Chapter 1 page 79

183 17 0
                                    

*WANNAN RAYUWAR💐💐💐*
Based on true life story

Chapter One
page 7⃣9⃣

By
*MARYAM SULEIMAN INDABAWA (Antyy)*

*FATIMA MUHAMMAD SANI (ZarahArkel)*
*HALIMA MUHAMMAD SUNUSI (Barrister S@dy)*

🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
*Hakuri da Juriya Online writer's (HAJOW)*✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Dedicated to *Hakuri da Juriya Online writer's Fans* (Allah bar zumunci da kauna)
Wannan littafin sadaukarwa ne ga daukacin masoyan Association din mu wato *HAJOW*

Duk yadda ta ji maza hakan bai hana ana kiran asalatu ta mike ba. akan sallaya ta hango shi wannan yasa ta koma da sauri ta kwanta yana ganin haka ya mike ya karaso yana fafin
"Sannu Ummu na Alllah miki albarka yasa ki gama da duniya lafiya!"

Kai tayi kasa dashi. Yace
"Zaki sallah ko?"
Kai ta gyada masa ya shiga ya kara hada mata ruwan zafi ta kara gasa jikin ta ta dauro alwala ta fito sai da ya sata akan sallaya sannan ya fita nasallaci. Ta jima akan tana addu'a Allah basu zaman lafiya ya kau da duk wata fitina bayan ta gama tayi azkhar ta dauki alkur'ani ta fara karantawa.

Karfe shida saura ya shigo tinda ya nufo dakin ta ya jiyo ta tana karatun alkur'ani ido ya lumahe ya karaso. Ya zauna a gaban ta. Tana kai aya ta rufe tana fadin
"Ina kwana?"

"Lafiya lou Zuma ta!"
Dagowa tayi da sauri yace
"Eh mana kin bani zumar ki a jiya wacce har yanzu baki na akwai zakin ta tamkar yanzu na gama sha."

Ido ta rufe ya daga ta yace
"Taso ki kwanta ki huta ai kin gaji da yawa ga gajiyar jiya gashi na saukar miki da wata."
Sukai kan gado suka kwana take bacci ya dauke su.

Basu suka farka ba sai goma da wani abu. A tare suka tashi. Ya shiga ya hada musu ruwan wanka ya fito ya dauke ta sukai ciki sai nonnoke masa take a haka yai mata wankan shima yayi suka fito. Shi da kansa ya shirya ta cikin wata atamfa sea green da ja tai kyau dinkin riga da siket ne ta saka fashion ja ta kwalliyar ta mai kyau.

Shima ya shirya cikin sea green din shadda sukai kyau sai tashin kamshi sukeyi. Dakin ta fara gyarawa ya dauke ta ya kai ta falo yace
"Wanna ni xanyi ai!"

Ya koma dakin. Ya gyara falon ta dinga bi da kallo tana fadin
"Yanzu duk nan daki nane. Allah sarki Abbah na Allah bani ikon yi maka biyayya. Allah kara budi."

Bai jima ba ya fito ya nufi kofa ya dauko basket din da Anty Zainab ta aiko musu da kayan abinci. Anan Falo suka baje suka karya bayan sun gama ya dauke ta ya goya yace
"Muje kiga gidan ki kan muzo kiga kayanki abinda kike bukata sai ki magana a siyo ko?"

Ita dai murmushi kawai tayi. Haka ya zagaya gidan da ita tama ta yabawa ba inda yafi burge ta kamar garden wajen yai kyau da saka nutsuwa.

Sallah azahar da aka kira ira tasa suka baro garden dim. Alwala sukai ya tafi massalaci ita kuma tayi sallah anan. tana idarwa taji ana sallama fitowa tayi taga an kawo musu abinci amsa tayi ta ajiye zata shiga daki ya shigo tsayawa tayi ya karaso yana fadin
"Kinyi sallah?"

"Nayi!"
"Kin mana addu'a?"

"Na mana!"
"Me kika romar mana."

"Zaman lafiya Allahbkauda mana fitina. Ya buda maka."
Yai murmushi yace
"Amin!"

Hannun ta ya ja suka nufi wajen akwatinan saukewa ya hau yi. Akwatinane mai set goma yai kyau nan ya hau bude mata kaya ne masu yawa da tsada ido ta zaro tace
"Wai kayan waye wannan?"

"Na Zuma ta ne!"
"Haba Yaa Muhammad ai wannan wahala ne sai kace ban da kaya."

"Amman ya zama dole dai nai miki lefe ko Ummu?"
"Ba dole bane Yaa Muhammad da dole ne ai Abba zasuyi magana kaga kayan da akai min a gida ne duk na kai wannan ina to ni?"

WANNAN RAYUWARWhere stories live. Discover now