ZAN SOKA A HAKA

By queenbk2020

391K 23.9K 2.2K

#5 tausayi June 2020. #3 tausayi 20 June 2020. #1 munafurci #8 hausa novel. #2 tear drop june 2021. More

page 1
Page 2
page 3
page 4
page 5
Page 6
page 7
Page 8
Page 9
page 10
page 11
page 12
page 13
page 1⃣4⃣
page 15
page 16
page 17
page 18
page 19
page 20
page 21
pahe 22
page 23
page 24
page 25
page 26
page 27
page 28
page 29
page 31
page 32
page 33
Page 34
page 35
page 36
AUTHOR'S NOTE
page 37
page 38
page 39
page 40
page 41
page 42
page 43
page 44
page 45
page 46
page 47
page 48
page 49
page 50
page 51
page 52
page 53
page 54
page 55
page 56
page 57
page 58
page 59
page 60
page 61
page 62
page 63
page 64
page 65
page 66
page 67
page 68
page 69
page 70
page 71
Page 72
page 73
page 74
Page 75
Page 76
page 78
page 79
page 80
page 81
page 82
page 83
page 84
page 85
page 86
page 87
page 88
page 89
page 90
The end and thanks.

page 30

3.8K 215 0
By queenbk2020

[10/02 2019 9:43 pm] 👸🏼Queen bk👸🏼:  🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨
🚨🚨
🚨


💎💎💎💎💎💎💎💎
*ZAN SOKA A HAKA*
💎💎💎💎💎💎💎💎
NA
*BILKISU ALIYU KANKIA
👸🏼 *QUEEN BK* 👸🏼




🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITTER'S* *((Z.A.W))*🖊
(Gidan zaman lafiya da Amana  insha Allah🤜🤛 )



Assalamualaikum my lovely readers, i don't even know where to start, wallah am short of words, i know saying sorry only won't settle the explanations you owe me, i know u've been expecting my update, zoo sorry for d disappointment, sincerely speacking am a lazy writter😞, so bear with me, i promise u i will see to that, abin nawa ne sai addu'a fans ku riƙa sani a addu'oinku dan Allah🙏🏻










Page3⃣0⃣

Wahse gari ranar asabar,  tun safe Asmah taje sashen Abdallah, sai dai tana shiga ta fito a gigice ta koma sashen Ammie, sai ko akai sa'a sukai kicib'is da Ammie a kitchen, ganin yadda ta shigo a firgice yasa Ammie saurin tambayar ta me ke faruwa, cikin in ina Asmah ke faɗin "Am-m-mie ya Ab-da-ll-ah" Ammie kam duk ta sha jinin jikinta ganin yadda Asmah ke magana kuma tana kiran ɗan nata, ta san ko meye akwai matsala, da ƙarfi take faɗin "meye ya samu Abdallannnnn"
cikin ƙwalla Asmah ke faɗin "Ammie ya abdallah zai mutu kizo fa kiga me yake"
Ai tun kafin Asmah ta ida magana Ammie ta ɗau hanyar part ɗin shi da sauri tana jin an anbaci mutuwa, Asmah ta rufa mata baya, Ammie na tafe tana maimaita *inalillahi wa inna ilaihir raji'un,* da sassarfa ta ƙarasa d'akin, ba ƙaramin karaya zuciyarta tayi ba ganin ɗanta a ƙasa yana ta birgima yana riƙe cikinshi, duba ɗaya zaka mai kagane yana cikin matsananin zafi na ciwo, idanunshi duk sun kakkafe ga bakinshi sai zubar dan farin kumfa yake, da sauri Ammie ta ƙarasa inda yake ta tallafo kanshi ta rungume shi, hawaye ɗaya na bin ɗaya a kan kuncinta, "ya Allah, ya rabhi ka kawo mun agaji, dan darajar maganganun da ke cikin Al Quraninka mai girma, da son da kake ma fiyayyan halitta Annabi MUHAMMAD (SAW), ya Allah ka sauwaƙe maɗana wannan zafin ciwon, ya Allah ka kawo mashi sauƙi cikin gaggawa, domin a gare ka sauƙi yake, ya mamallakin kowa da komai" duk cikin kuka take maganar, Asmah tace Ameen kana ta matso tace "Ammie a kira doctor mana?" take Ammie ta dawo duniyar dan ita da lissafinta duk ya toshe, duk ta ruɗe ma ta rasa abun yi.

"Yauwa Asmah maza jeki wajen Auntyn yara kice ta kira Dr.Kb, yazo da sauri urgent issue ne, gashi Abbansu baya nan i maza"

Bayan fitarta, Ammie ta maida dubanta ga Abdallah da yake shirin shiɗewa, ganin yadda yake riƙe ciki yana mutsumutsu, bata taɓa ganin Abdallah cikin irin yanayin ciwo haka ba, don shi baya da rakin ciwo shi yasa ma duk ta ruɗe haka, a hankali ta sa hanunta tana shafa mashi kumatu tare da tofa mashi AS'ALULLAHUL AZHIM RABUL ARSHIL AZHIM AN YASH FIKHA, so bakwai, sannan ta karanta mashi LA ILA HA ILLA ANTA SUBUHANAKA INNI KUNTU MINA ZALIMIN so ukku, ta karanta ayatul kursiyy, amanan rasulu da fatiha ƙafa ɗaya ɗaya, sannan ta ɗora da ALLAHUMMA LAKAL HAMDU, WA ILAIKHAL MUSHTAKHA, WA ANTAL MUSTA'AN WA BIKHAL MUSTAGAZ, WA ALKHAL TUƘULAN WALA HAULA WALA ƘUWATI ILLA BILLA, sannan tace ya Allah na roƙe ka da sunayenka kyawawa, kuma nayi tawassali da wannan addu'ar, ya Allah kai ka tseratar da Annabi musa daga kaidin fir'auna ta wannan addu'a, ya Allah ka yaye ma ɗana duk wata cuta, ka raba shi da duk wani mai cutar shi, kamusu katangar ƙarfe ya Allah, kai kace mu roƙe ka zaka amsa mana ya Allah kai me iko ne akan komai, ya Allah kasa ciwon nan kaffara ne kuma ka yaye mashi duk wani cuta da cutarwa gareshi ya rabhi" nan ta shiga tofa mai ko ina a jikin shi.

"Ammie me ya sameshi haka" cewar Auntyn yara muryarta cike da mamaki.

Girgiza kai kawai Ammie tayi, kafin suka ji sallamar Dr.KB, dama tuni Auntyn yara ta gaya mai, kuma dama gidan shi na kusa, infact ma shiyasa ma ya zama resident doctor ɗinsu, kuma an ci sa'a yana gida domin baya call jiya da dare yayi dutyn shi, yana zuwa ya amsa Abdallah bayan sun mayar dashi kan gado take ya shiga duba shi,

Bayan ya gama gwaje gwajensa, ya masa allurar bacci kana ya masa ta pain relieve, sannan ya bada wasu magunguna yace in ya tashi, a bashi sannan a haɗa mashi lipton da lemon tsami a bashi, insha Allah komai zai lafa.

Ammie tace "Dr. Kb har yanzu baka faɗa mun meke samunshi ba, duk ciwonsa bantaɓa ganin kallar wanda ya azabtar dashi ba kallar na yau ba, da alama wani abunne da ban"

"Ay gaskiya wani abunne da ban, amman ki kwantar da hankalinki hajiya ba wani abu bane na tada hankali"

"To inba wani abu bane na tada hankali ka faɗa mun mana"

"Ay zan faɗa amman ina so ne Alhaji ya dawo sai in faɗa maku gaba ɗaya"

"Abbansu sai fa talata zai dawo yaje dubai ne saro kaya"

"Shikenan Allah ya dawo dashi lafiya, bari in tafi da ya tashi aka bashi magungunan kukaga ba dai dai ba ku kirani"

"To shikenan Dr. mun gode"

Yana tafiya Ammie ta ƙara matsawa kusa dashi, fuskar shi tayi fayau baccin shi yake a hankali kuma yana fidda ajiyar zuciya, ta kama hannun shi tana tofa mai addu'oi.

Sai Azahar lis ya tashi duk anbashi abunda Dr. yace a bashi kuma ba laifi yasa mu sauƙi sosai, kawai dai bai iya tashi ne don daya tashi juwa yake ji.


****     ******     *********

"Ki tausaya mun wallahi ina sonki, Asmah na fara fargabar rasa ki wallahi, kin kosan yadda nake sonki bana iya tunanin zan iya rayuwa baki, dan Allah kimun magana mana ko naji sanyi a raina, rashin ansanin nan da kike wallah yana mun illa a zuciya, yana kuma samun kokontan anya baki san da maganar Aunty nafy ba?" Aliyu ne ya gama faɗin haka bayan ya gama koro ma Asmah da yadda sukai da Aunty nafy.

" ya Aliyu bana maka ƙarya kuma bazan fara yanzu ba, bansan magana ko ɗaya akan wannan batun mijin da aunty nafy take magana ba"

" To Asmah yanzu ya za ayi me kika tunanin itace mafita"

Yadda taga duk ya ɗaga hankalinshi akan batun, yasa tayi amfani da muryar lallashi wajen faɗin "ya Aliyuna ka kwantar da hankalinka Asmah taka ce, kuma ka sani nima ina sonka kuma bana fatan rabuwar mu in ba mutuwa ba saiko ƙaddara daba mu iya kaucewa"

"Hmmmmm in kina faɗin kaddarar nan sai in riƙa jin wani yanayi kuma gabana sai yana faɗuwa, dan Allah kin bar faɗin haka zanje inta addu'a kuma kema kina yi, Allah ya fishemu Alkhairi"

"Ameen ya Aliyu"

daganan kuma suka juya akalar hirar tasu...




##################

*RANAR TALATA*

Abbah, Ammie, da Dr.kabir ne zaune a babban falon Abbah, kasancewar Auntyn yara bata nan tana cikin gari gaisuwa,
Dr.KB
ya
maida kallonshi ga Abbah
kana yace wannan ciwon cikin
da Abdallah yayi kwanakin baya da suka wuce
ba komai bane illah yana da
buƙatar mace wato yana da
sha'awa wanda hakan shi
ya haddasa mashi ciwon cikin,
yanzu mafita kawai ammai
aure domin yanayin ciwon
nashi zai iya shan wahala sosai in hakan bata
samu ba, kallon kallon Abbah da Ammie suka shiga yi,
Ammie ta nisa tare da faɗin

" toooo Allah gamu gare ka, hmmmm anzo wajen inji mai kukan wanka yanzu shi Abdallah da ko budurwa baida yaza ai a shawo wannan batun?"

Abbah ya amshe da " to ƙaddara ma yana da budurwar wace ZATA SO SHI a yadda yake balle har ta aure shi?"

Dr.Kb yace "aa Alhaji kar kace
haka akwai mata da yawa
daza su so Abdallah a yadda yake,
domin abdallah gushewar hankali kawai ya
samu kuma shima muna sa
ran bana har abada ba, baya
da haka namiji kamar Abdallah har akwai wacce za amata tayi tace
bata sonsa da kamar wuya,
matsalar kawai wasu matan
ta wani fannin zasu ɗauki
abun, kasan su mata akwaisu da ɗaukar gulma,
wasu kodan kar ace wacce mijinta yana da taɓin hanakali baza ta fara ba,
wasu kuma ko dan kuɗi za
suyi, matsalal shine kuma
azo ba a samu soyyayya a
tsakani ba, domin ya kamata a ce akwai soyyayya mai karfi tsakanin shi da matar shi yadda
zatana kula dashi sosai, kuma
kaga in anyi dan kuɗi maganar so be ma taso ba,
kunga kuma ba tausayi a tsakani,
kuma mu we are not after
that, amman Alhaji mai zai
hana ku bin cika cikin dangi
nasan baza a rasa wacce *ZATA SO SHI A HAKA* ba.

Abbah yace "shikenan Doctor mun gode da shawara sosai insha Allah we will put our effort on that"

Dr yace " Allah ya taimaka bari inzo in tafi"

Ammie tace " To Dr. In ciwon nashi ya kuma tashi ba wani magani da za a bashi?"

"Ay akwai na gaya ma asmah tana haɗa mashi lipton da lemon tsami duk dare tana bashi, haka ma in ya taso kubashi shi komai zai lafa insha Allahu"

"To madallah mun gode a gaishe da iyali"

Bayan tafiyar Dr. Ammie ta dawo kujerar da Abbah yake suka zauna suna fuskantar juna, shiru ne ya wanzu na tsawon daƙiƙa biyar, kowa da kalar tunanin da yake a zuciyar shi, Ammie ta fara cewa

"Abbansu yanzu ya za'ayi kai nake jira ka fara magana"

Sai da ya saki dogon lumfashi kana yace " the issue is complicated saboda yanzu duk cikin jikokin gidanmu yara ne manyan duk sunyi aure, saiko Samira da Amiran ya Aminu ( babban yayansu) kuma ansamasu rana, to sai wa kuma?" ya faɗa tare da nuna alamun yana tunani.

"To Abbansu duk inasu sholin (Aisha) da zainab ɗin ya mustafa ai suma duk sunkai minzalin aure yanzu fa Ss3 suke, ga juwairiyyar Anty Ruƙƙayya ma"

"ohhh to to to na tuna koma dai meye zan samu ya Aminu mu tattauna, Alabashi sai inbar komai a hannunshi, zan kuma samu Aunty uwani ( ƙanwar babansu) da maganar itama bazata rasa ba tunda naga tana riƙa mata da yawa"

"To hakan yayi dai dai nima zan cigaba da bincikawa Allah sa mu dace"

" Ameen, sai dai kisani duk wacce zamu samo sai mun tabbatar zata so Abdallah a hakan da yake, so na tsakani ga Allah nake nufi"

"Ay na fahimta Abbansu Allah ya zaɓa mashi mata ta gari, sai mu dage da addua"





A/N

OUR PROPHET ❤

HE IS THE MOST BEAUTIFUL CREATION OF ALLAH TA'ALA AND HIS NOOR EXISTED EVEN B4 GOD MADE ADAM A.S

FIAMANILLAH
👸🏼QUEEN BK👸🏼

Continue Reading

You'll Also Like

86.1K 4.4K 27
{COMPLETED} Suho adopted 7 children and everything went well, till his partner ran away. He met Lay at Lay's work and Lay became the nanny of the 7 n...
260K 16.6K 47
The feeling of being abandoned by one's own family was not unknown to Aadhira. She hates her family for abandoning her when she was only a newborn, l...
53.4K 1.9K 12
Just walk in and read, I promise u are going to be mesmerize with the emotional love story embedded in this novel.
59.7K 1.7K 29
This will be a Terror Twins X Oc Fanfiction! - Silverspeed is Jazz's twin sister,and it was during a short time after the war on Cybertron had begun...