“Ki yi bachi ki more”

Juyowa nai da sauri da zimmar nai masa magana sai bakina ya gogi nasa numfashina ya gauraya da nasa, babu abunda yake kallo sai bakin nawa.

“Talk”

Ya fada bakinsa na gugar nawa, a dole nima a haka nai masa magana bakina da nasa na gogar juna.

“Ina son naje nima ai”

“So kike mu je can mu taru mu lalace? No za ki tsaya a nan ki huta kamar yadda Hajiya tace idan sun ba ni gado bayan kin huta zan aiko a dauke ki, kuma zan siyo miki sabon line da zaki rika amfani da shi a nan so that ki kira Mama ki sanar mata mun iso”

Ya karasa tare da kissing dina sannan ya daga ni ya nufi akwatinsa ya rufe ya dauki abubuwan bukata ya saka aljihu,sai kuma ya sake nufo ni da kansa ya dago ni ya rumgume ni ya sake kissing dina sannan ya fita tana dago min hannu. Da kallo na bishi har ya fice ina mamakin hali da dabi'unsa idan aka fada maka Ahmad zai iya zanzarewa yai haka saka rantse da Allah karya ne kace ba zai aikata ba, ni a rayuwata ma ban taba auren namiji marar kunya kamar Ahmad ba, shi komai nasa kirkiri yake kuma da gasken gaskiya to wa ma zai ganshi yace shi aka kawo jinya?
Fitarsa da kamar minti bakwai aka kwankwasa kofar dakin
Tashi nai jikina nata kamshin turarensa na dauki rigata na saka sannan naje na bude, wata farar mace na gani dauke da tray din abinci ta miko min, sai na rufe dakin na juyo na dawo, burger burger and snacks sai drink da safafen kwai, ban kula abinba na nufi bandaki da murmushin daya kasa bari kumatuna, wanka nai sannan nai alwala na fito har lokacin murmushi nake ina jin wani irin shaukin kaunarsa a raina. Haka na bi na rama ko wace sallah sannan bude abunda aka kawo na ci wanda zan iya ci na bi lafiyar gado na kwanta bachi son raina nai ta bachi kamar dan ni kadai akai bachin.

Ban farka ba sai kusan la'asar shima kuma bugun kofar dakin ne ya tashe ni wannan karon wata makar mace ce mai zubin yarbawa ta kawo min tuwo da miyar taushe ga namomi a ciki na yi mamaki sosai ashe a acan ma ana samun irin abincin mu, sai da muka gaisa da ita na karba tana tambayar daga wani garin na zo nan.

“Gasau Zamfara”

Sai ta amsa min da ta san garin sannan tai min sallama ta tafi, duk da ban ji kiran sallah ba dana duba agogona ya nuna min hudu har da wani abu a lokacin, hanzarin shiga bandakin nai na yi alwala ya fito nai sallah sannan na ci abincin na koshi na sha ruwa na sake bin lafiyar gado na kwanta na cigaba da bachina.
Dana auna lokacin magariba yayi sai na tashi nai sallah sannan na jira isha'i itama nai, ina ta jiran Ahmad ya aiko a dauke ni be aiko ba har dare ya soma misalin tara matar nan ta sake kwamkwaso dakina ta kawo min doya da miya, ina ci ina lumshe ido domin doyar ta yi laushi sosai ga dan zaki zaki kana aji kadan wata kila sun saka madara ne dan alamu ya nuna haka yadda doyar tai fari.

  ‘To fa komai a nan banza ne, ko a nigeria da rayuwa take da tsada ai wasu na kan yi doya da madara da miya balle a nan da komai yake banza’

Na fada a raina ina ta kara auna doyar da miyar kifi, bayan na gama cin abincin ina kokarin kwantawa sai na ji an buga kofar, da kuzarina na nufi kofar ya bude, sai nai arba da Hajiya tana sanye da riga da wando sai karuwar rigar sanyin data dora sama kamar ba ita da dankwalin da tai rolling kanta da shi har da su gilas, kasa nai da kaina na gaisheta ta amsa min tana cire madubin idon sannan na bata hanya ta shigo ciki.

“Za mu je da ke can gurin Gwarzo ne”

“Jikin nasa da sauki ko?”

“Da sauki sosai ba su dai ba su dai babu wani result ba amman kana ganinsa ai kasan da sauki kan dan yace ya daina jin komai yanxu, ina jin dai har da addu'ar nan da muka hada masa da rubutu, kin san wani lokacin iska ma suna haka fa”

“Haka ne Hajiya Allah ya kara lafiya”

“Amin ki saka rigar sanyinki mu tafi”

Na mike na dauko rigar sanyin da Ahmad ya saka min na dora saman doguwar rigata sannan na dauki mayafin abayar na rufe kaina muka fita tare da Hajiya. Taxi muka shiga amman kamar wandanda suke a cikin motar gida haka muke a cikin taxin, ni kam bana aikim komai sai kallo ashe garin ya fi kyau da dare ko'ina haske ne ga mayan allunan talla kala kala har da na jaruman india.

GOBE NA (My Future)Where stories live. Discover now