40

1.9K 322 156
                                    

Hakan nan yau yake sha'awar zuwa gurin aiki da wuri, daman kuma ya tashi ya ji jikinsa sai a hankali so yana bukatar yai aiki da wuri ya dawo gida if possible. And he like to wear a suit today like always sai dai wani lokacin yana saka shadda dan yafi jinsa more comfortable fiye da suit.
  Bayan ya gama shiryawa ya shigo bangaren Hajiyarsa still ya same ta tana aikin hada masa breakfast sai dai yau ba ita kadai ba har da Siyama. As he already knows siyama bata tashi da wuri sai idan makaranta zata je, amman ga a kitchen tare da Hajiyarsa da mai aikinsu har ma da cousin dinsa Khadija wacce kwararriyar banker baker ce. 

“Yau me kuka hadawa haka ne?”

Da sauri dukansu suka juya suka kalleshi domin ba su san da zuwansa ba sai ganinsa da kai a kofar kitchen yana ta kamshin turare.

“Amman Bro you wake early”

Cewar Siyama tana nufo inda yake. Agogon hannunsa ya duba wanda ya nuna masa bakwai da yan mintuna.

“Yeah ina son naje aiki da wuri ne”

“Oh bro i wanted to surprise you.....”

Ta fada tana bata fuska, sai Khadija ta tari numfashinta tana murmushi.

“We can still surprised him dear... ”

Ya kalli Khadija da fuskar rashin fahimta. Sai ta jango masa kujerar kitchen din ta aje bayansa.

“Dan zauna”

Be zauna ba be kuma nuna alamar zai zauna din ba balle har ya furta wani abu. Siyama know him well, he is no nonsense at all, hakan yasa ta hade hannayenta.

“Pls”

Sai da ya kalli Hajiyarsa wace ita ma tai masa alama da ya zauna din sannan ya zauna yana binsu da kallo. Da gudu Khadija da Siyama suka fita daga kitchen din, like 6 minutes suka dawo sai Hajiya ya fita.

“Close your eyes pls”

Be musa ba tunda Siyama ce tai masa maganar, a take ya rufe idon sai ta kama hannunsa yana masa jagora a hankali har suka fita daga kitchen din, gaban dinning area ta nufa shi sannan ta saki hannunsa.

“Now open your eyes....”

A hankali ya bude idon, by surprise yai arba da katon birthday cake mai hotonsa.

“Wow”

Ya furta yana kallon mahaifiyarsa da ke Murmushi kamin ya rumgumi Siyama wacce ke ce masa happy birthday.

“Thank you Blood, Thank you Mom, thanks Sis”

Ya fadawa Siyama Hajiya and Khadija wacce tai masa respond da murmushi.

“So duk kun san yau birthday na kenan, ni na manta sam”

“Taya za ayi na manta ranar da na maifi Ahmad Gwarzo...”

Cewar Hajiya tana murmushi, sai yai murmushi ya kai hannunsa ya debi cake din ya kaiwa Hajiya a baki.

“I love you Hajiya ta”

One after the other ya bisu ya saka musu cake din a baki har Khadija, sannan suma suka ba shi, daga bisani Siyama ta ciko hannunta da cake din zata shafa masa sai yai saurin rike mata hannu ya murda har sai da ta kai kasa tana ihu.

“Wayyo Hajiya....”

“Gwarzo karka kare min ya”

“Hajiya ba zan bari ta bata min tufafi ba today is special day for me...”

Sai duk suka saka dariya har ita Siyamar sannan ya sake ta ya dauki tissue ya goge hannunsa.

“Yau din nan ko? I very very special day for us, i call your friend on phone and i told him ya saka kowa yai surprise dinka da wani abu each and every person a kamfaninka, so karkaje ka dinga musu fada ni na saka su”

GOBE NA (My Future)Donde viven las historias. Descúbrelo ahora