Chapter 1 page 77

179 11 1
                                    

*WANNAN RAYUWAR💐💐💐*
Based on true life story

Chapter One
page 7⃣7⃣

By
*MARYAM SULEIMAN INDABAWA (Antyy)*

*FATIMA MUHAMMAD SANI (ZarahArkel)*
*HALIMA MUHAMMAD SUNUSI (Barrister S@dy)*

🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
*Hakuri da Juriya Online writer's (HAJOW)*✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Dedicated to *Hakuri da Juriya Online writer's Fans* (Allah bar zumunci da kauna)
Wannan littafin sadaukarwa ne ga daukacin masoyan Association din mu wato *HAJOW*


A bakin gate suka hadu da Anty Zainab ya fito a mota ya leka ya mikawa Yaa Suleiman hannu yana fadin
"Sannu mun gode da dawaiyya!"

"Kar ka damu ai kanwata ce."
Ya kalli Anty Zainab yace
"Shine kika baro ta ita kadai?"

"Ko na koma ciki mu zauna tare?"
"Da dai yafi amman kuma ai Yayan mu."

Sukai dariya. Yace
"To Antyn mu mun gode Alah huce gajiya ku gaida gida sai mun zo ban gajiya."

"To muna zuba ido."
Yaa Suleiman yace
"Aci amarci lafiya."

Yai dariya yace
"Nagode!"
Sannan suka tafi ya koma motar sa ya shigar ya dauki bags din da ya shigo dasu ya kai dakin ana falo ya dire sannan ya dawo ya fara shiga da akwatin nan dake bayan motar sa.

Anan falo ya gama ajiye su sannan ya nufi dakin ta. Tana zaune rufe da fuska ya shigo bakin sa dauke da sallama. Gaban ta ne ya fadi murya na rawa ta amsa. Ya shigo ya durkusa a gaban gadon yana bude fuskar ta.
"Tsarki ya tabbata ga ubangiji da ya hallici wannan yarinya."

Ya fada a fili ba tare da ya san ya fada ba. Hakika Ummu tayi kyakyawa ce ya rasa da yaushe tafi masa kyau dan wannan kyan na yanzu wani cool ne mai ratsa zuciya.

Hawayen da ya gani a kumatun ta yasa ya dawo daga tunanin da ya tafi yasa hannu ya goge mata yana fadin
"Barka da shigowa gidan Muhammad hakika ina farin cikin da ban taba yin sa ba a rayuwa. Ina addu'a Allah ya bamu zaman lafiya yasa ni dake mutuwa ce zata raba mu."

Ya mike yana fadin
"Ki daina kuka dan gidan nan babu bakin ciki sai farin ciki insba Allahu kuma abinda kike so shi za ai miki dan haka ki daina damuwa kinji kanwata."

Kai ta gyada yace
"Yauwah!"
Yanzu taho muje kici abinci ko sai muzo muyi sallah ta godiya ga Allah."

Ya fada yana kamo hannun ta mai laushi da taushi. Falo suka isa suna shiga taga akwatuna jibge a gefe. Ya zaunar da ita yace
"Ina zuwa!"

Kitchen ya shiga ya dauko plate da cups ya wanke sannan ya taho dasu. Naman da ya siya ya juye a ciki sannan ya zuba musu lemo ya matsa kusa da ita.

Naman ya dauka yayii bakin ta dashi yana fadin
"Bismillah!"

Dagowa tayi suna hada ido tai kasa da kai ta bude bakin ta a hankali ta fara ci tana ci yana ci har suka gama sannan ya kwashe ya kama hannun ta sukai daki. Ban daki suka shiga sukai alwala suka fito ya shinfidda sallaya ya tada sallah.

Tare sukai raka'a biyu sannan ya zauna yai musu addu'a sosai ya juyo ya dafa kan ta yana mai fadin
"Allahmma inni as'aluka kharaha wa khaira ma jabalta alaihi,  wa'a'uzu bika min sharriha wa sharri ma jabalta alaihi!"

Yana gamawa ya dauke hannu yana mai mata murmushi. Nan yai mata tambayoyi akan addini game da tsarki da sauran su. Bai yi mamaki ba dan yasan wacece Ummu malama ce tana da sani sosai dan in akace kure za ai zata iya kure shi baya tamtama da wannan.

WANNAN RAYUWARWhere stories live. Discover now