ZAN SOKA A HAKA

By queenbk2020

392K 23.9K 2.2K

#5 tausayi June 2020. #3 tausayi 20 June 2020. #1 munafurci #8 hausa novel. #2 tear drop june 2021. More

page 1
Page 2
page 3
page 4
page 5
Page 6
page 7
Page 8
Page 9
page 10
page 11
page 12
page 13
page 1⃣4⃣
page 15
page 16
page 17
page 18
page 19
page 20
page 21
pahe 22
page 23
page 25
page 26
page 27
page 28
page 29
page 30
page 31
page 32
page 33
Page 34
page 35
page 36
AUTHOR'S NOTE
page 37
page 38
page 39
page 40
page 41
page 42
page 43
page 44
page 45
page 46
page 47
page 48
page 49
page 50
page 51
page 52
page 53
page 54
page 55
page 56
page 57
page 58
page 59
page 60
page 61
page 62
page 63
page 64
page 65
page 66
page 67
page 68
page 69
page 70
page 71
Page 72
page 73
page 74
Page 75
Page 76
page 78
page 79
page 80
page 81
page 82
page 83
page 84
page 85
page 86
page 87
page 88
page 89
page 90
The end and thanks.

page 24

3.9K 213 0
By queenbk2020

🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨🚨
🚨🚨🚨
🚨🚨
🚨









💎💎💎💎💎💎💎💎
*ZAN SOKA A HAKA*
💎💎💎💎💎💎💎💎
*NA*
_BILKISU ALIYU KANKIA_







🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITTER'S🖊*
(( _Gidan   zaman  lafiya  da   amana   insha   Allah_ 🤜🤛 ))







MURJANATU Y'AR BABA
MAMAN MARYAM
MARYAM YAQUB
MIJINA SIRRINA GROUP

Wanan page d'in naku ne fans kuyi yadda kuke so inayinku irin totally




Page2⃣4⃣






[23/12 4:40 pm] 👸🏼Queen bk👸🏼:




TUSHE MAFARAR DAWA

Alhaji. Zayyan haifaffan garin kano ne, kuma shahararran d'an kasuwa wanda ya bunk'asa ta fannin kasuwanci, su biyu ne a gun mahaifansu, shine na farko sai k'anwarshi Zainab wadda ake cema Aunty uwani, yanzu haka tana aure a garin katsina, tana auren wani d'an siyasa, d'an ta d'aya tilo me suna Muhamud sojan ruwane, d'an uwa kuma aboki ga Abdallah, shi kuma Alhaji Zayyan anan kano ya kafa dangi nan ya auri matanshi biyu, ya kuma tara y'ay'a sha takwas, Muhammad ne na takwas a gidan su yana da k'anne goma kenan, sun taso cikin kulawa da gata domin babansu ba k'aramin mai naira bane, yana da gidajan mai bila adadin na kanshi ma banda wanda suka gada shida Haj.uwani a matsayin gado na iyayensu, ga manyan manyan plazas, super makets, baby's boutique kai da abubuwa ma da yawa da yake dasu, bama garin kano kad'ai ba, don haka iyalanshi ba abunda suka nema suka rasa, ilimi kam ya basu tunda ga kan boko har arabi uwa uba tarbiya, da yaro ya d'an fara tasawa zai fara koya mai kasuwanci, ya nagama secoundary kuma zai bashi jari ya fara ja, yana kasuwancinshi yana karatu a haka har ya samu mata yai aure, matan kuwa duk wacee ta gama secoundary sai ya mata aure ita ma ya bata jari da zatana juyawa, shi Muhammad ya karanci Business Administration ne shiyasa Alh. Zayyan yafi sakar mashi ragamar kasuwancin shi sosai, kasancewar fanin ya karanta kacokan, akwai wata tsohuwar shak'uwa da aminta dake tsakanin su da masarautar Mai duguri tun iyaye da kakanni, to haka abun yazo har kan Alhaji. Zayyan da sarkin dake mulki a yanzu a garin mai suna Sarki Sulaiman Soro da ke kan karagar mulki yanzu, shak'uwa ce ba y'ar k'arama ba tsakanin Alhaji Zayyan da sarki Sulaiman Soro wadda har ta kai soyayya mai k'arfi ta k'ullu tsakanin Muhammad d'an Alh.Zayyan da y'ar wajen sarki Amina, lokacinda iyayen suka tsinci maganar ba k'aramin farin ciki suka shiga ba, don a ganinsu zasu k'ara dank'on zumunci ne, nan da nan aka fara shirye shiryen biki kasancewar lokacin muhammad ya gama karatunsa kuma har ya fara aiki, gashi dama tun kafin ya gama karatun shi ya dogara da kansa, a yayin da ita kuma Amina take shekarata ta k'arshe a secoundary.




*******        *********   
MASARAUTAR MAI DUGURI

Sarki sulaiman gagarumin sarki ne da ake tunk'aho dashi a duk fad'in jahar mai duguri, domin adalin sarki ne, mai son talakawanshi, sam baya k'yamar su kuma yana taimakonsu sasai, shiyasa suma suke son shi, mahaifinsa ya rasu kana ya hau karagar mulki, yana zaune da mahaifiyar shi a gidan sarautar, ana cemata mai babban d'aki, tana da power sosai a gidan shi kanshi bai zartar da hukunci sai ya shawarce ta, duk fad'in gidan daga shi har matanshi ba wanda ya isa ta aje kara ya tsallake, bare kuma bayi da kuyangin gidan, matar sarki sulaiman ta farko sunanta Bilkisu wacce ake kira da Mai gado, auren had'i ne akayi don y'ar uwa ce, y'ay'anta shida kuma duk mata ne, Mai babban d'aki ta kawo mashi mata tace ya aure ta wata k'ila adace ya samu magaji, haka ko akayi ya auri kilishi, sai dai shekararsu hud'u da aure ko b'atan wata bata tab'a ba, nan ma Mai babban d'aki ta kuma kawo mashi wata shuwa me suna Fatima tace ya aure ta ko Allah yasa adace, cikin ikon Allah ko bayan aure da wata tara ta sunkuto k'aton d'anta mai kama da mai martaba sak, hakan ba k'aramin soyuwa yayi ba a zukatan mai martaba da mai babban suna ba, biki gagarumi aka shirya ma sunan d'an, wanda ya tara sarakuna na garuruwa da manyan mutane, anci ansha anyi shagali naira tai kuka, d'a yaci sunan kakansa ma'ana tsohon sarki Aliyu sai ake kiranshi da Yarima Hydar,  duk fad'in masarautar sai ina aka saka ina aka aje ake da d'a da uwan tsabar farinjinin da suka samu gun jama'a, fanin mai martaba kam sai ririta su yake yana tarairayar su, ai kar ku tona a tab'o mai babban d'aki abun yafi gaban wasa, ashe duk abun nan da yake faruwa a gidan Mai gado da Kilishi ba k'aramin b'acin rai suka shiga ba, don haka sai suka had'a kai suka ware ta, suka shiga y'an k'ulle k'ullen su, suna had'a mata makirci, ita ko Allah kawai tasa a gaba, kullum tana cikin addu'a, hakan yasa ta kwanciyar hankali, haihuwarta ta biyu ma namiji ta kuma haihuwa, aka samai Muhammad Areef, sai Nana Amina, sai Nana Halimatu, sai autansu Mustafa, wannan kenan.








****   ******   ***********

Gagarumin biki ne akayi tsakanin Alhj. Muhammad Zayyan da Haj. Amina sulaiman Soro, ba k'aramin shagali akai ba, biki ne na atara dangi a basu labari, bayan an gama aka kai amarya gidan angonta kano a sharad'a, gidan da ya fara ginawa, d'an k'aramin gida ne dai dai zamansu, rayuwa suke cikin tsabta da girmama juna baka jin kansu, a hankali da taimakon Allah Alh. Muhammad ya ta samun albarkar dukiya, domin kullum kasuwancinshi bunk'asa yake, shekararsu guda da aure Allah ya uxurta tasu da samun k'aruwa, Haj.Amina ta haifo d'an ta namiji kyakkyawa, suka samashi Abdallah, Abdallah ya taso cikin gata, so da kulawa fiye da yadda kuke zato, iyayen suka d'auki son duniyan nan suka aza akan d'an nan, haka ma y'an uwa duk inda ya shiga kamar a lashe shi don so, in ta k'aicemaku yaron akwai farin jini, sai da sukayi da gaske sannan suka rik'a d'an nasu, don da yaje hutu ko can Mai duguri ko nan Kano dai su nemi su rik'e shi, sai iyan nashi sun fidda kunya sun nuna masu sufa sam basu yadda ba, kana suke hak'ura, bayan shekara ukku suka haifa mace suka sa mata Urwa, a lokanci Alh.Muhammad ya bunk'asa don yazama shaharrarn mai kud'i, ba k'aramin jida Naira yake ba, shekarar urwa d'aya Alh. Muhammad ya auro Shafa'atu, tunda Allah ya tsaga da rabon aurensu, farko haj. Amina tayi kishi amman daga baya sai ta sassauto ganin yadda shafa'tu ke sonta da y'ay'anta, tana matuk'ar son yaran har sun saba da ita, kuma son tsakani ga Allah take masu, kuma dama ance in kana son kasamu son uwa to kaso y'ay'anta, yakasance ma duk ran girkin Amina a b'angaren shafa'atu suke kwana, yaran ma suna sonta to hakan ne yasa taci auntyn yara, ganin haka yasa Haj. Amina sakewa da ita sosai, suna zaune lafiya da junansu, suka d'auki kansu kamar ya da k'anwa, sam bakajin kansu sai dai abunda ba'a rasa ba tunda zaman tare ya gaji haka, hakan kuwa ba k'aramin dad'i yama Alh. Muhammad Zayyan ba, to hankulan mutanen gidan ya kwanta sai suka zage sukaita zuba y'ay'a, y'ar haj. Shafa'atu ta farko mace aka samata Hibbah, sai ta biyu Hauwa'u wadda suke sa'anni da Shaila y'ar wajen Haj. Amina, daga nan auntyn yara ta haiho yasmeen a lokacin Ammie bata haihu ba, sai bayan shekara biyu ta haifi Bilkisu ( Mimi), bayan wata ukku kuma auntyn yara ta haifo Nihal, ya kasance Abdallah ne kad'ai d'a namiji a gidan, kuma ya saba da Abbah sosai, shiyasa kullum suna tare duk in da zashi Abdallah, komai nashi Abdallah, nikam nace kodan shi kad'ai ne namiji shi yasa yafi nuna yafi nan nan dashi ne oho, yana matuk'ar son y'ay'an nashi, ya basu ilimi boko da arabi ga tsantsan tarbiya, Abdallah an rasa halin wa ya d'auko dan shi kwata kwata magana ba ta damai ba, amman a idon bak'unta, in bai sanka ba to bazakaji surutunshi ba, amman in kuka saba ya sanka to za kaji surutun sa, gashi da tsabta uwa uba wata muguwar natsuwa da yake da ita, wanda ganinka na farko dashi zaka fuskanta haka, sun taso tun suna k'anana shida Mahmud d'an wajen aunty uwani tare, da yake wajen lokaci guda aka haife su, kuma anan gidan hajiyar kano wato mahaifiyar su Abbah aka yaye su, daga nan shak'uwa mai k'arfi ta shiga tsakanin su, da k'yar aka rabasu, suna ko gama primary iyayen nasu suka yanke hukuncin kaisu makarantar secoundary d'aya, London sukayi makarantar MACMILLIAN SECOUNDARY SCHOOL, bayan sun gama su kadawo gida Nigeria, don duk ra'ayin su na karatu yazo d'aya, dukkansu suna son su zama sojojin ruwa ne, don haka suka wuce makarantar sojoji don cinma burikansu.



Sauran k'annan Abdallah kuwa suna gama secoundary Abbah yake aurar dasu, a cewarsa mace na gama secoundary school zai mata aure alabashi in tayi auren shi zai biya mata ta cigaba da karatu har son ranta, kuma dukansu sai sun sauke k'ura'ani a hadda kafin su shiga senior class, kuma sai ya kaisu d'akin Allah kamin ya kaisu na miji, Urwa ta auri mijinta shima d'an kasuwa ne amman akwai ilimin boko sosai na addini kam malami ne, da auranta ta karanci SHARI'A LAW, yanzu haka ita cikakkar Lawyer ce mai zaman kanta, y'ay'anta biyar, ASWAD, MAHEER, NABILA, FATIMA sai BILAL.

Hibbah ma tayi aure, mijinta likita ne yanzu y'ay'ansu uku, MINAL, AKRAM sai SAUDAT.

Shaila da Hauwa'u a tare sukayi aure yanzu suna da y'ay'a d'add'aya, Hauwa'u tana da Fudhal d'inta, a yayainda shaila take da Zaitoona, to iyakar waenda sukayi aure kenan a y'ay'an Alh. Muhammad Zayyan, wannan kenan.







Su Abdallah da Khalil an gama karatu cikin sa'a, bayan an gama k'addamar dasu a matsayin sodojin ruwa (Navy), gida ma ba k'aramar liyafa aka shirya masu ba, bayan an ci an sha anyi bidiri an watse, Abbah ya masu kyautar filaye don su fara gininsu, banda plazas supermarkets da gidajen mai da ya basu akan suyi jari dasu su cigaba da kasuwansu, sannan yace su fito da mata suyi aure, da yake bakinsu d'aya sai suka ce su ai yara ne basu isa aure ba, Abbah rik'e baki yayi yana mamakin wai mai shekara 25 ne yake cema kansa yaro, in haka ne kenan su sadda suke aure jarirai suke, nan ya masu tatas tare da cewa duk wanda bai fito da mata ba a cikinsu dakansa zai mai matar, kullum cikin tuna masu yake, kuma su a zahirin gaskiya basu shirya ma auren bane, kuma ma basu da wadda suke so, har gwanda Khalil yana budurwowi shidai bai da ra'ayin aure yanzu ne kawai, shi ko gogan kwata kwata mata ma basu a gabanshi a lokacin, kullum dai da ya bijiro masu da maganar sai sui ta mai kwana kwana, ana haka har aka masu posting d'insu na first mission d'insu, ba k'aramin jin d'ad'i sukai ba domin wannan ne karo na farko za su fita aiki ba training ba, kuma ki ba komai Abbah zai daina damunsu suyi aure, murna a wajensu kar ku tona haka ma iyayen su, ranar nata matsowa su kuma sai shiri suke, duk sunje bankwana wajen y'an uwa da abokan arzik'i kasancewar basu san iya tsawon lokacin da zasu d'auka ba, don har yanzu bama agaya masu mission d'insu ba da garuruwan dazasu, haka sukajje kowa sai albarka yake sa masu da fatan samun nasara, ranar tafiya suka fito cikin shirinsu na fararen uniform d'insu wanda yake masu kyau abun sai kun gani, jirgi za su hau suje can abuja head quarter su, inda rundunar zata taru kamin a rarraba masu missions d'insu da kuma garuruwa, har airport suka rakasu, sai da jirginsu ya d'aga Abuja birnin tarayya kana suka jiyo bayan sun masu addu'oi.








wash nagaji, sai gobe insha Allah page biyu zan maku in Allah ya bani iko, muje zuwa.






*THERE ARE MORE GOODS BOUGHT BY THE HEART THAN BY THE HEAD.*

👸🏼 *QUEEN BK* 👸🏼

Continue Reading

You'll Also Like

12.3K 1K 56
Shin abinda nayi zan samu sassaucin allah kuwa bare na iyayena,wanda sun yi alkwarin duk wanda yayi mua'amala dani bashi basu. Taya zan tunkaresu bar...
1.5K 168 22
saukakekken hanyar shiga,Amma naiman hanyar fita it will be diely.......WHEN IN NO WAY OUT
3.1K 389 31
Fyaɗe aka yi miki. Shi ne abinda zuciyarta ke ƙara nanatawa. Ban san waye ba, ban kuma san dalilinsa na aikata haka a gareni ba, ni a sanina bani...
53.5K 1.9K 12
Just walk in and read, I promise u are going to be mesmerize with the emotional love story embedded in this novel.