Chapter 1 page 58

241 22 0
                                    

*WANNAN RAYUWAR💐💐💐*
Based on true life story

Chapter One
page 5⃣8⃣

By
*MARYAM SULEIMAN INDABAWA (Antyy)*

*FATIMA MUHAMMAD SANI (ZarahArkel)*
*HALIMA MUHAMMAD SUNUSI (Barrister S@dy)*

🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
*Hakuri da Juriya Online writer's (HAJOW)*✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Dedicated to *Hakuri da Juriya Online writer's Fans* (Allah bar zumunci da kauna)
Wannan littafin sadaukarwa ne ga daukacin masoyan Association din mu wato *HAJOW*


Kudin yaje ya biya kusan dubu hamsin da biyar sannan ya wuce zai tafi dakin da aka kwantar da Halima. Isma'il yace
"Wai ka tsaya muyi magana mana."

Tsayawa yayi yace
"Menene?"
"Akan Waccar yariyar mana!"

"Wa fa?"
"Wacce na hada ku!"

"Oh Sadiya?"
"Sunan ta kenan!"

"Yes!"
Kabir ya bashi amsa. Isma'il
"Wow nice name."
"Eh mijin Halima da Sadiya ba!"

Fuska ya dan bata yace
"Ya kukai?"
"Uhmm nothing mun gaisa ne kawai. Isma'il Halima fa ba lafiya!"

"Allah sauwake!"
Kallon sa Kabir yayi yace
"Kamar ya Allah sauwake. Ko da yake Amin sai me kuma?"

"Shikenan me zan mata ni na daura mata ciwon!"
"Isma'il kasan ba zan shige maka batun auren Sadiya ba sai ka fara auren Halima!"

"Akan me?"
"Saboda ita ya cancanta ka fara aura."

"To uba na."
"Me...?"

"Eh nace to uba na!"
"Me kake nufi?"

"Abinda nace ka sani wallahi baka isa ka sa na auri Halima ba dan yanzu bana son ta."
"What?"

"Eh bana son Halima ba zan aure ta ba Sadiya nake so!"
Wani murmushi Kabir yayi yace
"No wonder! Mu shiga daga ciki na kai magunguna nan!"

Wani kallo yaiwa Kabir sannan yabi bayan sa suka shiga dakin. Yana ganin Hajara yaji jinin jikin sa ya tsinke. Kabir ya mika mata ledar maganin yace
"Ya jikin nata?"

"Da sauki."
Wajen gadon ya karasa ya ganta tana bacci kana gani kasan ba baccin dadi take ba. Duk ta rame.
"Ina yini Yaa Isma'il?"

"Lafiya lou ya kike?"
"Alhamdulillah kaga Anty Halima ba lafiya ko?"

"Allah sauwake ai ban sani ba me yake damun ta?"
"Nima ban sani ba"

Kai Kabir girgiza kawai ya dago daga kallon Halima dai dai fitowar Hafsa ta fito daga toilet kenan tace
"A'ah har ka dawo Kabir?"

"Eh! Ya jikin nata?"
"Da sauki me tace maka?"

"Bill ne daman sai jan hankali akan kula da lafiyar ta da rage mata damuwa sannan a kula da kalar maganin da zata na sha."
Yai dan murmushi yace
"Sai batun bedrest da suke ta bayar wa wai a barta kar ta kara samun wani har sai na da six month."

Itama murmushin Hafsat tayi tace
"Allah sarki. Allah bata lafiya angode nawa ne bill din?"

"An biya ai ayi ta addu'a Allah bata lafiya kawai."
"Insha Alahu amman Kabir ai dawainiyyar tai yawa."

"Ba komai."
Wayar sa ce tai kara ya dauka ba tare da ya lura da mai kiran ba. Tace
"Assalamu alaikum!"

"Wa'ailkun salam wacece?"
"Sadiya ce!"

"Sadiya kuma?"
Tace
"Wacce muka hadu jiya!"

"Oh Sadiya ya kike ya gida?"
"Alhamsulillah ya kake?"

WANNAN RAYUWARWhere stories live. Discover now