22

1.6K 208 22
                                    


Gaba daya littafin nan Sadaukarwar ne ga Zainab A Baba💖

AHMAD POV.

Wayarsa ce tai ringing, da gangan ya ki duba wayar ya ga mai kiran balle yai deciding idan zai dauka ko ba zai yi picking ba. Babu kira mai muhimman a gurinsa kamar na Hajiyarsa sai kuma na kanwarsa da yarsa su ne kadai mutanen da suke da muhimmanci fiye da komai a rayuwarsa, yana girmama kiransu yana mutunta bukatunsu, kamar yadda yake martaba su. As long as yana tare da Hajiya ko yana cikin gida, duk wanda ya kira shi sai idan yaga dama zai daga kiransa kowa shi a duniyar nan kuwa.

“Ba wayarka ce ke ringing ba?”

Cewar Hajiya ganin be daga ba duk kuwa da ta san halinsa na kin son call, ya fi son sako fiye da kira.

“Ita ce wata kila wane ni bana son amsawa yanzu”

“Ko dai yan matan ne ke kira?”

Kallonta yai da murmushi a fuskarsa.

“Kowa da bukin zuciyarsa, Allah na tuba wace mace ce zata wahalar da kanta yanzu na son dan Hajiya?”

“Hmmm ai yan matan yanzu shegen wayo ne da su, yanzu sai su tatse ka tass baka sani ba”

“Hajiyata, kin kasa gane cewar ni ba yaro ba ne, ka ci abinci? Me ka ci? Yaushe zaka dawo, karka wuce minti talatin a waje, da sauransu na yara ne, Hajiya ni babban mutum ne a yanzu tun da har Daddy ya kirani nai min wasiyar kula da ku, kuma cikin ikon Allah da iyawarsa na iya rike gidan nan da kula da ku da tafiyar da komai na kamfani yadda ya dace ya kamata ace kin fahimci cewar dan ki ba yaro ba ne a yanzu”

Murmushi tai Murmushi mai sautin irin na su na manya.

“Har gobe kai yaro ne Gwarzo, maza ai ba wayo ne da ku ba, ba komai kuke ganewa ba sai na nuna muku”

Ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya kalli Baby Namra.

“My Love je ki dakinki bari mu yi magana da Hajiyarki ko?”

“Okay Daddy”

Sai da ta sumbanci kumatunsa sannan ta haye sama, shi kuma ya bita kallo kamin ya ciro wayar tasa da ke ringing yai picking.

“Yusuf ya akai?”

“Lafiya kalau, oga ya gida ya family?”
   
Fine go straight to the point

Oga maganar vip ne”

“No ya dai kusa ka san kace baka son sai abu yai gab a fada maka, shiyasa na tuna maka”

“I think kudin shekara ya kamata mu fara biya na wata wata nan yana confusing dina, ka lissafa na shekara nawa ya kama zan turawa abokina number ka sai ku yi magana”

Be jira Yusuf din da ya kira wayar ya kashe ba, balle har ya saurare abunda zai fada ya kashe wayar, yana kallon Hajiyarsa zai yi magana ta tari numfashinsa.

“Har yanzu ba a daina biya Vip din nan ba? Shekara nawa Gwarzo? A yanzu ka gama maganar cewar ka girma, ni nasan abunda na ke ai na san waye kai”

“Ba haka ba ne Hajiya, abunda kika kasa ganewa freedom din danki,  Hajiya kin kasa bari na yi komai kamar ko wane namiji, kin ki aminta na zauna a gidan kaina, kin hana auren duk yarinyar na kawo, ko fita nai idan na wuce ka'idar da kika ba ni sai kin nuna bacin ranki ko kuma ki nuna min hankalinki ya tashi ba ki san inda na ke ba, duk yadda nake son na fita na fira a waje na wuce 9 ko na kai 10pm sai ki ce min ba haka ba.

Exclusive City, a nan na hadu da Halima, a kujerar da nake biya a yanzu a gurin na same ta zauna, kin sani Hajiya every week muna zuwa gurin mu sha iska, and ta taba fada min ita take biyan gurin ko da bata zo ba, and after mun yi aure ita ta cigaba da biyan gurin, duk yadda na so na cigaba da biya sai ta hana ni, she once told me na bari sai idan bata da rayuwa sannan na cigaba da biya, and nai mata alkawari daga lokacin da na auri wata macen ba zan sake biya ba, alkawarinta nake kokarin cikawa Hajiya gurin nan yana da muhimmanci a gareni saboda mahaifiyar Namra, ko rai aka bata mata a gurin take zuwa tai kuka, idan kika mata wani abun a gurin take zuwa ta zauna tai bacin ranta ta gama sannan ta kira tace idan na taso daga office na biyo ta nan na dauke ta, wani lokacin kuma da kaina nake zuwa nemanta a gurin, ni kaina a yanzu ko anjima ko wani lokaci na kan je can na zauna kuma na samu natsuwa kamar tana raye... ”

GOBE NA (My Future)Where stories live. Discover now