Chapter 1 Page 62

178 20 1
                                    

*WANNAN RAYUWAR💐💐💐*
Based on true life story

Chapter One
page 6⃣2⃣

By
*MARYAM SULEIMAN INDABAWA (Antyy)*

*FATIMA MUHAMMAD SANI (ZarahArkel)*
*HALIMA MUHAMMAD SUNUSI (Barrister S@dy)*

🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
*Hakuri da Juriya Online writer's (HAJOW)*✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Dedicated to *Hakuri da Juriya Online writer's Fans* (Allah bar zumunci da kauna)
Wannan littafin sadaukarwa ne ga daukacin masoyan Association din mu wato *HAJOW*

Tin da Isma'il ya koma gida ya kasa tsaye ya kasa zaune gaba daya ya rasa nutuswar sa. Kabir ya bashi mamaki haka nan Sadiya ta kara shayar da shi ruwan mamaki domin daman ya gane ita macece mai aji ba kowa take biyewa ba. Amman lallai daga Kabir har ita zasu san waye Isma'il.

Dan shi Kabir zai nuna masa baya neman abu ya rasa zai auri Sadiya sai dai in zai mutu ya mutu. Ita kuma zata shigo hannun sa duk son da yake mata hakan ba zai sa ya hukuntata ba domin ba macen da ta taba ci masa mutunci kamar haka har da mari sai ya shafa wajen yana wani killer smile. Can yai kwafa yace
"Ba zaka burgeni ba Kabir sai ka sauri Halima na gama da ita bana kuma bukatar ta."

Mikewa yayi sai kuma ya koma ya zauna. Yayi haka yafi sau uku yana saka da warwara.

*
Kabir na komawa gida yai wanka ya canja kaya. Cikin gida ya shiga ya samu Hajiyar sa a falo ya gaisheta ta karai masa ya mai jiki sannan ya mike ya nufi dining abinci yaci ya koshi sannan ya mike yai mata sai da safe.

Yana komawa bangaren sa ya kwanta sai dai da ya rufe idon sa sai yaga Sadiya na matasawa Halima kafar ta. Take tunanin Halima kuma ya shiga kwakwalarsa. Tausayin ta kawai yake ji

Bazai ce laifin ta bane domun yasan Isma'il tantiri ne sai dai in bai so abu ba amman zai iya komai dan ya samu wannan abun. Haka nan na yasan kaddarar ta ce Allah ya daura mafa amman yanzu tayaya yarinya karama ta shiga wannan halin wane zata shiga gaba ya lura Halima na son Isma'il wanda shi duk so da kulawar da ya nuna mana na yaudara ne a yanzu babu.

Me zai yi dan ya taimaka mata? Abinda yake ta tambayar kansa kenan. Tuna statement din Isma'il yayi da yaxe
"Sai ka aure ta zaka burgeni."

Kai ya girgiza yana fadin
"Tayaya zan iya auren ta. Hakika ina son ta amman ina kishin ta in na aure ta kuwa ba zan zalunce ta ba dan duk lokacin da na tuna da abinda ta aikata zanji kamar in kashe kai nane zanji na tsani rayuwa ta. Zan sa ta shiga wani hali ne."

Zuciyar sa ya dafe yana fadin
"But i love her ba pride din ta nakewa ba ita kanta nakewa Allah shi yasan dalilin da ya dauran son!"

Hannu ya daga sama yace
"Allah kamar yadda ka dauran son Halima Alllah ka kawon mafita akan sa. Allah ka bani ikon taumaka mata Allah ka bani ikon share mata hawaye Allah ka bani ikon shiryar da ita. Allah ka bani ikon kulawa da ita da kare ta."
Sai ya shfa yana kwanciyya.  Rainin hankalin Isma'il kawai yake hangiwa ace ka lalata yarinya sannan ka guje ta shi kuwa tayaya zai tsaya Isma'il ya samu Sadiya.

Zaune ya mike da sauri
"Dole i tsairatar da Sadiya daga auren Isma'il dan ba mutum aure bane. Sadiya bata dace dashi ba."

"To tayaya?"
Shine shine abinda ya kasa ganewa. Ranar haka ya kwana bai runtsa ba daga tunanin Halima sai na Sadiya.

*
Tin da ta tafi yake neman layin ta amman yaki shiga duk ya sauya a cikin yini daya daka kalle shi zaka san yana cikin damuwa mai tsanani ma kuwa. Yana zaune tin safe bai fito ba.

WANNAN RAYUWARWhere stories live. Discover now