50

2.2K 308 222
                                    

TWO MONTHS LATER....

Alhamdulillah Thumma Al-hamdulillah.
  Godiya ce abunda ta cancanci fita daga bakina na yanzu, izuwa ga mahallincina ko da kuwa ina cikin tsananin rayuwa ballantana yanzu da rayuwar ta fara sauya min.
Abubuwa da yawa da ban zata ba daga Ahmad suna ta samu na, ni da shi a yanzu kusan mun zama abokai, yana sake min sosai yana fada min abubuwan da za su kwantar min da hankali, yana dora ni a kowace hanya ta jagoranci.
Ban tana sani haka yake da sakewa da son jama'a ba sai yanzu, a cikin abubuwan da yai minba kamar yadda ya dukufa a nemawa Kabir Lafiya, wanda farinciki ba ni kadai ya saka ba har da yan'uwansa domin na ga hakan a fuskarsu, asibiti aka maida shi suka masa duk wani gwaje gwaje daya kamata, sannan suka dora shi akan magani, duk wani abu da za a kashe masa ko aka kashe masa ta aljihun Ahmad yake fita.
   da abun ya ki yi a nan ne suka tura asibitin sokoto wato uduth, tare da yan'uwansa biyu aka je, da kuma matarsa.
  Bayan nemawa Kabir lafiya kuma yarana ya saka su a makarantarsa, school bus ke kaisu tana daukosu.
  Wani lokacin ina da na kalleshi sai na ji kamar na bude masa zuciyata yaga irin farincikin daya saka ni, idan kuma na tuna abubuwan da suka faru tsakaninmu sai nai dariya, farkon haduwarmu da kuma abubuwan da yai min na cin fuska kamin yanzu, da kuma yadda muke a yanzu sai wani abun ya bani dariya wani kuma ya bani mamaki.

Kamar ko yaushe yau ma na shirya shirin zuwa aikina, cikin bakar abaya kusan abaya tafi yawa a cikin tufafi domin ina jin sakewa sosai idan na saka ta gashi babu ruwanka da wani rike hijab ko gyara gyale.
  Ban yi kwalliya ba, hoda ce kawai na shafa bayan mai sai dan turaren da na saka, sannan na shafa dan mai a bakina na dauki bakar jakata na rayata na nufi dakin Mama nai mata sallama, a tsakar gida na samu Inna ita mai mata sai na dawo na kama hanyar zuwa office din rai na fes.
  Na samu napep daf da kofar gidanmu ya sauke wasu sai kawai na tsayar da shi na fada masa inda zai kai ni sannan na shiga.
   Misalin tara da yan mintuna na isa office din, ko da na shiga na samu komai tsaf kamar kullum, wato masu gyara office din sun gyara shi sai kamshi yake. Jaka na aje a inda na saba ajewa na nufi window ya bude abun mamaki yau Ahmad ya shigo da wuri na hango shi jikin windows sa tsaye hannunsa daya rike da mug dayan kuma a aljihunsa har yana dago min mai kofin alamar gaisuwa. Ni kuma na daga masa hannu ina murmushi sannan na juyo na zauna a kujera na fara aikina.
Knocked akai kamin na ce komai Yunus ya turo kofar office din ya shigo.

“Good morning”

“Morning how are you sir”

“Fine, hope dai baki gaji da ni ba”

Ya fada yana murmushi kamar yadda nima nake mayar masa da murmushin.

“No haba dai Bismillah”

Na fada ina nuna masa gurin da system din take. Yau kusan kwana biyu kenan a office dina yake aikinsa saboda system din da ke office dinsa ta samu matsala kamar yadda ya fada min.
 
“Yau ma dai kin yi kyau kamar jiya, wai kiye sirrin”

Ya fada yana nufar gurin da System din take yana aje kayan dake hannunsa. Ni kuma sai nai dariya mai sauti.

“Na gode, sirrin aikin kamfaninku ne ka san yana karawa ma'aikatanku kyau da natsuwa”

He was laughing so hard kamar na fadi masa wani abun dariya sosai.

“Oh wow okay zan fadawa mutanen kamfaninku haka kuwa, so that kowa ya rike aikinsa da kyau kar yai laifin da zai saka a koreshi”

Nima dariyar nai.

“Gaskiya ya kamata kam, ko ma an koresu ku makale kar su je”

“Hahaha Haima kenan”

Ya fada yana cigaba da dariyar, wani abu na ji marar dadi ya ratsa zuciyata sakamakon kirana da yai da sunan da Abdulhamid ke kirana da shi. ban sake cewa komai ba na cigaba da aikina, sai jin nai wayata ta yi kara alamar sako, a zato na mtn ne hakan yasa na share wayar ban duba.

GOBE NA (My Future)Where stories live. Discover now