GN-3

2.1K 222 26
                                    

Kuka nai mai isata sannan na tashi na shiga bandakin na wanke fuskarta na fito na nufi gaban madubin na dan shafa mai kadan da hoda sai dai hakan be boye kumburin da fuskata da kuma idanuwana sukai ba.
  Hijab din da yai yanayi da farar atamfar da nake saye na dauka na saka sannan na dauki wayata na saka a jakata na dauki laptop din na saka takalmi na fito daga dakina. Yau ban tsaya bin ta kan Amal ba balle har na kaita da kaina gidan kanensa daman wani lokacin shi yake kaita idan na fita na barta a gunsa wani lokacin kuma ni nake kai ta sai dai idan ni na kaita ta fi min kuka saboda takuwa irin nata. Na saba daman a duk lokacin da zanje aiki sai dai naje a napep ba dai ya kai ni ba, kusan tun da na fara aiki sau biyu ya taba rage min hanya ya kai ni da motarsa, babu kuma yadda ban yi ba da shi akan ya siya min mota amman ya ki ba dan bashi da hali ba, sai dan ya fi son nai ta wahalar zuwa aiki a napep ga kuma kai yara scul da nake duka a napep, ya bar ni da dawainiya kala kala kamin a dan bashi da halin dauka ba sai dan keta irin na shi.
  Har na shiga napep ban daina tunanin wayar da naji yanayi da wata ba, ciki har da zancen kudin da zai bata bayan ni na roki alfarmar ya cika min na samu na siye injimin wanki yace min ba shi da su, ga kuma zancen hutun daya samu har yana fadin wane gari take son suje, ada can kam na kasa yarda cewar Aminu yana neman matan banza duk kuwa da kasancewar ina ganin chat dinsa da wasu matan wani lokaci ko kuma na ji yana fira da su, sai dai a nawa tunanin irin chatting din nan ne na budurwa da saurayi da maza suke yi, wanda ba zaka iya raba maza da shi ba, sai dai ganin condom a aljihun wandonsa ya tabbatar min da abunda Abdallah yake yawan fada min, sukar auren da yake min na uban diyata yau na tabbatar da shi, no matter what Aminu zai fada min ba zan taba yarda ba, taya abokinsa zai bashi ajiyar condom miyasa shi ba zai aje da kansa ba sai ya bashi ajiya? Ban san lokacin da kuka ya kubuce min ba, ashe tun da na soma tunanin nake hawaye ban sani ba.

“Hajiya Lafiya dai?”

“Lafiya kalau dan Allah juya da ni inda ka dauko ni”

Na fada ina jan majinar hancina,tare da saka hannuna na share hawayena. Kamar yadda na umarce shi haka ya juya ya koma, sai dai ban bari ya karasa ba na tsayar da shi na sauka na bashi kudin shi, daman ba gidan zan koma ba, gidan su kawata Hajara zan je na saba zuwa can a duk lokacin da abun duniya ya taru yai min yawa ita kanta da zarra ta ganni ta san akwai wata matsalar. Sallamar da nai cikin muryar kuka ce ta karantar da ita ina cikin wani hali.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”

Shi ta furta amaimakon ta amsa min sallamar, ta aje Affan da ke hannunta saman kujera ta taso ta nufo inda nake ta dafa ni ganin kamar ba zan iya karasowa saboda kukan da ya koma min sabo.

“Halimatu”

“Na'am”

Na amsa daker, sannan na zauna a kujerar da ke kusa da ni ita ta zauna kusa da ni tana ta kallon kukan da nake cikin damuwa, har sai da nai wanda zan iya sannan na labarta mata abunda ya saka ni kuka a yau.

“Wata kila da gaske ajiya aka bashi, ki rika kyautata masa zato dan Allah”

Kaina na daga na kalleta.

“Idan wacan ajiya aka bashi wayar da na ji yana yi fa?”

Sai tai shiru domin a nan bata da amsar ba ni, ina da tabbacin babu wani abun da zata fada da zai kare shi a nan.

“Ba zan ce kunne ki be ji daidai ba, amnan ina son ki sani yawancin mazan nan haka suke, suna nan kashewa matan waje kudi ko da kuwa ba su yi ma na gida ba, ki yi hakuri Halima”

“Ko da yaushe idan na fada miki damuwa nai shiru kike cewa, ba ki tunanin hakurin nan zai iya zame min illa? Wallahi na gaji Haraja na gaji”

“Karki gaji da bautar Allah, ki dauki aure a matsayin idaba kuma ibadar da ta fi ko wace wahala, dan'adam be tana yin hakuri ya kasa cin ribar hakurin ba, idan rashin kyautawa Aminu baya kyauta miki amman ki yi hakuri wata rana za ki ji dadi”

GOBE NA (My Future)Where stories live. Discover now