Chapter 1 Page 59

180 20 0
                                    

*WANNAN RAYUWAR💐💐💐*
Based on true life story

Chapter One
page 5⃣9⃣

By
*MARYAM SULEIMAN INDABAWA (Antyy)*

*FATIMA MUHAMMAD SANI (ZarahArkel)*
*HALIMA MUHAMMAD SUNUSI (Barrister S@dy)*

🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
*Hakuri da Juriya Online writer's (HAJOW)*✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Dedicated to *Hakuri da Juriya Online writer's Fans* (Allah bar zumunci da kauna)
Wannan littafin sadaukarwa ne ga daukacin masoyan Association din mu wato *HAJOW*

Ya juya zai tafi. Sadiya ya hango ta shigo asibitin sanye da riga da siket yan kanti  maroon kala tayi rolling kan ta da karamin bakin mayafi hannun ta rike da bakar jaka da bakin hill cover shoe tayi kyau tana tafe kamar ba zata taka kasa ba. Hannun ta rike da waya tana dannawa sannan ta kara a kunne.

Tsayawa kallon ta yayi ta kara wayar a kunne tana fadin
"Hello gani a reception din ina zanyo!"

Dagowa Kabir yayi yace
"Gani nan ina wajen nima."
Ya katse wayar ya karasa wajen ta. Tana ganin sa ta saki murmushi tana fadin
"Kabir ya me jikin?"

"Da sauki!"
"Allah kara sauki!"

"Amin muje ko?"
"Ok!"

Mutuwar tsaye Isma'il yayi a wajen to me hakan yake nufi kenan a ina Kabir yasan ta har suka saba haka anya kuwa yarinyar ce. Ido ya murje ya kara kallon ta ita ce dai dan haka sai ya koma ya zaune ya dafe kai. Can kuma yai murmushi yace
"Shiyasa yake cika baki ba zan aure ta ba. Lallai har yanzu Kabir baka san waye Isma'il ba mu zuba muga."

Ya mike sai kuma ya juyo ya gansu sun sha kwanar dakin da aka kwantar da Halima juyawa yayi yabi bayan su. Suna shiga dakin suka tadda Halima ta farka da sauri Sadiya ta karasa ta dago ta tana fadin
"Sannu!"

Ido ta lumshe ta gyara mata zama sannan tace
"Since when take kwance!"

"Tin jiya sai yanzu ta farka bari a kira Doctor!"
Hafsat ta fada ta fita. Sadiya tace
"Wanka ya kamata tayi sannan a bata abu mai dumi but bari doctor tazo."

Isma'il na tsaye ta window yana kallon ta. Ba a jima ba sai ga Hafsat da nurse dayar kuma ta tafi kiran Fateema. Dubata Nurse din tayi tace
"Ai naga komai ba is normal!"

Dai dai shigowar Dr Fateema kenan ta dubata taga ba matsala sannan tace
"Alhamdulillah a taimaka mata ta gasa jikin ta abata abu mai dumi taci sannan tasha magani Allah bata lafiya."

"Amin!"
Ta juya zata fita Sadiya tace
"Dr Fateema!"

Juyowa tayi ta tsaya tana kallon ta. Sadiya tace
"Baki sanni ba amman ni nasan ki kuma ina jin program naki am Dr Sadiya Muhammad a staff at Aminu Kano teaching hospital!"

Murmushi Fateema ta saki tace
"Nice to meet you ya aiki?"
"Alhamdulillah!"

Suka fita a tare suna dan tattaunawa akan aikin su. Sadiya tace
"Asibitin nan ya burge ni ko na dawo nan ne?"

"Zaki iya aiki a under private bayan kina karkashin federal!"
"Menene ai mu burin mu, mu taimakawa marasa lafiya ba kudun da zamu samu ba."

"Gaskiya ne wannan shine buri mai kyau ga dan kasa na gari."
Har office suka shiga suna tattaunawa akan aiki a haka sukai sallama bayan sunyi musayar number dan har Sadiya tace
"Zatana zuwa tana helping nasu kyauta voluntary."

Fateema tai godiya sannan suka rabu tafi tayi dan komawa dakin da Halima take. A hanya ta hadu da Isma'il yace
"Yan mata!"

Bata juyo ba kara bin ta yayi batai aune ba taga ya sha gabanta hannu ta daga ta zuba masa mari dai dai fitowar Kabir da Hafsat zai mai da ta gida. Ta nuna sa da yatsa tace
"Mind your business na maka kala da banzan yan matan nan ne? Matsan a hanya."

WANNAN RAYUWARWhere stories live. Discover now