ZAN SOKA A HAKA

נכתב על ידי queenbk2020

392K 23.9K 2.2K

#5 tausayi June 2020. #3 tausayi 20 June 2020. #1 munafurci #8 hausa novel. #2 tear drop june 2021. עוד

page 1
Page 2
page 3
page 4
page 5
Page 6
page 7
Page 8
Page 9
page 10
page 11
page 12
page 13
page 1⃣4⃣
page 15
page 16
page 17
page 18
page 19
page 20
page 21
pahe 22
page 23
page 24
page 25
page 26
page 27
page 28
page 29
page 30
page 31
page 32
page 33
Page 34
page 35
page 36
AUTHOR'S NOTE
page 37
page 38
page 39
page 40
page 41
page 42
page 43
page 44
page 45
page 46
page 47
page 48
page 49
page 50
page 51
page 52
page 53
page 54
page 56
page 57
page 58
page 59
page 60
page 61
page 62
page 63
page 64
page 65
page 66
page 67
page 68
page 69
page 70
page 71
Page 72
page 73
page 74
Page 75
Page 76
page 78
page 79
page 80
page 81
page 82
page 83
page 84
page 85
page 86
page 87
page 88
page 89
page 90
The end and thanks.

page 55

4.8K 292 61
נכתב על ידי queenbk2020

🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨
🚨🚨
🚨






💎💎💎💎💎💎💎💎
*ZAN SOKA A HAKA*
💎💎💎💎💎💎💎💎
NA
*BILKISU ALIYU KANKIA
👸🏼 *QUEEN BK* 👸🏼









🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITTER'S* *((Z.A.W))*🖊
(Gidan zaman lafiya da Amana insha Allah🤜🤛 )





















Page5⃣5⃣





A kwana a tashi ba wuya wajen Allah yanzu wata ɗaya kenan da auren Abdallah da Asmah, kullum ƙara shaƙuwa suke da son juna, Ammie da Abbah kam ba ƙaramin ji suke da ɗan da sirikar tasu ba, su Auntyn yara kuwa an warke garas, yanzu yadda take jinta da dawo da lafiyarta zata cigaba da muguntarta dan da ciwo ya sata saduda.





🦚 🦚 🦚
Asmah ce ta tashi daga bacci tana salati gaɓa ɗaya jikinta ya jiƙe sharkaf da zufa sai data maida lumfashi sosai sannan ta dawo hayyacinta zare jikinta tayi daga Abdallah ta miƙe tana ta tunanin me yasa wannan ƴen kwanakin take yawan mafarkin Ummanta, toilet ta faɗa ta ɗauro alwalla tazo ta shiga sallah tana kai kukanta a wajen ubangiji, ta daɗe tana addu'a ta roƙi Allah akan ya taimaka mata a kasuwancin da ta fara sannan ta roƙar ma Abdallah sauƙi ta roƙi Allah akan yasa ta gana da Ummanta in tana raye, sannan ta roƙi Allah akan ya katange ta da sharrin Auntyn yara da duk wani mai son cutar dasu, kiran sallah taji an fara can Abdallah ya fara motsawa dan yanzu zama da Asmah ya saba kwata kwata bai bari sallah ta wuce shi kuma har ta asuba ya saba tashi wata rana ma shi ke tada Asmar barin ma ranar da ya tara mata gajiya da yawa, yanzu ana samun sauƙin shi sosai dan har ƙur'ani yana zama Asmah ta koya mai, dan dama tuni Asmah ta daina bashi maganin da Auntyn yara ke bata, ko da har yanzu bata daina kawo mata ba tare da mata kashedi akan ta tabbatar tana bashi ita ko Asmah bata nuna mata komai a gabanta zata nuna tana ba Abdallah sosai kuma tai ta mata godiya akan taimakon shi da take, amman Auntyn yara na fita Asmah zata tiltilar da su a sink tana faɗin "haba Auntyn yara Ma'un da kika sani ba ita bace Asmar yanzu ba, Asmah wayayya ce me ja da ita kuma sai ya shirya dan ita da Allah kawai ta dogara" ta faɗa tana dariya tana ƙara gode ma Allah akan asirin Auntyn yara da ta sani.




A hankali ya fara tattaɓa gadon kusa dashi bai jiyo Asmah ba da sauri ya tashi yana buɗe ido yana mursuƙa su can ya hango Asmah dake zaune saman abun sallah wadda idonta ke kanshi tun fara motsawar shi take kallonshi, murmushi yayi yace "beauty ashe wayau kika mun ko?".

Itama murmushin ta saki tace "wane wayau na maka?".

"Gayanan kin tashi kina ta sallah ni baki tada ni ba saboda baki so na samu lada ko".

"Haba babyna ya zaka ce haka wallahi na fi kowa son ka samu lada, kayi haƙuri babyna kaji zanna ta daka yanzu insha Allah".

"Beauty kin dai mun addu'a ko?".

"Sosai baby addu'ar ka tafi dukkan addu'oin da nayi yawa".

"Kenan kin fi sona ko".

"Sosai baby nafi sanka, ina sonka fiye da kaina".

"Uhmm ai ni ban ma son kaina nafi sonki fiye da komai hadda wayata fa".

Dariya tai ganin yace yafi sonta akan wayar shi tasan yadda yake ba wayar shi mahimmanci sosai ko bai faɗa bama tasan yadda yake sonta kawai dai bai iya expressing kanshi ne, karkaɗa kai tayi tace "wayyo babyna ina sonka sosai har abada".


Kulle idonshi yayi yana kaɗa hannu yana faɗin "Beauty ina sonki ina sonki ina sonki ina s......" ƙarasowa tayi tare da toshe mashi baki da hannunta dan tasan ba shiru zai ba in ba ita ta tsaida shi ba cewa tai "ya isa haka baby nasani to bari faɗi kaji?" sai da ya ɗaga mata kai sannan ta sakar mashi baki matsawa yayi yana cewa "beauty ina sonki sau malalin gashin tinkiya".


Dariya tayi tace "nima".

"Kice Allah wallahi".

"Babyna tashi muje muyi alwalla kaga kar lokaci ya ƙure munanan muna surutu bayan mun gama we have all the time muyi ta chatting forever".



Bayan sun idar da sallah suka koma kan gado Abdallah ya tura kanshi cikin rigarta tasan dawan garin nan ta bada kai bori ya hau, dan dama ta saba da nacin Abdallah dole take daure mai tana faranta mashi dai dai gwargwado dan ba yada inda zai huta in ba gunta ba, dole take tausaya mashi tana mai haƙuri duk da wani lokacin abun na ci mata tuwo a ƙwarya dan shi kwata kwata baya gajiya da abu ɗaya.







# # # # # # # #

*2:30pm*

Da sauri Asmah ta fito daga ɓangarensu tana so ta kaima Ammie waya dan Naty ce ta kirata suka gaisa nan Naty ke gaya mata ai tana ta kiran wayar Ammie baya shiga shine Asmah tace bari ta kaima Ammien wayar, ko da ta kaimata sai ta juyo ta fito kenan ta hango Jummai sai sauri take ta shige sashen Auntyn yara, da sauri Asmah ta fito daga inda ta maƙe ita ma da sauri ta ƙarasa nata ɓangaren ɗaki ta nufa direct ta kunna system ɗinta, ko ba komai tasan yau akwai data dan ta taɓa jin Aunty na neman Jumman ita dama tun asali Jumman bata mata.



Ta zauna ta natsu tana kallo ba kowa a ɗakin addu'a ta fara Allah yasa su shigo, can ko taga an turo ƙofar Auntyn yara ce ta shigo tana faɗin "Jummai shigo daga ciki tunda yaran na falo".

Jummai ce ta shigo tana turo ƙofar, zama sukai kan gado Aunty ta dubi Jummai tace "haba Jummai wannan dogon zango da kikai mun kina ganin kin kyauta?".


Jummai ta taɓe baki tace "hmmm wallahi wata harkar kuɗi na samu in gaya maki wani garan Alhaji na samu a Abuja ina wankar shi san raina ba dole kijini shiru ba".


"Ke dai Jummai nace maki ki daina wannan masha'ar amman kin ƙi ko?".

"Uhmmm ke dai zauna nan baki san romon da ke cikin wannan harkar ba".

"Ke kika san roman dake ciki tunda ke keyi ni dai ba dani ba sa lallan kaza".

"Daɗi na dake hajiyar nan kin ƙi wayewa har yanzu...".

Da sauri Auntyn yara ta katseta da faɗin "kyaji dashi ciwon ajali a ɗan yatsa wayewar ba, ni ba wannan ba dama tun tuni nake neman numberki dan aikin nan fa da boka ɗarɓusa ya mana an samu matsala".


"Aiko dole ki ta nema baki samu nima ina ta trying numberki bata shiga an samu akasi ne wajen da muke ba network gaba ɗaya dan wallahi muna wani ƙauyen Abuja ne dan na lura Alhajin yana tsoron matar shi sosai ƙarya ya mata fa wai za suje wani seminar a wajen aikinsu shine fa ma muka je mukan ɗan hole, ina jinki garin ya akai aikin ya rushe basu ci bane ko yaya".


"Tabbas fa sunci dan sati guda nayi ina zuba masu shi a abinci amman kwata kwata ni banga wani aiki ba in banda saɓanin shi anya wannan bokan ya san me yake kuwa".


"Hmm kinji ki da wani batu sai kace baki san aikin nashi ba kina magana kamar bai taɓa maki aiki ba kuma baki ga biyan buƙata ba metseew uhmmm kin manta ne ya ce mana Asmah nada taurin kai dan akwaita da sallah da addu'oi sai sa'a za'a ci galaba akanta".



"To ni dai yanzu ina so ya mun wanda zai kamata sosai na dai san harka ce ta kuɗi to akwai su zamu wanke shi dasu kuma, yanzu ni so nake ya mun aikin da zai maida Abdallah matacce amman da rai ma'ana kawai ya kwantar dashi ba ya iya komai shi gashi rayayye amman kamar matacce yake da haka haƙa ta zata cinma ruwa kinga ita Asmah datake taka rawa da bazarsa a gidan nan to zata daina tasiri don ban ma baki labari ba kinga uban kuɗin da suka jibga mata ba'a daɗe ba wai ta fara sana'a na zo shiga falon Alhaji kenan na jiyo su sai na dakata naji mai suke tattaunawa bayan na gama ji haushi ma yasa na juya na lura ita Asmar nan inban gama da ita da wuri ba nan gaba zata hanani rawar gaban hantsi da alama dan haka yanzu a maida mun Abdallah matacce a cikin rayayyau in naga still ita Asmar tana da power to lokacin kawai sai mu kawar da ita, dan na ɗau alwashin matuƙar ni shafa'atu ina shaƙar lumfashi a doran kasar nan to wani tsatson Abdallah ba ze taɓa rayuwa ba balle har anuna mana feleƙe".




Jummai ta karkace tace "lallai shafa ina rainaki ashe kema shaiɗaniyar kanki ce" hannu Auntyn yara ta miƙo ma Jummai suna kashewa.




Jummai tace "kar ki damu ƙawalli da kaina zanje gurin boka in mai jawabi dan nima da aikin da zaimun dan gidan Alhaji na riga na gama shigar sa dan ƴaƴan shi ma biyu ga daula kinga in ci karena ba babbaka balle gashi, dan inshi yana tsoran matar sa to ni zakanya nake sai dai taji tsorona ehe".



Sukai dariya suna tafawa Auntyn yara tace "aiko dakin burgeni kiyi aurenki ki huta da yawan gantalin nan kuma ki zauna a gidan ba kamar auren da kika saba ba ba'a cika shekara kin saki mijin".


"Haba kar ki damu ai ni duk inda daula take to ina nan, dan ni ƴar bautar kuɗi ce".


"Ai yayi kyau bari na shiga in kawo maki na motsa baki".

Jummai ta cigaba da tauna cingam tana faɗin "da kin kyauta".



A hankali Asmah ta rufe system ɗin idanunta sunyi ja kukan da tayi tana roƙan Allah ya ƙara mata katanga dasu yanzu ta ƙara gano halin Auntyn yara da kuma me zugata, tana ƙara gode ma Allah damar da ya bata na sanin muguntar da ake ƙulla masu.



Nan tai ta kuka tana kiran Allah, Abdallah ne ya shigo yana faɗin "beauty kina ina" turo ƙofar ɗakin yayi, langaɓar da kai yayi ganin tana kuka shima duk yaji ba daɗi ganin hawayenta, ɗago idan ta tayi ta kalle shi tuna lokacin da Auntyn yara tace a maida shi matacce cikin rayayyu tai, da gudu ta ƙarasa inda yake ta shige jikinshi shima hannu yasa ya zagaye ta yana faɗin,


"Beauty rigima yanzu kuma me yasa ki kuka, maza ki gaya mun inna kuka ne in taya ki in kuma na farin ciki ne in share maki hawaye dan nasan ke ko murna kike sai kin yi kuka".


Cikin mamki da kwokwonto ko Abdallah ne da kansa ya faɗa wannan maganar ta ɗago tana kallonsa, sai dai da ta kalli ƙwayar idonshi maganar Auntyn yara ke mata gizo, kissing ɗin shi ta shiga yi a duk inda bakinta ya taɓo a fuskar shi tana faɗin "babyna ta Allah ba tasu ba baza su taɓa cin nasara akan mu ba har abada da yardar ubangiji".

"Suwaye beauty?".

"Maƙiyanmu".

"Su waye maƙiya?".

Ganin in ta tsaya mai bayani zata dagula mashi lissafi ne yasa kawai ta hana shi magana ta hanyar haɗe bakinsu waje ɗaya tana jan ajiyar zuciya.






*08:00pm*

Ammie ce ta shiga ta amso wayarta wajen Ammie nan ta samu kanta da tambayar Ammie akan tana so taje gidan Aunty Nafy ta gaishe su tunda bata je ba tun bayan biki to dama ta daɗe tana so ta tambaye ta ta kasa yau ma da ƙyar ta tambayetan, nan Ammie tace mata yaushe kike so kije, Asmah cikin ɗauki tace ko yaushe ma Ammie, nan dai sukai akan gobe ta shirya sai Na iraƙi ya kaita tayo masu wuni ya ɗauko ta da yanma, Asmah tai ta godiya dan bata zata Ammie zata ce gobe ba abun ya zo mata kwatsam, nan suka rabu akan Ammie zata shedawa Abbah batun.




*WASHAGARI*

Tunda safe Asmah ta shirya duk da da ƙyar ta shawo kan Abdallah ya yadda ya barta dan ma tace mashi zata siyo mashi babyne ya yadda dan ƴan kwanakin nan kullum sai ya dame ta akan ta sayo mashi babyn da za suna wasa tare, Abdallah bai yadda suka tafi ba sai data lallaɓa shi yabi Abbah suka fita tukun suka kama hanya bayan Ammie ta cika ta da tsaraba Auntyn yara ma hadda bata lemo mai uban yawa tace ta kai masu.




Asmah ta ɗan tura ƙyaurensu Aunty Nafy tana murmushi dan bazata zatai mata, aiko Aunty Nafy tayi mamakin ganinta kuma tayi murna sosai nan suka ɓararraje suka sha hirarsu, sun ɗan kuma lelleƙa gidajen ƴan uwan Aunty Nafy da suke kusa sun gaisa har gidan Yabi sunje duk inda suka je haka Asmah ke raba masu abun alheri suna san barka tare da jin daɗin zuwanta haka suma suke bata irin su dai kuka kuɓewa da dai sauransu, sai wajen biyu suka koma gida, sun gama sallla kenan Asmah taji wayarta na ringing sunan Ammie ne ke yawo a fuskar wayar, da sallama ta amsa.



Ammie tace "yauwa Asma'u dama wannan ɗan kwangilar nan ne wai yazo amsar wasu takaddu da yace ki aje masa zai zo ya amsa to gashi yazo amsa kuma yana sauri".


"Laa Ammie aiko suna cikin drower ƙasan wadrove ɗita... y".


Da sauri Ammie ta katseta da faɗin "bari kawai naje na ɗauko, ki shirya ƙarfe biyar za'azo ɗaukarki".


"To Ammie sai na dawo".

Bayan sun yanke wayar tace ma mutumin tana zuwa da sauri ta isa part ɗinsu mukullin da Asmah ta bata kan ta tai tasa ta buɗe ta shiga ɗakinta ta wuce direct tana buɗa drower da Asmar ta mata kwatance taga takaddu an kimtsa su a wajen ɗaukowa tayi duka dan ita batasan wanne mutumin ke nema ba tana tashi taga wani ɗan karamin abu ya faɗo duƙawa tayi ta ɗauka nan taga ashe hoto ne juyo da fuskar hoton tayi tana kallo take na hango mamaki da rashin gamsuwa da abunda idanunta ke gane mata kwance a idanunta gefen gado ta zauna tana so tayi nazarin abubuwa a hankali ta buɗa bakinta tace ".........







👸🏼QUEENBK👸🏼

המשך קריאה

You'll Also Like

181K 17K 79
"Sickler gare ta, kuma ku kuka ja mata." Ta yi shiru daga nan, dafe da goshinta, tana jin yadda kanta ke sara mata. "A kullum dad'a wayar wa mutane k...
134K 8.7K 55
Kallon kitse ba litaffina bane na marubuciyar nan ne Halima Abdullahi k/mashi
1.5K 168 22
saukakekken hanyar shiga,Amma naiman hanyar fita it will be diely.......WHEN IN NO WAY OUT
118K 5.1K 63
Labari ne mai ďauķe da tsantsan tausayi mugun hali zafin kishi da nadama, dan Allah ki yafeni kidawo gareni nasan ban kyauta miki ba,, ku bibiyeni h...