MATAR DATTIJO page 48

833 15 0
                                    

💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋

*©jeeddah Tijjani*
          *Adam*
*(jeeddahtulkhair)*

*Follow me on instagram @jeeddahtijjani*

*dedicated to Suhaimah M Bello*

48

Muryar dan shi munir yaji wani sanyi yaji a ransa, saboda yayi missing yayan nasa yana son kasancewa da su amma halin uwar su yasa ya bar su, cike da ladabi yake masa magana tare da gaishe shi, murmushi naga yana yi sai abin ya bani mamaki, ganin yadda yake magana yana fara'a ne yasa na gane ba Hajiya maryam bace, cike da walwala suka kammala wayar ya dawo da kallonsa gare ni, matsowa yayi daf da ni tare da kwantar da kansa a jikina,cike da xaulaya yake min magana nasan har hankalin ki ya tashi ko amaryar dattijo kin xaci ogarki ce ta kira? Murmushi nayi ni hankalina bai tashi ba don ta kiraka, xan fi so a ce ta dawo hanya madai-daiciya don ta samu yardar mijinta, wannan rashin xaman lafiyar gaba daya bana jin dadinsa, kwanto da ni yayi yana min kallon kauna.

Hankalin ki yana burge ni Niimatullah idan kika yi wani abin kamar babba ce tayi, kina da hangen nesa kuma ba ki da kyashi, duk da cutarwar da maryam ke yi miki amma kina so ta dai-daita da ni, gaskiya kin cika mace ta gari Allah yayi miki albarka, kaina a sunkuye na amsa masa da ameen.

Dago fuskata yayi yana kallona, kin son da wa muka yi waya yanxu? Girgixa kaina nayi sannan na amsa masa da a'a, gyaran murya yayi sannan ya fara yi min magana, munir ne ya kira ni yake bani hakuri a kan abubuwan da suke faruwa, kuma ya roki na koma gida amma ni gaskiya baxan koma ba sai na huta sosai da matata.

Kamo hannun shi nayi na rike kayi hakuri mu koma dattijona kaga kada a shiga hakkinta da yayanta, kuma kaga danta ma baya goyon bayan abinda take yi, tunda har ya shigo maganar ya kamata ka koma gida ko a yanxu nasan ta gane kuskurenta, murmushi yayi lallai har yanxu baki san wacece maryam ba Niimatullah shi yasa kike fadar haka, wallahi ina tabbatar miki baxa ta fasa abinda take yi ba, ni fa nasan halin kayana.

Sauke ajiyar xuciya nayi, duk abinda xata yi mana ya kamata ka rika hakuri dattijona tunda kaine shugaban gidan kai xaka tsara abinda xai fi xama daidai a gidanka, a ganina tahowar da muka yi nan baxai xama maslaha ga xamantakewar mu ba sai dai ma ta kara tsanata saboda tunani xa tayi na mallake ka na janye ra'ayinka.

Shafa kaina yayi xan yi naxarin maganarki amaryata, hira muka yi sannan na raka shi ya shirya ya tafi office, bai fi 2hours da tafiya ba ya dawo, cike da mamaki nake tambayarsa.

Me kuma ya dawo da kai dattijona, marairaicewa yayi yana kallona ba tare da yayi min magana ba, karasowa yayi ya narke a jikina cike da tausayawa na dube shi,me yake damunka mijina? rausayar da kai yayi sannan yayi min magana, soyayyarki ce ta dawo da ni har na fara aiki na gudo na taho wajenki, Allah ya sani bana koshi da soyayyarki amaryata, bata fuska nayi xan yi kuka.

Dan Allah kayi hakuri dattijona yau a gajiye nake kaga nayi maka aiki da yawa jiya ka taimaka ka kyale ni yau na huta, jawo ni jikinsa yayi ki taimaka min amaryata kin san da cewa a wajenki kawai nake samun nutsuwa, duk hakurin da na bashi bai karba ba sai da yayi abinda yake so,sannan ya sake shiryawa ya koma office.

Da ya tafi ma bai saurara da kirana a waya ba,bayan mintuna kadan yake kirana mu yi magana, yaji lafiyar babynsa.

****

Munir ne ya fito daga daki da sauri ya biyo bayan mamansa yana mata magana, ina xaki je mama? A yatsine ta dube shi gidan ubanka xan je babana, cike da tausasawa yake mata magana kinga irin abinda nake fada miki mama ki daina irin wadannan abubuwan saboda kina shiga hakkin dady kina fita ba tare da ixninsa ba, a fusace ta juyo ta wanke shi da mari, na fada maka ka fita daga cikin idanuna na rufe kafin ranka ya baci,tunda ka nuna baka kaunata na fita a harkar ka, don haka nima ka bar tawa kafin na saba maka, wucewa tayi ta barshi hannunsa rike da fuskarsa, kaninsa ne ya hango shi cike da tausayawa ya karaso wajen da yake kama hannun yayan nasa yayi tare da jansa gefe daya.

Kayi hakuri yaya a bisa dukkan abinda mama xata yi maka a kan amaryar dady, dole mu jajirce mu ga mun tsamota daga halin da take son jefa kanta har ma da mu, dan Allah kada kayi fushi ka cigaba da nuna mata gaskiya wata rana xata gane, ni kaga ko gaskiyar xan fada mata ma baxa ta tsaya ta saurare ni ba, kai din da kake yi ka cigaba da yi Allah ya baka lada.

Hirar xumunci suka cigaba da yi tare da tattauna matsalar da suke fuskanta a wajen mahaifiyar su.

Kai tsaye gidan kawarta ta xarce da kuka ta shiga gidan, cikin tashin hankali ta tarbeta tare da tambayarta abinda yasa take kuka, kasa bata amsa tayi saboda kukan da take yi, sai da tayi ya isheta sannan ta dubeta.

Wallahi ina cikin tashin hankali tunda dadyn munir yayi aure ban kara samun farin ciki ba, wannan yarinyar taxo ta raba ni da shi, yanxu xancen nan da nake miki kusan kwanansa uku baya kwana a gida, ni duk wannan ba shi ne ma abinda yake tayar min da hankali ba illa yadda ta shiga malamai ta raba ni da su munir yanzu yaran nan gaba daya a bayanta suke basa ganin laifinta, dan Allah ki taimaka min kawata ta karasa maganar tana kuka.

Girgixa kai tayi tana jimamin abinda Hajiya maryam ta fada mata, gaskiya kina cikin tashin hankali kwarai da gaske, amma me yasa kika bari har aka yi auren wannan shi ne kuskure na farko da kika yi, da kin fada min wallahi ko tarewa baxa tayi ba abin xai lalace, yanxu ma dai ba a makara ba kawo kunnenki kiji wata magana, rada tayi mata bayan sun gama ta mika mata hannu suka tafa, sannan suka dauki mayafansu suka fita.

*follow me on wattpad @jeeddahtulkhaeer Tijj*

*jeeddahtulkhair😘*

MATAR DATTIJO CompleteDonde viven las historias. Descúbrelo ahora