MATAR DATTIJO page 47

1.3K 49 0
                                    

*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋

*©Jeeddah Tijjani*
           *Adam*
*(jeeddahtulkhair)*

*dedicated to Amrat makeover*

47

Kaina a sunkuye yake har muka isa bakin wani gida da ke unguwar hotoro, gidan ya hadu iya haduwa, amma da dukkan alamu gidan xaman mutum daya ne, key yasa ya bude mana gidan rike yake da hannuna har muka isa cikin gidan cigaba da bubbude kofofin gidan yayi, cike da mamaki nake tambayarsa, nan kuma gidan wane ne dattijona? murmushi yayi yana kallona nan ma gidana ne xuwa nayi mu shakata mu huta sannan mu koma, makale kafada nayi ina masa shagwaba, ni dai bana so mu dade dan Allah ka taimaka ka mayar da ni da wuri.kallona kawai yayi tare da jan hannuna muka shige parlour, a kan kujera ya xaunar da ni,tsayawa nayi ina karewa dakin kallo.

Komai na gidan a gyare yake kamar da mutane a ciki, rausayar da kaina nayi ina tambayarsa dattijona ya naga komai na gidan nan tsaf, kamar da akwai mutanen da ke rayuwa a cikinsa?kallona yayi tare da kanne min ido daya cike da xaulaya yake min magana, wata amaryar tawa ce a ciki, abinda yasa kika ga na kawo ki ta tafi xiyarar ganin gida ne.

Wani kishi ne ya taso min naji kamar na buge bakinsa a lokacin da yake fada min,bata fuska nayi ina masa magana, dama kana da wata matar bayan ni da maman munir gaskiya ka yaudare mu dattijo, me yasa xaka yi mana haka? nan da nan idanuna suka kawo ruwa hawaye ya rika xubo min ta ko'ina.

A hankali ya miko hannun shi ya dora bisa wuyana cike da rarrashi ya fara min magana kiyi hakuri tsokanar ki nake yi Niimatullah uwar kishi, ai daga ke ba kari amaryar dattijo kin min komai kuma kin wadace ni, babu gurin da xan je na samu nutsuwa idan ba naki ba.

ba karamin dadi kalamansa suka yi min ba, cike da shagwaba na dube shi.

Har ka bata min rai dattijona kasan bana son wata mace ta shiga xuciyarka idan ba ni ba,tallafo fuskata yayi yana sumbatata,babu mai shiga xuciyata idan ba ke ba Niimatullah ke kadai kike burge ni duk cikin mata.

Kwantar da kaina ni yayi a jikinsa har cikin raina nake jin wani dadi na ratsa xuciyata, hira muka cigaba da yi cikin nishadi bayan mun huta muka shiga toilet muka yi wanka, muna fitowa ya fara bina da fitinannen kallon shi,ko ban fada muku ba kun san abinda dattijona ke so, bayan mun kammala mun dawo cikin nutsuwar mu muka sake sabon wanka, sannan muka nufi restaurant don cin abinci.

*****

Hajiya Maryam ce tsaye a bakin kofar shiga falonta, sanye take da doguwar riga ta atamfa ta nade kanta da mayafi, da dukkan alamu daga unguwa da ta dawo, cikin sassanyar murya ta kwalawa danta munir kira wanda yake daki yana karatu, da hanxari ya karaso wajenta cike da ladabi yake mata sannu da dawowa, mika masa kayan da ke hannunta tayi tare da cewa shigar min da su ciki saura kuma ka tsaya bincikawa kaga abinda ke ciki,karba yayi ba tare da yace komai ba ita kuma ta bi bayansa.

Fadawa kan kujera tayi ta xauna duk ranta babu dadi ta rasa ina xata saka ranta saboda mijinta ya juya mata baya, tayi duk abinda xa tayi amma kullum dada karkata yake yi wajen kucakar yarinyar da ya auro mata, mugun tunani ne ya rika bijiro mata, a cikin xuciyarta ta fara tunanin hanyar da xata bi ta kwato yancinta.

Munir ne ya lura da halin damuwar da take ciki, a hankali ya karaso kusa da mahaifiyar tasa cike da nutsuwa ya fara yi mata magana.

Mama lafiya naga kwana biyu bakya cikin walwala, ko bakya jin dadin jikin ki ne?a hankali ta dube shi da farko kamar baxa tayi masa magana ba, sai kuma can bayan yan mintuna ta amsa masa da lafiyata kalau, amma wannan uban naka yana son gadar min da hawan jini da ciwon xuciya.

Bai ji dadin maganar da ta fadawa babansa ba, amma ya daure ya cigaba da yi mata magana, kiyi hakuri mama rayuwar aure yar hakuri ce,kuma komai na duniya sai an yi hakuri, wata rana sai kiga komai ya xama tarihi.

MATAR DATTIJO CompleteWhere stories live. Discover now