MATAR DATTIJO page 30

1.7K 75 1
                                    

💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋

*©jeeddah Tijjani*
          *Adam*
*(jeeddahtulkhair)*

*follow me on instagram @jeeddahtijjani*

*masu kaeatu wanda ku ka an turo daxu mistake aka yi wannan shi ne original*

*dedicated to Aminiyata masoyiyata abokiyar shawarata, kuma abokiyar fadana Maijidda Bello Allah ya bar mu tare*

30

Washe gari da safe da wuri na tashi na kintsa kaina na gyara dakina, yau kwanana biyar kenan a gidan dattijo wannan dalilin yasa na shiga kitchen don na dafa mana abincin da xa muyi breakfast da shi, haddiyar atamfa na sanya,ba karamin karbata tayi ba,kaina ba dan kwali sai gashina da ya xubo har gadon baya, cike da nutsuwa na karaso wajen shi, cikin salon jan hankali na dube shi, dattijona tashi na hada mana abinci, murmushi yayi tare da miko min hannunsa na mikar da shi tsaye, jan hannun shi nayi har muka isa bakin dining,abincin na shiga bashi muna ci muna hira mai debe mana kewa bayan mun kammala na sake yin wani wankan sannan na dawo jikinsa na kwanta romancing muka cigaba da yi saboda na lura ba karamin debe masa kewa yake yi ba, yau gaba daya bai fita ba abinda ya rika yi da ni kenan ni kuma ban nuna gaxawata ba saboda nasan mijina yana da matukar hakuri da juriya.

Hajiya maryam ce zaune cikin falo, jingine take da kujera sai faman
kada kafa take yi da alama zuciyarta a kusa take, don kallo daya xaka yi mata kasan tana cikin bacin rai, yaron ta munir ne yazo zai shiga dakin shi.

kiran sunan shi tayi, munir xo nan ina son magana da kai, cike da ladabi ya dawo ya tsugunnah tare da cewa gani momy, tambayar shi ta fara yi.

dadynku ya fita ne ko yana nan, cike da nutsuwa ya bata amsa, Aa momy yana nan, tun safe da ya fito ya koma bai kuma fitowa ba, tsaki tayi agogon wayarta ta duba karfe biyar saura na yamma, cike da kulawa yake tambayarta, me yake faruwa momy, a takaice ta amsa masa da ba komai.

fita tayi ta nufi sashin Niimatullah cike da bala'i da gadara take bugun kofar, gami da masifa daga yin aure yau kwana biyar amma har wannan yar iskar yarinyar ta fara juya masa tunani, xai fara juya min baya dama wannan soyayyar da yake mata ai ba banxa ba, da gani asiri ne,  yanxu a ce muna gida daya amma baxan rika saka shi a idona ba, lallai da sake, da karfinta take bugun kofar.

A firgice na tashi daga baccin da nake yi saboda bugun da take yi, da saurina na fito parlour don ganewa idanuna abinda ke faruwa.

zaune na tarar da dattijona, sanye yake da singlet da boxer tarar dashi nayi yana ta faman danna computer da alama bai ma san ana yin bugun ba, a hankali na karasa wajensa tare da dafa kafadarsa, dattijona baka ji ana buga kofa bane? a hankali ya dube ni wlh na shagala da aiki ban ji ba, da sauri na nufi bakin kofar don budewa addu'a nake yi Allah dai yasa innah da baba ne suka kawo min xiyara. tare da dattijona, muka nufi kofar ya fara kokarin budewa.

Abokiyar zamana muka gani tsaye tana huci kamar wata macijiya, dattijjo ne yayi karfin halin yi mata magana.

madam lafiya dai ko, ya yara? tsaki tayi tare da galla masa wata uwar harara, cike da ladabi na tsugunnah na gaidata, cike da tsawa ta amsa min da ban wuni ba kya ganni, shegiyar yarinya gaki karama sai uban iyayi kin mallake min miji, kin raba ni da shi, bari kiji na gaya miki duk irin kulle-kullen da ku ke yi ke da iyayanki har kika yi sanadin aure min miji na san shi, kuma wallahi da sannu xan yi maganin ki, juyawa tayi kan dattijo tana masifa.

kai kuma kaji kunya tsohon banxa ka rasa wadda xaka aura sai yarinya karama, wacce ko yayanka sun girmeta, dan tsabar abin kunya ni wallahi kunya kake bani, dubi irin shigar da take jikinta saboda tsabar karuwanci, sai a lokacin na lura da kayan da ke jikina sleeping dress ne riga da wando.

kallona tayi sannan ta saki tsaki saboda wanan abar ne yasa yau baka fito kaga yaranka ba, alhalin dukkan su suna da muradin ganinka, shi yasa tun tuni na hana ka auro dangin asiri saboda nasan abinda xai faru kenan, wallahi ni wannan ko yar aiki bazan dauke ta ba, don baxan xauna da kaxama ba.

cikin fushi ya fara yi mata magana, dakata Maryam na gaji da irin wanan rashin kirkin da kike min, kuma wannan da kika raina tafi min ke sau dari tunda bata daga murya sama da ta mijinta, bata aibata ni, kuma bata gaza wajen kula da ni, da  yi min biyayar aure ba, gaba daya na rasa inda hankalin ki da tunanin ki yake, a ce yarinyar da kika haifa a cikin ki da ita xaki xauna kina fada ki mayar da ita abokiyar gabar ki, saboda kawai kina hassadar cewa ta fiki iya kula da miji da tarairayarsa, fita ki bar min sashina kafin na bata miki ran ki, tun farko ke kiya yi watsi da damar ki, da baki san abinda ya dace da rayuwar ki ba, tunda ba xaman lafiya ne xai rika kawo ki ba kada ki sake xuwa nan. mayar da kofar yayi ya kulle sannan yaja hannuna muka shiga daki.

Da dukkan alamu ran shi ya baci da abinda Hajiya tayi masa rarrashinsa na shiga yi ina kwantar masa da hankali, cike da kulawa ya dube ni, ba komai my Niimatullah komai ya wuce, nasan indai ina da ke baxan taba yin bakin ciki ba.

cike da soyayya ya kamo ni ya rungume ni, tashi mu tafi mu sha ice cream Amaryar dattijo, daki na shiga na sanya bakar doguwar riga, nayi kyau sosai sannan muka kama hanya muka tafi, sai da xuciyar mu tayi sanyi muka sha soyayya muka manta abinda matar Alhaji tayi mana sannan muka dawo gida.

kirjinsa na fada saboda na dan gaji da yawa, shafa bayana yayi, Niimatullah kinga irin abinda nake fada miki na rasa    a rayuwata ko, shi yasa na shigo da ke cikin rayuwata ki fara bani kulawa.

cike da shagwaba na shafo fuskarsa, xan kula da kai Hubbyna, shi yasa ma a yau nake son wannan daren ya xama daren da xan faranta maka, da sauri ya dube ni da gaske kike Niimatullah ko kuma irin ta ran nan xaki min?
cikin kulawa na dube shi wlh babu wasa a maganata babyna.

cike da farin ciki ya rungume ni sungumata yayi cak kamar wata yar baby sai toilet muka yi wanka tare da alwala, bayan mun fito muka gabatar da sallah irin ta ma’aurata da kanshi ya chanza min kaya, Ina dan nokewa saboda kunya da kuma nauyin dattijona shima kayan ya chanza ya feshi mu da turare ya bare sweet yasa min a bakina, cikin salon soyayya ya fara tsotsan bakina yana neman sweet din da ya sanya min.

cikin natsuwa da kwarewa ya fara romancing dina shafa ni ya rika yi ta ko'ina, daga nan ya dauke ni ya dire ni a kan gado, Ya kai minti talatin dattijo yana romancing dina duk ya fita a hayyacinsa jikinsa har rawa yake, har da yar kwallarsa,  chan ya bude qafafuna ya daura bakinsa a kan clitoris dina tuni na fara hawa network har da su kukan dadi sai da nayi releasing sau biyu sannan dattijona ya Zare bakinsa, kukan da nayi lokacin da nayi releasing ba qaramin tada hankalin dattijo yayi ba,” da sauri da sauri yake karanto min addu’ar Saduwa da iyali tuni idona ya fara raina fata a  hankali ya fara bi da ni, chan daya shige ni wani irin razannanen kara na saki Wanda a lokacin dattijona ya mance da wacce yake tare, yin abin sa kawai yake idan a  ka yi la’akari da dadewar da yayi na rashin samun kulawa,Please karki fita daga rayuwata Niimatullah ke haske ce a duniyata, sai a kanki na kara  tabbatar da meye aure, na kuma  kara sanin  yadda dad'in mace yake, Niimatullah kina da dad'i ga ni'ima, ke din  ta daban ce, wallahi bazan iya rayuwa babu ke ba, ban san dad'in sex ya kai haka ba sai a kanki, ban san haka mace ke da ni'ima da dad'i ba sai a kanki, wallahi bazan iya rabuwa dake ba,  idan kika bar ni zan fad'a halakar neman mata,wayyyyyo dad'iiiiiiii, ihu da gurnani tare da sambatunsa, iri iri dattijo ya dinga yi ...........

*follow me on wattpad @jeeddahtulkheer Tijj*

*jeeddahtulkhair😘*

MATAR DATTIJO CompleteWhere stories live. Discover now