Haleematu (43)

39 2 2
                                    

***Na: Reedahmz
***43

A rude Mu'azzam ya debi ruwa ya watsa mata tayi salati tabude ido taga dagaske kowa yana nan fa ba mafarki take ba tazauna Kawu Umar yace Haleematu ki natsu ki kwantar da hankalin ki kinajina ki fawwalawa Allah kisake barmishi zabi a karo na biyu tunda ga abinda yayanki yace tace Kawu bakomi duk wani abu mukaddari ne daga Allah nayarda da kaddara yace yawwa Allah ya miki albarka tace Amin ya rufe taro da addu'a zuciar Larai fari shikuwa Shamsu yarasa abinda ke mishi dadi koda suka dawo gida kuka kawai yakeyi Mu'azzam nabashi hakuri.

Husna zaune tana shan tea tace wa kawayenta nifa kunga ko number din Mu'azzam dinan ban karba ba tundaga kallon da Shamsu yamin gashi kwana biyu basa zuwa wurin Sofy tace aizasu dawo ne May be busy ne yahanasu fitowa Sholy tace Husna soyayya ba duk kinbi kin rude nifa banga wani haduwarshi ba suka sa dariya dukkan su tace ina zaki gani tunda ba abinda Kikeso bane kuma fa hakane cewar Sholy uhmmm Sofy tayi ajiyar zucia tace yanzu kina ganin Abbanku zai bari kuwa tace in sha Allah hakan nike sa rai kutayani da addu'a kawaii insamu Amincewarshi

Tasallah Tana jin kirar wayar taduba taga Larai tace aiki yaci ya kenan tana dagawa taji farin ciki da Larai keyi tasan aikinta yaci tace ke abufa yayi tace haba dayan kuma sainazo zakiji aida bakin shi ya furta bayason Auranan tasallah tace miye yarage ai nafadamiki aikin malam ba wasa subhanallah kaji bata ko wai malam Amma na karya tunda ba aikin Allah da Annabi yakeyi ba Yan uwa Mata muji tsoron Allah abinda yahanemu mubarshi kar muyi Allah shishigi Allah ya sa mudace Amin takashe waya ita kadai tace saura kuma a mallakewa Rabi'a Mu'azzam kunji son Kaiko

Haleematu zaune tarasa mike mata dadi a ranta Mu'azzam yashigo ya mata nasiha yabata shawarwari tace tagode kuma tasan bayin kan Shamsu bane kaddara ce Mu'azzam yace hakane Shamsu yashigo ya bata hakuri yace baisan mike damun shi ba shidai bayajin dadin garin duka zaikoma gobe tace ina maka fatan alkhairi Yaya suka mike suka fita Rabi'a tazo wai kizo ta taso tazo Baba Laraba tace toh yanzu tunda Shamsu ya janye saiki fito da wani ko Inna Larai tace aa kibarta mana ai zamu jira tunda dama Shamsu aka likewa yanzu ya janye Haleematu tace komi lokacine wurin Allah

Kusan wata biyu bayan fitowar neco Shamsu yafara fafutikar nemar masu admission duk da Haleematu tafara fuskantar kalubale ba rayuwa a cikin gidan duk wanda zaizo wurinta ana cewa yafito sai ya gudu abu dai yakai suna fada mata bakin jini gareta Shamsu da Mu'azzam sunyi yadda zasuyi batun admission abu ya gagara Rabi'a Usman Danfodio University Sokoto sunbata admission ita da Umar Amira itama tasamu Umaru Musa yaradua University katsina Pol science Haleematu ita daya tasamu ABU Zaria Masscom hakanan Inna Larai tace ita dama bataso a hadasu gara waccan mayyar tayi ita daya Amira tace haba dai mama

Haleematu ta shirya tsaf kayanta don tana Allah Allah tabar wannan gida Shamsu dayace zaizo yatafi da ita zuwa Zaria Inna Larai hanawa tayi don Rabi'a da Umar sukadai zasu tafi yace ai Rabi'a tanada Umar sannan Mu'azzam na wani aiki a Katsina zaiyiwa Amira komi tace ai Haleematu ba yarinya bace yanzu yace shikenan Shine yayiwa Haleematu bayanin su hadu a Zaria kawai taje ta nema gafara Inna Larai tace toh Allah sa ayi abinda akaje nema kar abi kwadayi Baba Laraba tace yawwa karki jawo mana abin magana cikin dangi tace tagode tamike ta na hawaye

Haleematu ta shirya tsaf kayanta don tana Allah Allah tabar wannan gida Shamsu dayace zaizo yatafi da ita zuwa Zaria Inna Larai hanawa tayi don Rabi'a da Umar sukadai zasu tafi yace ai Rabi'a tanada Umar sannan Mu'azzam na wani aiki a Katsina zaiy...

Oops! This image does not follow our content guidelines. To continue publishing, please remove it or upload a different image.

HALEEMATU IBRAHIM KATAGUM (UMMI)

Haleematu Where stories live. Discover now