35

1.7K 229 45
                                    

Kasa cewa komai yai  ya tsaya a gurin kamar an dasashi, Sadi kan sai gumi yake hadawa abun ka da marar gaskiya, Murja kuma na can dakinta tana aikin ihu kamar da gaske Aljanun ne suka ziyarce ta har da wani yare take shi ba yarbanci ba, ba kuma iyamuranci ba.

“A kaita asibiti, no gurin malamai”

Fadi ya fada wiki wiki da ido, sai Aminu yai masa murmushi tare da gyada masa kai alamar gamsuwa.

“Za a kaita”

Ya amsa masa sannan ya nufi dakinsa jikinsa babu kwari, saman gadonsa ya zauna sai ya rasa abunda zai fara tunani, korarsa da akai a gurin aiki ko kuma tararda dan'uwansa tare da matarsa? Kwantawa yai saman gadon yana ta kallon silin.

“Aminu ka ji tsoro Allah abunda kake mana baka kyautawa, ka rika tunawa kana da yara kana da mata, ace magidanci kamar idan ya bar gida ba zai dawo ba sai karfe daya ko biyu na dare...?”

“Ke Halima a nan gidana ne ina da yancin shigowa a lokacin da nake so na fita na lokacin da na ke so, ba ki isa ki saka min doka a gidana ba”

“Ba doka nake son saka maka ba, abunda kake yi nake kokarin nuna maka illarsa, duk abunda kai wa matar wani sai an yi ma taka, kuma duk abunda kai wa yar wani sai an yi wa yarka....”

“Idan iskancin kike so ni ban hana ki yi ba, ga ki ga guri har kya fada min wani wai sai an yi ma yar wani matar wani dan baki da hankali”

“Allah ya tsare ni, ban aikata zina ina budurwa ba ba zan aikata da aurena ba, ga hakkin yayana ga na iyayena ga na mijina ga na ubangijina? Wallahi ba zan iya ba”

Ya fada tana share hawayenta sannan ta tashi ta bar masa dakin. Tuna wannan yasa shi share hawayensa ya rumgume hannayensa a kirjinsa. A yau na mallakawa murja komai, ita ke saka masa duk dokar da tai mata, be isa ya kai 9 a waje ba, be isa ya dawo gidan ba tare da saninta ba, amman hakan be hana ta cin amanarsa ba. Abunda be taba mafarki ba, domin a lokacin da zai aureta sai da yai bincike mai karfi aka tabbatar masa da tarbiyarta sannan ya aureta, sannan ya yaba da shigarta da hankalinta shiyasa ya aureta ashe be tsira daga abunda yake gudu ba, kuma ta rasa wanda zata aikata da shi sai dan'uwansa uwa daya uba daya! Wani irin abu yaji ya tsaya masa a kirji ya danne masa numfashi har sai da yai saurin kifewa a saman gadon ya runtse ido sannan ya samu  sassauci.

“Allah yasa ka gane kuskuren da kake aikatawa da wuri, ko dan yaranka..... ”

Maganar Halimatu ta sake dawo masa.

“Na gane Halimatu na gane......”

Ya fada yana fashewa da kuka wasu hawaye masu zafi suna sauko masa. Kamar an tsikare shi sai ya zabura tai saurin tashi zaune. So da gaske Halimatu take da fada masa cewar Sadi yai ma Namra fyade? Sadi ya daka masa wuka har sau biyu kenan? Yayi saurin tashi zaune, ji yai babu wanda yake bukatar gani a yanzu kamar Halimatu da yayanta.

Tashi yai ya fice daga gidan gaba daya, a bakin gate ya samu abun hawa ya fada masa unguwar su Halimatu, kamin su isa duk sai ya tsawalla kamar wanda ya shekara ba ga yaranba. Sai kuma yai rashin sa'a ya tarar bata gidan wai ta tafi dauko yaran daga School. Kai tsaye Scul din ya wuce a can ya sameta ta tana kokarin taron napep tana rike da hannun yaranta. Sai a lokacin yake jin rashin kyautawa ta ya zai barta ita kadai tana daukar responsibility ba yaransa bayan yana raye? Gaba daya sai jikinsa yai sanyi, karasa yai kusa da su, kallo daya tai masa ta dauke kai sai ya koma gaba Namra ya risina ya kai hannu ya shafa fuskarta yana murmushi.

“Daddy ina wuni?”

Kasa amsawa yai sai ya rumgume ta hawaye na sauko masa. Tun yana yi a hankali har ta kai mutane na kallonsa.

“Miye haka? A cikin jama'a muke fa, ka sake ta gida zamu je”

Sakinta yai ya dago kai yana kallon Halimatu wacce ke watsa masa wata uwar harara, kamin ya kai hannu ya shafa kan duka yayansa sannan ya mike tsaye ya share hawayensa, ita kuma taja yaranta sukai gaba, yana tsaye a bakin titin yana kallonsu har suka samu Napep suka shiga suka bar shi a gurin. Shi ma achaba ya hau ya dauki hanyar family house dinsu.
  Ko da be fada ba kana ganinsa kasan yana cikin tsakanin damuwa, kamar yadda mahaifiyarsa ta karanta a fuskarsa. Gashi ya shigo mata har dakin bachinta babu sallama balle gaisuwa.

GOBE NA (My Future)Onde as histórias ganham vida. Descobre agora