🥀KARSHAN🥀
🥀WAHALA🥀
🥀By🥀
🥀SAFNAH ALIYU JAWABI🥀
(B🥀H🥀W🥀A)
🎄🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🎄🎄🎄🎄🎄🥀🥀🥀🎄🎄🎄🎄🎄
🎄🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀
🎄🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🎄
🎄🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🥀🎄
🎄🥀🥀🥀🥀🥀🥀🎄
🎄🥀🥀🥀🥀🎄
🎄🎄
Innalillahi wainna ilaihi raji'un
ALLAH yayiwa kanina Muhammad sani rasuwa,jiya akayi addu'ar uku Ina cikin alhinin Haka Kuma sai ga wata rasuwa wacce girgizar da nayi baxata misaltu ba, kawata asabe Ina rokon ALLAH ya gafarta Miki duk kannin zunuban ki ya sada ki da duk kannin alkairi zamu hadu IN SHA ALLAH agida Mai cike da ni'ima wato gidan aljanna zanyi kyawar ki harzuwa KARSHAN numfashi na miss you.
Bismillahi rahamanin
Da ma'maki lantana ke Kallon laure Dan ta fuskanci daga jikin ta warin ke fitowa.
Ganin lantana na niman Bata Mata lokaci yasa asabe ta cakumo wuyar rigar lantana shake ta tayi da duk karfinta tana cewa,"ke ballagaza abincin Yan cirani Ina Kika kai min yarinya?
Zazzaro ido lantana ta shigayi Dan tun ba yau ba ta dade tana Jin labarin karfi irin na asabe, Dan kuwa maza ma Haka suka ganta suka barta.
"dabara ce ta fado mata, murmushi tayi tace,"ke kuwa ALLAH yayi Mara wayau ni Ina Nan Ina tunanin yanda zan tallafawa rayuwar ki Amma ke kina Nan kina shashanci dallah sakar min riga.
Sakin ta asabe tayi tana jiran jin abinda zata fada mata.
Kujera lantana ta jawo dama da ragowar kudi cikin jakar ta Wanda hajiya ta bata dubu talatin ne yayi saura,dubu goma ta zaro ta mikawa asabe,jiki na rawa asabe tasa hannun ta karba tana murmushi.
Kallon banza lantana tayi Mata tace, wallahi kinyi da Mai yi bazan Kuma kawa Miki kudi ko sako ba koda kuwa basira ta aiko ni.
Da sauri asabe ta shiga Bata hakuri Saida taja Mata aji sannan ta nuna ta hakuri Amma cikin ranta tsoro ne fal.
Da murmushi akan fuskar laure tace,"kawar Ina nawa Kinga dai halin da nake ciki abincin cima gagarata yake.
Tsawa lantana ta daka mata tana cewa,"ke dalla rufa Mana baki Ina ruwa na da halin da kika tsinci kanki aciki, nice na saka ki acikin halin ko kuwa?
Baki bude laure ke kallon lantana Dan Bata taba zatton Haka daga gare taba,Haka tanaji tana gani suka fice daga gidan suna tafawa.
Kuka laure ta sake tana data sanin halin data saka kanta duk adalilin hudubar lantana.
In takaice Miki yanzu laure saidai Wanda yaga ALLAH da (annabi)ya dauka ya bata.
Lantana kuwa tun daga lokacin Bata kuma waiwayar garin Nan ba.
Ajiyar zuciya*SAFNAH*ta sauke hawaye ke bin fuskar ta idon ta kuwa duk sun canza kala,lallashinta mom ta shigayi da kyar suka samu ta kwanta tayi barci,dakin mahaifin maimuna aka Kai *NASIR*da kannan mahaifin sa, maimuna kuwa babu yanda innar ta Bata yiba kanta tafi gida inyaso gobe ta dawo.
Aikuwa kenkeshe ido tayi tace batasan zancan ba Haka dai Inna tayi hakuri ta barta ta kwana.
Washa gari da safe duk suka shirya bayan sun gama karin kumallo suka dauki hangar gidan kakan nin *SAFNAH*tunda suka dau hanya take jin faduwar gaba ga wani irin sanyi da jikin ta yayi,lura da hakan yasa maimuna ta ruko hannun ta tana Mata magana Wanda Ni kaina bAnsan me take fada Mata ba saidai ga yanda Naga *SAFNAH*ta baka Mata duka nasan zolayar ta take.
(Kawan ce wacce aka Gina ta domin ALLAH Haka take kasancewa bazan taba daina godiya ga ALLAH daya azurta Ni da samun kawa irin kiba MAIMUNA ALIYU Ina alfahari dake ALLAH ya raya muktar RAMADAN)
Afeeya kuwa Basu suka isa garin ba sai bayan sallar isha abinka da wayan da basu San gari ba.
Tarba Mai kyau suka samu Dan mahaifiyar Jameel cire kunyar tayi agefe ta shiga hidima da bakin ,dan ganin da gaske dai asabe ba taimaka Mata zatayi ba, alhamdulillah kawai afeeya ke furtawa lokacin da tayi ido hudu da mahaifiyar Jameel sai asannan tagane tsantsar kyaun Jameel yasamo asaline daga mahaifiyar sa.
"Hira suka shigayi sosai da nuna tsantsar missing din juna da suka yi.
"My ruhee har yanzu dai *SAFNAH*babu labarin ko?
Ajiyar zuciya ya sauke yace,"har yanzu shiru saidai ki sani ban taba cire tunanin ta ko mancewa da ita Koda kuwa na Rabin sa'a bane.
,"ALLAH ya baiyanar da ita aduk inda take,tana kaiwa nan ta tashi batare da ta kuma juyowa ba kiranta Jameel yake Amma ina,dafe kansa yayi Yana Jin bai kyauta ba dan ko babu komai Bata taba nuna kishi akan *SAFNAH*ba hasalima ko da yaushe tana nuna tafi kaunar ta akan yanda shi yake ikrarin Yana kaunar ta.
Murmushi yayi yace,"IN SHA ALLAH gobe zanbiya sadakin ki agaban kowa da kowa bazaki tafi daga garin Nan ba Saida saka ranar aure na akanki.
tabar Mar dake kofar dakin ta zauna tana rizgar kuka iya son ranta Saida tayi Mai isarta sannan ta wanke fuska ta shiga ciki da niyar barci Amma saidai me yanda taga safe haka taga dare Dan kwanta kwata babu alamun barcin ko kadan atattare da ita.
Kasancewar dare yayi sosai kafin su iso garin, hakan yasa lantana ta kaisu gidan kawar ta suka kwana,washa gari da safe suka nufi cikin rugar su,har kofar gida motar da suka dauka tasha daga cikin izom zuwa rugar ta sauke su,jin karar mota yasa asabe lekowa Dan ganin abinda ke faruwa.
Bude marfin motar yayi daidai da fitowar mahaifiyar Tata, suna hada ido ai da gudu asabe ta nufo ta tana cewa ,"wa nake gani kamar yar lele ta? murmushi basira tayi daga cikin motar ta na cewa,"nice inna.
Shewa hade da guda asabe ta shigayi tana cewa,"Ina mahassada yau dai kufito kuga yanda yar lele ta, ta dawo kamar yar'kasar ketare.
Jin hakan yasa basira tashi da niyar fitowa asabe na ganin haka takara ingizata ciki tana cewa,"zauna Yar lele karki fito sonake wayan Nan Yan bakin cikin su fito su gayanda kika koma.
Kuka Mai karfi basira ta sake tana ALLAH wadai da hali irin na mahaifiyar ta,nan Danan kuwa mutane suka fara fitowa ta ko ina Dan ganin basirar.
Ganin yanda basira ke kuka ga lantana agefe tana tayata yasa gabaki daya asabe Tasha jinin jikin ta dago fuskar basira tayi tace,"ke lafiyar ki kuwa daga dawowa sai kuka meke faruwa?
Sandar da take dogarawa dashi ta dauko ta dagara ta fito daga cikin motar tunda asabe taga sandar ta sandare agurin tana jira taga ikon ALLAH ga mutane cike azagaye dasu.
Tafiya ta farayi tana dogara sandar kallon asabe tayi tace,"gani na fito mutane suga yarda ku biyu kuka take rawar gani wajan salawantar da rayuwa ta, nuna lantana tayi wacce tun zuwan su take zubda hawaye.
Kamar mayunwa cin Zaki haka asabe tayi kan lantana,ga ma'maki na lantana ko gizau batayi ba,duka asabe take kai mata ta ko ina Amma ko alamur mayar da martani ko kare Kai lantana batayi ba, dan ita kanta ji take ta gaji da rayuwar ma gabaki daya.
Ganin tana niman illatata yasa mutane suka shiga tsakanin su,ita kuwa tuni basi ta shige ciki tana kuka wacce take Jin bazata taba daina yin taba.
Da kyar aka samu aka kwace lantana daga hannun asabe.
Asabe na shiga gida ta samu basi kwance tana rera kuka,dafita tayi tana cewa,"garin ya Haka ta faru basira ta yayi hakan ta kasance?
"Niman kudin da kika turani Inna niman kudi gashi na dawo da kudi Amma babu kafa.
Kuka duk kansu suke daga bisani basira ta baiwa innar ta labarin abinda ya faru Bayan barin su garin babu Abinda ta rage daga abinda ya faru harda wanda tayi.
Kuka asabe keyi kamar ranta zai fita.
🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄
Layin gidan asabe suka fara wuce wa kamar zasu shiga Amma sai inna wato mahaifiyar maimuna tace su tafi can family house dinsu idan yaso sai ita tazo ta gaishe ta daga baya.
Bugun zuciyar*SAFNAH*kuwa Kara tsanan ta yake kamar zuciyar ta zata Faso girjinta ta fito,a Haka har suka karasa kofar gidan.
Sallama sukayi daga kofar gidan sannan suka tsaya jiran abasu izinin shigowa.
Muryar da ta amsa sallamar yasa*SAFNAH*dago Kai da sauri Jin muryar da bazata taba mancewa da ita ba .....
Kuyi hakuri dani
Barka da sallah to all Muslims umma