42

2.1K 320 190
                                    

Da hannu daya yake tuka motar yayinda dayan hannunsa yake dafe da idonsa, wani zafin bala'i idon yake masa ga ruwan da ake kama da bakin kwarya, har baya iya gani da kyau saboda karfinsu.
A dole ya faka motarsa gafen titi, slowly ya dauke hannunsa daga idon da ke masa wani mugun zugi, ji yai idaniyar ta cika da abu mai kauri shi ba hawaye ba kuma ba ya san jini ne har sai da ya duba hannunsa. Jini a ciki kuma shine yake cika masa idon har baya gani da idon daya.
  Lumshe idanuwan yai duka biyu yana sauraren yadda zugin yake shigar masa har cikin kansa, a rufe da idon ya saka hannun aljihu ya dauko wayarsa sai a lokacin yai kokarin bude idon daya yana duba iPhone dinsa wacce ta gama daukewa dip, sakamakon ruwan da ta sha, ba wayar kadai ba tufafin jikinsa ma sun gama jika seat dinsa balle kuma wayarsa.
Iskar bakinsa ya bushar yanzu be san yadda zai yi ya kira Doc Nura ba balle yaji idan ma yana gari ko yana asibitin ko gida, daman can a tsarinsa be yarda wani likitan ya duba shi ba sai family doc su, domin ya yarda da aikinsa hundred percent.

“Ba ma ita ce mahaukaciyar ba ni ne mahaukacin, taya zan shigar mata fada? Fadan ma da mahaukaci dan'uwanta? Matar da ta kashe min yarinyar? What's is wrong with me?”

Ya fada yana jin haushin abunda ya aika..

“Bata ma tsaya ta dubani ba fa sai kawai ta gudu, idan ma kashe ni zai yi ita dai ta tsira, mahaukaciyar banza i hate her”

Ya sake fada cikin fusata yana cizon bakinsa. A gurin ya tsaya har sai da ruwan suka dauke gaba daya sannan ya karasa tukin zuwa gida kamin ya isa har wani jiri yake ji cikin kansa.

“Ai I'm human being be kamata ina gani ayi kisan kai ba, shiyasa na taimake ta, amman yanzu na gano matar nan bakincikina take so take ta illatani bayan ta kashe min ya, be m kamata na barta tana aiki a kamfani na ba ai”

Shi kadai yake ta magana da kansa har ya faka motarsa a harabar gidan, yana kokarin bude motar ya fita ya tambayi kansa.

“Ko ma miya kai ni fada da mahaukaci? Da mahaukaci da mahaukaciya suna fada ni mai hankali miya kai ni ciki?”

After ya fito daga motar ya bawa kansa amsa.

“Kaddara.... ”

Part dinsa ya wuce, yana shiga ya fara ziyartar bandakin ya wanke fuskarsa, ya saka tissue yana tare jinin a hankali sannan ya dawo dakinsa ya dauko dayar wayarsa da ke gida yana kokarin kiran Doc Nura.

“Hasara nawa ga saka ni a yau? Ta saka na jika tufafina ga idona daya ga phone dina.....”

Wani irin haushinta ne ya kara cika msa zuciya. Sai da ya tabbatar Doc Nura na aibitin sannan ya canj tufafin jikinsa ya dauko key din wata motar ya fice ba tare da ya leka part din Hajiya ba, domin baya son ya tashi hankalinta.

A asibiti babu kalar dariyar da Doc Nura be msa ba.

“To kai yanzu miya kaika raba fada da mahaukaci? Ai gashi an bak tukuici”

“You make me hate her more”

“Wai wacece wannan?”

“Wata mahaukaciya ce mai ruwan masu hankali”

Ya hada fuska babu annuri can kuma yai murmushi.

“Ita ma fa taji wuya, ba da wasa ya moreta ba”

Dadi yaji tun da ita ma ta ji wuya, but maganar Allah shi yafi kowa shan wuya tunda shi be shi yaja mahaukacin ba.
Bayan Doc ya duba idon ya bashi maganin na sha da shafawa a idon ya kuma fada msa yadda zai kula da ido. After ya dawo gida ya kira shiga part dinsa ya kiran Yunus.

“Yu akwai wani mahaukaci da ke kusa da kamfanin mu, daga hannun dama gurin wani shagon kwano, za ka iya gane shi?”

Sai da Yunus yai tunani sosai sannan ya amsa masa da.

GOBE NA (My Future)Where stories live. Discover now