Chapter 1 page 57

187 20 4
                                    

*WANNAN RAYUWAR💐💐💐*
Based on true life story

Chapter One
page 5⃣7⃣

By
*MARYAM SULEIMAN INDABAWA (Antyy)*

*FATIMA MUHAMMAD SANI (ZarahArkel)*
*HALIMA MUHAMMAD SUNUSI (Barrister S@dy)*

🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
*Hakuri da Juriya Online writer's (HAJOW)*✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Dedicated to *Hakuri da Juriya Online writer's Fans* (Allah bar zumunci da kauna)
Wannan littafin sadaukarwa ne ga daukacin masoyan Association din mu wato *HAJOW*


Wajen karfe goma ta fito daga bandakin gidan senator Lawal daure take da towel ya kalle ta yace
"Wai ke dole sai kinje gida ne?"

"Kasan me zanje nayi tinda kaji na matsa zani gida akwai abinda zanyi mai mahimmanci."
"Yaushe zaki dawo dan ina son wannan karan mu fita tare dan ba zan iya missing naki ko na kwana daya ba yau ma bansan ya zanyi ba."

Murmushi ta saki tace
"Sai ka tafi gun matar ka ai!"
"Ta bani me?"

"Abinda ta saba baka."
Ta fada tana zama a gaban dressing mirrow. Bayan ta yaje ya tsaya yana fadin
"Ai kuma tin da na hadu dake ko wacce mace lami nake jin ta."

Juyowa tayi tace
"Haba?"
"Kema kin sani Farisa!"

Wani murmushi tayi tace
"Ina yawan fada maka ka saba da wasu matab domin ni ba dauwamammiya bace."

"Farisa ba zan iya barin ki wallahi!"
"Kana da aiki!"

"Ke kike ganin haka ki daure ki auren dan Allah."
"Aure Lawal?"

Kai ya gyada yana dafa kafadar ta. Yace
"A yanzu ba aure a gaba na."

"Saboda me Farisa?"
"Saboda abu biyu zuwa uku."

"Ina jin ki!"
"Kaga na daya halin ku!"

"Menene da halin mu."
Ya fada yana mikar da ita tsaye. Tace
"Da kun auri mace kun daina nuna mata soyayya sai ta zama shara a gunku sai ku fita neman wasu matan!"

"In na same ki ni wacce mace zan fita nema?"
"Hmmm Lawal kenan!"

"Da gaske nake.bayan shi sai me?"
"Ban gama tara abinda nake so na tara ba."

"Kamar?"
"Dukiya mana."

Yace
"Ki fadan ko me kike so zan baki."
Wani murmushin rainin hankali ta saki tace
"So nake nafika kudi gaba daya ma kai kan ka dan ban dauki abinda kake dashi a bakin komai ba."

"Farisa daru Baby!"
Tai murmushi yace
"Kin fi karfi na dai kenan ko?"

"Ba haka bane. Matsala daya ita ce ba zan iya auren wanda mukai *wannan rayuwar* dashi ba."
"In na tuba fa!"

"Sai gaba dai amman kasan me?"
"Sai kin fada!"

"Kai ba sona kake ba."
"Saboda me kika ce haka?"

"Saboda nasan haka ne. Kana son jiki nane kawai!"
"Haba Farisa wallahi da gaske ina son ki ba dan abinda kike dashi ba."

Wata dariyar rainin hankali tayi ta mike tace
"Hmmm ban yadda da dadin bakin ku ba Lawal!"

"Ki yadda dani Farisa ina son ki dan Allah ba dan ni'imar ki ba zan iya zama dake a ko da wane hali."
"Ina jin kalaman nan agun maza da yawa amman narasa gane na gaskiya."

"Lokaci zai zo da zai nuna hakan!"
"In yayi na tabbatar!"

"Kefa kina so na?"
Dariya tayi tace
"Ni bana son kowa yanzu tukunna amman kana daya daga cikin wadan da ke burgeni da jin zan iya rayuwa dasu."

WANNAN RAYUWARWhere stories live. Discover now