MATAR DATTIJO page 55

970 37 0
                                    

💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋

*©jeeddah Tijjani*
           *Adam*
*(jeeddahtulkhair)*

*follow me on instagram @jeeddahtijjani*

55

Kai tsaye gidan su Hajiya maryam ya nufa, a bakin kofa ya tsaya ya aika yaro a sanar musu cewa ya iso, da fara'a mahaifinta ya fito ya tarbe shi tare suka shiga har cikin gida, yana shiga ya tarar har an yi masa Shimfida ana jiran isowarsa.

A ladabce suka gaisa da babanta bayan sun dan yi hira ya dubi dattijo, nasan baxa kayi mamakin kiran da nayi maka ba Alhaji, domin tatsuniyar gixo bata wuce ta koki, murmushi dattijo yayi tare da cewa gaskiya ne baba.

Gyara xama yayi sannan ya fara yi masa magana, abu na farko da xan fara cewa shi ne Allah ya baka hakuri Allah ya huci xuciyarka domin xama da Maryam sai an kai xuciya nesa, kayi namijin kokari da har ku ka kai wannan lokacin tare ba tare da kun rabu ba, bana bukatar jin musabbabin abinda ya janyo rabuwar ku domin nasan duk laifin daga wajenta yake, don haka ina kara baka hakuri Allah ya huci xuciyarka, sannan baxan maka dole a kan ka dawo da ita ba, idan kaga akwai matsala kuma xaka fi samun kwanciyar hankali to ka bar mayar da ita.

Duk kunya sai ta kama dattijo ganin yadda mahaifinta yake fadar laifinta da kansa, kansa a sunkuye ya bashi amsa, ina nan ina tunani a kan haka indai ta gyara halinta ba komai sai mu cigaba da xama dama ai sulhu nake so a yi. Cike da farin ciki ya dube shi gaskiya ne Alhaji to idan da alkhairi Allah ya dai-daita, amsawa yayi da ameen suka yi sallama.

Kwance Hajiya maryam take tana tuna irin rayuwar jin dadin da ta yi a gidan dattijo, addua ta fara yi a kan Allah ya gyara tsakaninta da mijinta ta koma dakinta yanzu ta gane muhimmancin da mijinta yake da shi, da duk bata ganin amfaninsa.

Bayan tayi wanka ta shirya ta saka hijabi don yanzu sam ba tada nutsuwar da xata tsaya ta gyara sosai, gidan abokin dattijo ta nufa tunda dama matarsa kawarta ce.

Tana isa bakin kofar gidan hawaye suka cika idanunta, ji take dama ita ma ta koma dakin mijinta ta rika cin gashin kanta kamar kowace mace, da kuka ta shiga gidan hankalinta a tashe ta fara tambayarta dalilin kukanta daki suka shiga saboda kada yara su fahimci halin da take ciki.

Suna shiga ta kara rushewa da kuka, zayyana mata yadda suka yi da dattijo tayi, ta tausaya mata sannan tayi mata nasiha sosai a kan irin abubuwan da take yi masa, ita kanta ta dade tana bata shawarwari a kan ta nutsu ta kama mijinta, wayar maigidanta ta kira ta shaida masa cewa yayi bakuwa, saboda idan ta fada masa kai tsaye cewa ita ce taxo baxai xo ba, saboda shi ma ta taba ci masa mutunci a kan Niimatullah.

Basu dade da yin waya ba ya iso gidan, yana yin ido biyu da Hajiya maryam ya bata rai, fuskarsa ba annuri ya karaso inda suke tare da cewa, kika ce nayi bakuwa ina bakuwar take? Jikinta a sanyaye ta nuna Hajiya maryam.

Fuskar shi a daure ya fara magana dama a kan wannan matar da bata san mutunci ba xaki dakko ni daga wajen aikina? amma baki kyauta min ba wallahi saboda tuni na fita daga shaaninta tunda naga bata san mutunci ba, a fusace ya fita ya bar dakin, bin sa tayi tana bashi hakuri a kan ya dawo amma kememe yaki dawowa.

Ba karamin xafi duniya tayi mata ba, duk inda take tunanin xata ra6a ta samu alfarma a bawa dattijo hakuri ta ci musu mutunci duk a kan auren Niimatullah, da kuka ta fito daga gidan.

Bayan ta koma gida ta kira wayar Niimatullah domin ta bata hakuri a bisa abubuwan da ta rika yi mata a baya.
sai duk kiran da tayi bata samu ta dauka ba, wannan abin ya kara jefeta a cikin damuwa.

Cikin kankanin lokaci ta canja tayi baki ta rame ga damuwar da take fuskanta na rashin muhalli mai kyau da abinci mai kyau, sannan ba damar tayi kuskure sai mahaifiyarta ta hau yi mata fada da gorin abincin da take ci, wannan dalilin ya kara sawa taji duk xaman gidan ya isheta ta kosa ta koma dakinta.

*follow me on wattpad @jeeddahtulkhaeer Tijj*

*jeeddahtulkhair😘*

MATAR DATTIJO CompleteWhere stories live. Discover now