Page 8

4.1K 238 2
                                    

🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨
🚨🚨
🚨






💎💎💎💎💎💎💎💎
*ZAN SOKA A HAKA*
💎💎💎💎💎💎💎💎
*NA*
_BILKISU ALIYU KANKIA_
*((QUEEN BK))*






🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITTER'S.*
(( _Gidan zaman lafiya da amana insha Allah_ 🤜🤛))



THIS PAGE IS YOUR'S, MY NAME SAKE, MY NICK-NAME SAKE, MY TOWN SAKE, MY...MY .....Lol😁
*BILKISU Z YA'U*
🅱K
my takwara ina yin ki sosai, Allah k'ara basira, da zak'in hannu, autar marubuta☺



Page0⃣8⃣



Haka rayuwa taja, cikin sati d'aya, duk abun da ma'u keyi, ba wanda ya canja illa wanda ya k'aru, duk ta k'ara lalacewa, ta rame, yanxu ko islamiya bata zuwa, saboda gwggo ta hana ta, don taga ta haddace, a cewar ta, me kuma zata koma tayi, in ban da gulma, ma'u ko bata damu sosai ba, saboda baffa yana mata k'arin sauran litittafan, yanxu gwoggo ta linka mata yawan furar da take sayar wa, yanxu hadda man shanu, dana kad'e, gashi in ta futa tun safe, sai ta saido take komo wa, ga kiwo, duk abu sha tara da ashirin sun had'e mata.

Ga shi baffah yayi tafiya, tun satin daya wuce, kuma bai dawo ba, inda ma take d'an samun sake, gwggo na gama kokon saeda warta, take fita ita da aminiyar ta, baba iyah, yawan gulmace2. Bangaren jauro ko, yana ta samun sauk'in raunukan shi, dan ma'u da lamunde da kansu suka amso, mashi magani wajen ta - sallah.

Wata irin k'ara ta ke ji, wanda duk me yin ta, yana cikin damuwa sosai, kuma yana da buk'atar taimako gaggawa, sae dai abun da ya d'aure mata kai, muryar da take k'arar ta santa, ba kuma k'aramin sani ba, tunda yawanci ita ce ta ke ji a mafarkinta, d'an mutumin ta ne, da ta saba ji a mafarkinta, duk da bata, tab'a ganin fuskar shi ba, amman ta rik'e muryar shi sak, a kid'ime ta fara bin, inda taji k'arar tafi yawa, kasancewar duhu ne, da lalube take tafiya, hannun ta, taji ya tab'a mata wani abu, da alama marfin k'ofa ne, ta manna kunnen ta, taji tabbas ta nan ne k'arar ke fitowa, cikin fargaba, ta d'an tura k'ofar kad'an, take k'ofar ta wangale gaba d'aya, ta na sakin wata, y'ar k'ara, ba abun da take iya gani, tsabar duhun, ba kuma abun da ta ke iya ji, illah wannan kururuwar, da shashek'a, sae kuma abun da yafi d'aure mata kai, k'arar ruwa kawai takeji, yada kasan ana tilla ma ruwan manya2 duwatsu, fancal2 kawai take ji, cikin rashin kwarin gwiwa, ta fara taka k'afar ta, ahankali cikin bud'add'iyar kofar, ba abun da take ji sae k'asa mai damshi, alamun akwai ruwa gaba, tana isa bakin gab'a, idonta ya hango mata alamun mutum, yana sanye da fararen kaya, ruwan na tasan ya janye shi, shi kuma yana dago hannu, yana karkada su, alamun ya na neman taimako, ta waiga, ko ina taga taya za ta taimaki wannan bawan Allah, amman bata ga kowa ba, kuma bata ga komai ba, gashi har yanxu bata dena jin wannan k'arar ba, dan haka kawai ta yanke hukuncin ta shiga ta jawo shi, tunda ta iya iyo, dan haka ta tattare zanin ta, tae tsalle dan ta fad'a cikin ruwan.

A firgice ma'u ta tashi, ta tsorata sosai da mafarkin nan da tayi, duba da yadda ta jik'e da zufa sharkaf, ba abun da ta keyi sai salati, bata tab'a yin mafarki, taji shi kamar a zahiri ba irin wannan, kuma har yanxu a cikin kunnan ta tana jin k'arar, haka tai ta addu'a, da kyar ta samu ta tattaro natsuwar ta, ta tashi taje ta d'oro alwalla, ta fara jera nafil fili, ganin ba a kira sallar asuba.

tunda tayi wannan mafarki, kwanakin tana yawan samun fargaba, ta rasa dalili, ita dae da taji addu'a kawai take, sae ta d'anji hankalin ta ya kwanta.

Yau tunda wuri, gwggo ta fita yawan yamad'id'inta, don haka ta samu ta d'an sake, kuma gashi yau ba futa talla, tunda fura ta k'are, kuma gwggo bata siyo gero ba, dan haka da wuri ta gama, duk abun da ta saba, ta tafi garke tatsar nono, ta dawo tana burkawa, kawai taji kamar hayaniya a bakin gida, da sauri ta futa, dan hankalin ta, dama ba'a kwance yake ba, abunda ta gani ya matuk'ar tayar mata da hankali.

Baffan ta ne, aka d'auko ranga2, yanayin da ta ganshi kamar ba lumfashi, a jikin shi, ta lura da k'afar shi ta dama, da akayi wa tsatsauran k'ulli, wata rikitacciyar k'ara ta saki, tare da fad'uwa k'asa, cikin kuka, take tambayar mutanen me ya faru da baffan nata, ganin ba wanda ya kula ta, sae ta cigaba da kuka, tana kiran Allah, don shi kad'ai zata kira, ya amsa ta, koda yaushe, wani dattijo ne, ganin kukan nata yayi yawa, shi ya amsa ta, da cewa tayi hak'uri ta daina kuka, ba mutuwa yayi ba, sannan hankalinta ya d'an hau saiti, su kuma sunyi nasarar, kwantar da shi, kan d'an gadan karar dake tsakar gidan, ma'u ko matswa tayi kusa dashi, dan taga zahirin cewa da gaske bai mutu ba, ta kama hanayen shi, sae lokacin ya b'ude ido, a take takaraya, ganin kwayar idon shi, daga gani kasan yana jin jiki, tace,

" Me ya sameka baffa na."

Mai gari ne yace, " kira hanne sae in muku jawabi."

A sanyaye ma'u tace, " bata nan, ta fita."
Mai gari sanin hali, karkad'a kai kawai yayi, yace, " kar ki damu ba wani abu bane, maciji ne ya sare shi, ma'u jin an ambaci maciji, take cikin ta ya hautsine, gashi tana jin yana wani cewa ba wani abu bane, macijin ne ba wani abu ba,😏
ya cigaba, matsalar da aka samu, shine ba'asan kallar macijin ba, don haka za'a sha wahala wajen magance matsalar, to kuma shima yace bai iya tantace kalar macijin, dan ba'a lure yake ba, kuma bai ga macijin ba, sae bayan ya sare shi, kuma shima bindin shi kawai ya gani, kasancewar dafin nashi na da zafi,
Audu fatalke ne, ya gan shi a dajin y'ar bushiya, shine ya kawo shi gida na bayan ya d'aure mashi wajen.

Amman na aika gidan ta-sallah, cewa a had'o magani, me k'arfi, na dafin maciji, dan da alama dafin na shi mai k'arfi ne, duba da yadda Mal. Wali, ya kumbura sosai, musamman ma k'afar shi, ga yadda idon shi yayi, ga kuma bakin shi yayi bak'i, bai ida rufe baki ba, lamunde ta shigo da sallamar ta, ta kawo maganin da kakar ta aiko, ta bayanin yadda za'a bashi, sannan ta koma kusa da k'awarta dake ta rabxa kuka, tana bata baki, duk da ita ma ta fara kukan,
sae da suka bashi maganin, sannan duk suka tafi, bayan sun mai fatan samun lafiya, itama lamunde, tafiya tayi tare da cewa zata xo gobe, dan magaruba ta k'arato.

Sai bayan magaruba gwggo ta dawo, tayi mamakin ganin halin da ya ke ciki, tunda ma'u ta bata labarin komai, amman ba ta wani razana ba, ba abun da tace illah, Allah k'ara sauk'i, shiko baffa na ta kanshi, bai ma san tana yi ba.

Sati d'aya kenan baffa na jinya, duk ana amfani da magunguna yadda suka dace, amman ba wan sauk'i da ke samuwa.
Jikin shi duk ya tsotse, ya bushe, yau tunda ya tashi ya ke fama da wani tari, magana ma da kyar ya keyi, gashi gwggo ma ba ta nan wai ta tafi rugar su biki, dama tunda ya fara ciwon, ma'u ke jinyar shi.

Ta iso gabanshi, tace, " baffa ga maganin tarin na amso maka, kasha ko kaji sauk'in tarin."
T tallabo shi, ta bashi, sannan ya koma ya kwanta, itako gefe ta koma ta zauna tana mai sannu, tana tofa mai addu'a.

Da hannu ya yafito ta, ya ma ta nuni da kusa da shi, tagane nufin shi dan haka ta dawo, ta zauna, inda yake nunawan.

Cikin sark'ewar muraya yace, " AS- MA- U, itako jin ya ambace ta da wannan sunan, tasan akwai wata mahimmiyar magana a bakin shi, dan ba kasa fai ya ke kiran ta da sunan ba, dan haka ta tattara mashi hankalin ta, da natsuwarta gaba d'aya.

Ya cigaba, da fad'in Asma'u ki saurareni da kyau, inaso yau in fad'a maki, abunda baki sani ba, ko ince labarin rayuwar ki, nasan yanxu kinyi hankalin adana duk wani batu, da zan fad'a maki a cikin zuciyar ki, ina son in fad'a maki ne dan in fita hakk'i, don ni tawa ta k'are, ba ni tunanin xan tashi a wannan ciwon, tuni ma'u ta fashe da kuka tana ya bar fad'in haka ciwo ai ba mutuwa bane, ya cigaba cikin sark'ewar murya.....




A/N

MEYE ASALIN MA'U❓

MEYE DALILIN MAFARKINTA❓

WAYE D'AN MUTUNINTA DA SUKA SABA, AMMAN TA MAFARKI❓

WELL AMSOSHINKU KU BIYO, Y'AR MUTAN KATSINA KUSHA LABARI
LOL😁😁


QUR'AN ((3:157))
PUT YOUR TRUST IN ALLAH, HE LOVES WHO PUT THEIR TRUST IN HIM.



👸🏼 *QUEEN BK* 👸🏼

ZAN SOKA A HAKAWhere stories live. Discover now