page 62

4.3K 273 12
                                    

🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨
🚨🚨
🚨









💎💎💎💎💎💎💎💎
*ZAN SOKA A HAKA*
💎💎💎💎💎💎💎💎
*_NA_*
*BILKISU ALIYU KANKIA
👸🏼 *_QUEEN BK_* 👸🏼










🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITTER'S* 📝
((Gidan   zaman  lafiya  da amana    insha    Allah🤜🏻🤛🏻))

















Page 62









Can ma cikin gida ba labarin dake zagayawa bayada na Asmah da Abdallan kowa kuwa ba ƙaramin mamaki da al'ajabi abun yake bashi ba, haka taron ya sheda jama'a wanda ya haɗa da waenda suka zo taya murna da ƴan gulma da tsegumi da masu yamaɗiɗi da magana cikin gari, anci an sha kalar wacce rai ke so, Mai martaba da kansa yayi addu'a sosai bayan saukar ƙur'ani da akai, haka aka rinƙa kwantar da shanaye da raguna nama kam sai kaci ka tafi dashi, Asmah kam ranar taga dangi kamar zasu fashe dan har mutan Katsina ƴan uwan mahaifinta haka suma sukayo taron dangi dan zuwa ganin ƴa da kuma ƴar uwartasu wacce take ɗiya ɗaya tilo gun Muhammad itako a ranar bata san adadin kyautar data samu ba, haka taro ya watse cikin farin ciki da kewar juna tsakanin ƴan uwan kowa sai sam barka yake.






Bayan kwana uku gidan shiru kamar ba shi bane a ciki da mutane cundum ba, dan duk an watse hatta su Aunty Urwa duk an tafi su Ammie ne kawai suka rage dan su Auntyn yara ma da suka zo tare da Abbah tuni sun juya, Su Yabi kam da Aunty Nafi basu daɗe da juyawa bama dan kwanansu huɗu alheri kam ba kallar wanda basu sha ba da kuma zasu tafi goma sha tara ta arziƙi su Naty da Mai martaba suka ƙara haɗa masu haka suka tafi suna santi da sam barka, cikin kwanakin nan kuwa Asmah kwata kwata taƙi yadda su haɗa hanya da Abdallah dan da ta ganshi zille mashi take dan tasan tas zai kunyata ta a bainar nasi, duk kuwa da lura da tai dashi kan yana matuƙar son ya ganta amman sam bata bashi dama ba kullum ko da dare yayi zata shige cikin ƴan uwa ta shaƙi baccinta ashe bata san hakannan da tayi ba ƙaramin cima Abdallah tuwo yake a ƙwarya ba wannan kenan.






Washegari da sassafe su Ammie suka wuce Kano ya rage daga Abdallah sai Asmah sai ko mutan gida, ranar Abdallah wuni yayi a sashen Naty amman sam bai kula Asmah ba ko kaɗan dan shi ya ɗau fushin abunda tai masa ɓangaren Asmah kam abun har tsoro ya fara bata dan da fari tasha wasa yake mata amman ganin yayi kicin kicin da rai ya shareta dan ko magana tayi baya amsa mata kuma Ummah a lure take dasu tun safiyar yau ɗin.





Misalin ƙarfe 8:20 Asmah ce zaune kan sallaya tana lazumi bayan tagama sallar isha'i ta kuma bi da nafilfilin data saba bayan ta shafa addu'ane ta taso cikin murmushi tana duban Ummanta dake ta gyara masu kayan cikin akwatinsu a wardrove ɗinta dan gefe ɗaya ta ware masu ƙarasowa tayi wajenta tana faɗin "sannu Ummata amman ba nace ki bari zanyi aikin ba bana so inga kina wahala Ummah ki bari na ida dan Allah" ta faɗa tana karɓe kayan dake hannun Ummah.



"A'a ɗiyata ki barshi bani nace na hutar dake ba, oya no more words jeki falo ki fara cin abunci gani nan isowa" ta faɗa tana maida abunda Asmah ta karba hannunta, da sauri Asmah ta riƙe mata hannu sai da ta  marairaice kana tace,



"Ummah dan Allah ki barni nayi albarkarki nake son insamu" shafa mata kumatu tayi tare da faɗin,

"Yauwa ƴar kirki Allah ya maki albarka i maza ki gama ni bari na gyara wannan jibgin kayan da aka babbaku" ta faɗa tana komawa side ɗin ɗakin da aka tara alherun da Asmah da Abdallan suka sassamu ɗin, Naty ce ta shigo ɗakin tare suka gyara kayan da Ummah duk wasu envelop na kuɗi suka ware su guri guda dangin su kaya ma haka suka kimtsa su cikin wani jibgegen akwati sai sauran ƙwarerayi, nono, manja da man gyaɗa da suka rage suka ajesu store kamin su Asmah su tashi tafiya duk kuwa da mafi yawan kayan sun jibga ma Ammie ta wuce dasu, bayan sun kammala ne suka isa falo nan suka iske har baba gaje (babbar kuyanagar Naty) ta jera masu dinner ɗinsu, Naty ta jawo ƙwaryar fura zata fara damu dan ita ta bada izinin kar ariƙa dama mata fura ta fi son ta dama da kanta, da sauri Asmah ta karɓe tana faɗin ta barta zatayi, Naty tai murmushi tana faɗin "oh ni wannan kishiyar tawa bata so taga ina motsa jikina anya kuwa ko dai zagon ƙasa kikai mun bansani ba kin ƙwace fada kin banni da ɓara ayaba?"duka suka sa dariya Asmah tace,



ZAN SOKA A HAKAWo Geschichten leben. Entdecke jetzt