata...
" Da kika yi shiru kina jin mutane 'din kuma fa, ba dake ake magana ba ne...banza munafu....".
Maganar Iyami tsayawa daidai yy lokacin da taga na gyara ri'kon yarinyar hannu na akaro na biyu.

Baki ta bu'de tana bina da kallo sai a sannan ta lura da yanayi na, a hankali cike da mamaki tace" Zaituna"!.

" Na'am Iyami..."
Na amsa ta cikin sanyi nima batare da na dubi fuskar ta ba.

" Me nake gani haka wai?..menene a hannun ki...?"

Kafin nayi magana..Hamma Bukar ya riga ni da fa'din" Ki 'karaso ki zauna mana Iyami dama maganar da zamuyi kenan..."

BINTEEE ( 'Yata ce)Where stories live. Discover now