Yace, "Ashe zamu kwana mu yini anan, meya kuke san jin labarina?

Taufiq yace, "Haka kawai ni ina san nake jin labarin mutane. Ka sani ko littafi zan wallafa".

Jinjina kai kawai yayi yana kallon yaran cike da sha'awar su. Sun burge shi kuma sai suka haɗu da mutum mai sauƙin kai da ya biye musu shirmen su.

"Yi min magana da Ogan na ku".

Ya faɗa yana duba agogon hannun sa.

"Ka yi magana da ni kawai kai tsaye nine Chief Executive ɗin ai".

Taufiq yace, "Nine rabu da wannan. Me kake so".

"Assalamualaikum".

Cewar Deeni yana ƙara miƙa hannu suks gai sa. Sannan su Ameer suka wuce suka tafi wurin wani hallau da ya zo.

"Da farko sunana  Umar Babangida, anan Gumel nake, ni ɗan siyasa ne sannan kuma ɗan kasuwa. Ina da shaguna  a cikin wani garin na nan Jigawa. Na zo ne domin na siya kayan ku na gwada s shaguna sabo dana buɗe na drinks".

"Bansani ba ko bakwa sararwa".

Murmushi Deeni yayi yace, "Zamu so mu haɗa kasuwancin mu da kai".

Ya faɗa yana miƙa masa suka gaisa. Shima ya karɓa yana murmushi. Daga nan suka yi exchanging numbers da shi sannan ya haɗa shi da Moddibo yayin da Moddibo yace za'a kai masa duk inda yake so.

Ameer ya kalla shida da Taufiq yace, "Ina gayyatar ku bikin yarana, nan da wata uku zaku zo?

Taufiq yace, "Zamu zo ko Yaya?

Ya faɗa yana kallan Deeni, murmushi kawai Deeni yayi bece masa komai ba.

Ameer yace, "Idan kana so, muna album ɗin biki, muna abubuwa da yawa ga numbern mu".

Ya faɗa yana miƙa masa katin sa da na Taufiq karɓa yayi yana karata abun jikin kafin kawai ya jinjina kai yana ce musu za su yi waya. Sannan ya tafi yana mamaki wannan ahali, shi kam sun yi masa daɗi bisa ɗari tun jiya da ya kalle su, balle kuma da yaran sa suka ringa cewa abin yayi daɗi, idan suka ce yayi to yayi ɗin.

******Kasancewar yau za'a koma hutu yasa ta shiryawa kawai ta tafi abinta tare da tare Napep ta shiga, ko wurin su Umma bata je ta gaida su ba, dan jiya yini suka yi ita da Hajja suna mata zancen Deeni bawan Allah. Yayin da ita suke ɗaura mata laifi, shiyasa suma ta basu space bata koma ba da daddare ita kadai tayi kwanan ta a part ɗin ta. Sai da ta fito tayiwa Umma waya wai ita ta wuce.

Hajja da ita ɗauki wayar tace, "Kin cewa mijin ki yau zaki koma wajen aiki?

Haɗe rai tayi kamar tana ganin ta.

Tace, "Ai hutun daman kwana biyu ne ranar sallah da jiya".

"Kya sanar da shi ai, dan yau za su dawo fa".

"Tunda bansan tafiyar su be kamata nasan dawowar su ba".

Ta faɗa tana kashe wayar ta tare da hawa tsare napep. Idan ran ta yayi dubu to ya ɓaci, haka kawai wani can yake ɓata maka rai. Sanda ta zo babu wanda ya zo sai ita kadai sai a wurin na su, bata damu da cewar ita kaɗai ba ce ba, ta shiga aikin ta. Tana nan taga fitowar Ogan na su ya do so ta yana waya.

"Dan Allah nace ko zaki taimaka ki ɗauko mana hotan wani gida".

"Amma ai ba aiki na bane ba".

Ta faɗa kan ta tsaye cikin halin ko in kula.

"Ba wanda ya zo, kuma tun kafin sallah yake sanar dani. Dan Allah taimaka min, na masa alƙawari".

Sai da ta haɗe rai. Sannan tace, "Nifa ba zaka cuce ni ba, waya sani ma ko kashe ni zaka yi, ko s cutar da ni. Tunda ƙiri-ƙiri kun nuna bakwa so na".

ZARAHADDEEN Opowieści tętniące życiem. Odkryj je teraz