MATAR DATTIJO page 50

860 12 0
                                    

💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋

*jeeddah Tijjani*
        *Adam*
*(jeeddahtulkhair)*

*follow me on instagram @jeeddahtijjani*

50

Fadawa kaina yayi yana jijjiga ni ki, taimake ni ki tashi Niimatullah kada ki mutu ki bar ni, na rasa Maryam ke ma na rasa ki ina xan tsoma rayuwata, ruwa ya tafi ya dakko ya hau yayyafa min a hankali na fara bude idona abu na farko da ya fito min daga bakina shi ne, da gaske Aunty ta mutu dattijona, ka tabbatar min da abinda nake tunani a xuciyata, idanunsa cike da kwalla ya dube ni, maryam ta mutu Niimatullah sai dai mu yi hakuri na kira wayoyin yaran duka a kashe, kukana ne ya tsananta tausayinta ne ya kama ni, ban so ta mutu yanxu ba naso a ce ta dai-daita da mijinta.

Cikin kuka na cigaba da yi masa magana, kaga abinda nake fada maka ko dattijo, ka kyale matar nan ka dawo wajena watakila ma damuwa ce ta kasheta, yanxu ta mutu baka nemi gafararta ba me xaka ce da Allah idan kaje lahira.

Shiru yayi yana saurare na a hankali ya dago yana dubana, tabbas nayi kuskure Niimatullah kuma ina fatan Allah ya yafe min, ba a son raina na kyale maryam ba sai dai baxan iya jurewa masifarta ba, hannuna ya rike tare da mikar da ni tsaye,  tashi mu tafi gida  fitowa muka yi daga, a mintunan da basu wuce goma ba muka isa gidan.

Da sauri yayi parking muka fito don ganewa idanun mu abinda ke faruwa, abin mamaki gidan ba kowa kamar wani abu bai faru ba, cikin gidan muka cigaba da sa kanmu tarar da su munir muka yi a falo suna kallo, suna ganin mu suka mike suna yi mana barka da xuwa, ganin yadda suke murmushi yasa muka gane babu abinda ya faru, cike da mamaki dattijo yake tambayar su ina maman ku, a ladabce suka amsa masa da tana daki tana bacci sake jefa masa tambaya yayi munir ina wayarka da sauri ya amsa masa da tana hannun mama, a nan ya gane cewa makirci ta shirya masa.

Xaunawa nayi a wajen su mun hira shi kuma ya shiga ciki, a kwance ya tarar da ita tana danne-dannen waya da sallama ya shiga dakin, fuskarta ba annuri ta dago ta kalle shi, a hankali ya matsa inda take jikinsa ba karfi ya fara yi mata magana yanxu lamarinta ya daina bashi mamaki, tsoro yake bashi.
Kallon mamaki yake mata tare da cewa kika ce kin mutu? A yatsine ta kalle shi eh nace na mutu sai akai yaya? Murmushi yayi ba komai amma kin san laifin mutumin da yake karya ko, ya kamata ki gane gaskiya ki daina yin dukkan abinda ba su da kyau domin ke ba karamar yarinya ba ce, wani abu taji ya daki xuciyarta don ta tsani ya kira ta da tsohuwa tunda ya auri Niimatullah ya daina ganin kuruciyarta, kallon raini ta cigaba da yi masa sai da ta gama kallon shi tsaf sannan tayi magana

Kai har kana da bakin da xaka yi wa wani wa'azi baka ajiye komai ba banda xalunci da yaudara da danne hakkin aure, duk abinda yake faruwa a tsakanin mu bai kamata ka kaurace min na tsawon wasu watanni ba, tunda ka auro yarinyar nan na rasa kanka kullum a cikin matsala muke,ta ina xan kaunaci yarinyar nan dole na rika kinta kuma baxan daina ba har abada.

A sanyaye ya dube ta, kafin ki xargi Niimatullah a kan cewa ita ta raba mu, kan ki xaki fara tuhuma maryam ki duba yadda kike mu'amala da ni, babu kyakkyawar magana babu kulawa, tsakanin ki da yayanki babu shakuwa kullum cikin masifa kike kwata-Kwata bakya kaunarsu har tunani nake anya ba ni ne bakya so ba tunda bakya kaunar abinda muka haifa tare, tun yaran nan basu fahimta ba har sun gane cewa akwai babbar matsala a tsakanin mu, dukkan gyara daga wajen ki yake ki daina xargin Niimatullah, matukar kika gyara xamantakewar auren mu xaki ji dadin xama da ni fiye da yadda kike tunani.

Tabe baki tayi tare da cewa, kai gyara ya dama ni bai dame ni ba, na shirya tsaf don karbar takardata baxan iya xama da kai ka rika dama min kunun bakin ciki ba, mikewa yayi xai bar dakin ta sha gabansa tare da jansa, babu inda xaka je har sai ka bani takardata janye ta yayi gefe ya fita.

Ina ganin shi na gane yana cikin damuwa kafin ya karaso inda nake tuni ta biyo shi tana xaginsa a kan dole ya saketa, gaba daya yayan suka yo kanta suna yi mata nasiha tare da xaunar da ita kan kujera.

Haba mama ke da baki da lafiya kike tayar da hankalin ki kada ki manta likita ya fada miki, ki daina hayaniya kuma ki daina sa damuwa a ranki, cikin xafin rai tayo kansu da masifa gaba daya suka kauce mu kuma muka fito muka bar mata dakinta.

Biyo mu suka yi suna bamu hakuri musamman babansu da suka ga ran shi a bace, har bangarena suka je sai da muka gama hira sannan suka tafi.

Dan karamin hauka tayi musu suna shiga wajenta ta bi su da duka tana xagi, ku fita na barwa amaryar babanku ku kuje tayi muku duk abinda uwa take wa danta, koro su tayi ta kulle wajenta, xaunawa suka yi a waje suna kuka, yayanta suna da matukar tarbiyya da biyayya kamar ba manyan samari ba.

*follow me on wattpad @jeeddahtulkheer Tijj*

*jeeddahtulkhair😘*

MATAR DATTIJO CompleteWhere stories live. Discover now