Chapter 1 page 80

195 16 1
                                    

*WANNAN RAYUWAR💐💐💐*
Based on true life story

Chapter One
page 8⃣0⃣

By
*MARYAM SULEIMAN INDABAWA (Antyy)*

*FATIMA MUHAMMAD SANI (ZarahArkel)*
*HALIMA MUHAMMAD SUNUSI (Barrister S@dy)*

🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
*Hakuri da Juriya Online writer's (HAJOW)*✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Dedicated to *Hakuri da Juriya Online writer's Fans* (Allah bar zumunci da kauna)
Wannan littafin sadaukarwa ne ga daukacin masoyan Association din mu wato *HAJOW*

*
Har yamma yana gidan sai ga Sadiya ta ware kamar ba ita ba sai hira suke sha a bar su.

Sai biyar ya mike yace zai tafi tare suka fito dan zatai masa rakiya. Mota ya shiga ta tsaya tana daga masa hannu. Yana zuwa bakin gate yaga Isma'il a bakin gate an hana sa shiga. Kai ya dauke kawai ya bar wajen.

Rokar su Isma'il ya dinga yi nan daya daga cikin gatrman din yace
"Favour daya da zan maka shine na kira ta a waya in ta yadda shikenan."
"Eh naji."

Nan ya fara kiran Sadiya wacce ta juya zata koma cikin gida ta tsaya tana duba wayar ta. Dauka tayi yace
"Ranki ya dade wani ne yazo ya takura sai ya shigo ya ganki wai."

"Waye shi?"
Ta tambaya. Kallon sa yayi yace
"Ya sunan ka?"

Isma'il dake tsaye yace
"Isma'il!"
Shima ya fada mata. Tace
"Barshi ya shigo. Gani nan."

Aka bude masa gate ya shiga. Ya fito yana bin harabar gidan da kallo. Daga nesa ya hango ta ta taho tana tafiya kamar ba zata taka kasa ba. Hijab ne a jikin ta amman yai mata kyau. Blue black wanda ya kara sa hasken ta ya fito. Gaban sa tazo ta tsaya ta harde hannu a kirji. Sai tai masa kwarjini yai kasa da kai ya fara kame kame.

Murmushi tayi dan ta saba haduwa da maza irin haka wanda kallo kawai take musu suke rikicewa.
"Sannu bawan Allah!"

"Yauwah. Ina yini?"
"Lafiya lou!"

Sai sukai shiru can tace
"Lafiya kake nema na?"

"Uhmm da uhm daman daman kawai na ganki ne nake son na kulla friendship dake!"
"Dani?"
Ta fada tana nuna kan ta.

Kai ya gyada kamar kadangare. Tace
"Am sorry bana abota da namiji dan da an fara abota dasu suke canja salon ta. Ni na zata taimako ka zo nema ko wani abu da aka ce ka nace in fito. Ni zan koma ciki in ba wata maganar."

Shiru yayi ta dago ta kalle shi tace
"To sai anjima!"
Ta juya tayi ciki ya bita da kallo kamar yaje ya kamo ta.

Tana shiga falon gidan su ta fada saman kujera tana jin wani sanyi domin Kabir ya amshi soyayyar ta itama zatai aure kamar yadda kowa keyi zata samu miji nagari da izinin Allah. Tinda ita dan Allah take son Kabir ba dan komai ba dan bata san waye uban sa ba ko shi kan sa.

Ranar duk wanda ya ganta daga masu aiki har yayen ta sun sha mamakin yadda suka ga tana farin ciki.

Da dare mahaifin ta na dawowa ya wuce bangaren ta. A falo ya same ta tana kallo. Yana sallama ta mike tana fadin
"Barka da zuwa Abbi na."

"Ah ai jiki yai sauki masha Allah."
Ya zauna itama ta zauna tana fadin
"Bafka da dawowa Abbi ya aiki?"

"Alhamdulillah Daughter ya jikin?"
"Abbi naji sauki."

"Mamin ta kai ki asibiti?"
"No Abbi Kabir ne yazo ya kai ne aka bani magani ya siyon na sha yanzu bana jin komai."

"Masha Allah."
Ta mike ya kawo masa ruwa da lemo tace
"Abbi na kawo maka abincin da na dafa dazu."

WANNAN RAYUWARWhere stories live. Discover now