GOBE NA (My Future)

By KhadeejaCandy

141K 16.8K 5.7K

Babu mace da zata labarta yadda wata macen take ji har sai ta taba kasancewa a cikin halin da wacan macen ta... More

00
GN-01
GN-2
GN-3
GN-4
GN-5
GN-06
GN-07
GN-09
GN-10
GN-11
GN-12
GN-13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
37
38
39
40
41
42
43
44
45
46
47
48
49
50
51
52
53
54
55
56
57
58
59
60
61
62
63
64

GN-08

1.9K 233 25
By KhadeejaCandy

Ina kallonta sai tausayinta da nawa ya rufe ni, ban san lokacin da na fashe da kuka ba na dafe kaina.

“Kai Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u”

Na fada cikin kuka, sai Adnan ya nufo ni yana fadin.

“Yi hakuri Momy sannu”

A zatonsa ciwon da nake masa ina na na dazun da ma fada masa ban sda lafiya ne yake damuna. A dole na share hawayena na kirkiro murmushi na mike tsaye na nufi inda Namra take.

“Kin tashi?”

“Ya jikin?”

“Bana jin ciwon komai”

Ta fada tana ta kallona da idonta da sukai ja saboda bachi, sai kuma ta kwanto da jikinta jikina.

“Bari na kawo miki wani abun ki ci kinji yar kirki”

Ta gyada min kai sai dai ina sauka mikewa tsaye daga kan kujerar sai ita ma ta sauko ta matsa kusa da ni kamar zata shige cikina.

“Zauna bari na kawo miki”

“A'a Uncle Abdallah yace ya daina bari kina yin nisa da ni duk inda kika je na biki ko da gurin aiki ne idan ba haka ba Baba Sadi zai iya zuwa ya yanke ni saboda na fada”

Kamin nai wata magana Adnan ya nufo inda mike da sauri yan zaro ido.

“Baba Sadi ne zai yanke ki? Mi kika fada”

“Ba komai, zo muje”

Hannunta naja ban bari ta sake cewa komai ba. Na nufi kitchen din da ita.

“A cikin gidan nan wani be isa ya zo ya taba ki ba, ke ba a nan ba ko a wani wajen ne wani be isa ya taba ki ba, ki kwantar da hankalinki kinji yar kirki”

Na fada mata ina kokarin zuba mata abincin, sai ta fara motsa ido.

“Mama ina jin tsoro”

“Ai Baba Sadi be san kin fadi wannan maganar ba, kuma ba fada masa zan yi ba dan haka ki kwantar da hankalinki kinji?”

Ta gyada min kai, a plate na zuba mata abincin sannan na janyo hannunta muka fito falo, zaunar ita nai ina kokarin bata abincin sai ta ce.

“Momy ban wanke baki ba”

“To je ki wanke”

Bata min musu ba ta tashi zuwa cikin dakinsu, daman can Namra ba yarinya ce mai kiriniya da jan magana ba, ko abu yake cinta yana da wahala ta iya fada ga ladabi da hankali kamar ita ce yayar Adnan, duk abunda na saka ta sai ta yi ba musu idan nace daina zata daina, ga jinkai duk abunda ta samu ita dai Momy dai Momy dai. Rashin ji da kiriniya sai Adnan shi da yake babba da Aiman dakr binta sai kuma wannan yar berar nan Amal ita kam fitinar ta tafi ta kowa ga barna komai ta dauka sai ta lalata.
  Wayata ce dake kan dinning tai kara, sai na aje plate din a kasa na tashi na nufi inda wayar take, number Abdallah ce har na yi kamar ba zan dauka ba idan sai kuma wata zuciya tace min na dauka wata kila wata maganar ce aka Namra.

“Assalamu Alaikum”

Na masa sallama da sanyayyiyar muryar da ke fassara irin damuwar dake tare da ni, domin bana da wani sauran kuzari a yanzu. Sai da yai shiru for few seconds sannan na amsa min.

“Wa'alaikissalam Halima ya jikin Namra na san ta farka yanzu ko?”

Na gyada kain kamar yana gabana, shi kuma kamar ya san abunda nai sai ya ce.

“Good ki yi hakuri na fada miki magana marar dadi dazun, rai na ne ya bace shiyasa, kuma dan Allah Halima karki saka damuwa a ranki, karki kamar ba zaki iya ba, kina da yan'uwan da zasu iya goya miki baya ki yi komai, karki bar Baba Sadi ya ci bulus”

“Zan aje wayar”

“Okay ki kula da kanki”

Sauke wayar nai ina ta tunanin ranar da Abdallah zai canja, wannan wa'azin ma yana min shi ne saboda ya san idan har na ce zan kwace hakkin yata dole aurena zai mutu, shi kuma abunda ya dade yana jira kenan tun kamin na haifi Namra, ya kwallafa min rai kullum burinsa da addu'arsa aurena dai ya mutu shiyasa yake yawan fada min maganganu marasa dadin ji akan Aminu, ko da yaushe yana fada min be kamata na zauna da shi ba.
Ni kuma ina daukar hakan da son zuciya da kuma son kai irin na bahaushen mutum, taya zaka kwallafawa ranka son matar aure matar wani? Saboda kawai kana da alaka da yan'uwantaka, wani lokacin har haukarsa nake gani domin mutun mai hankali da tunani ba zai yi abunda yake ba.
  Ina cikin wannan tunanin na ji an buga kofar falon.

“Shigo”

Na fada domin na san kofar a bude take ban saka mata key ba. Hajara ce ta turo kofar falon ta shigo tana dauke da Amal sai dariya take bakina har kunne, rayuwarta na burni ne ita kan ta yi dacen aure ba kamar ni ba, abu mai wahala ka ganta a cikin damuwa duk wani abun da take bukata a take mijinta yake mata shi sai idan ba shi da hali.

“Ga yarki nan ta ishe ni da kuka daga kawai na taimaka na je da ita biki, sai ka ce na sato ta”

Na mika hannu na karbe ta sai ta ki zuwa sai ita fushi take tana turo baki.

“Yi hakuri Amal kyale Mama Hajara mun bata da ita har da tufafin Afrah aka saka miki iyeee yarinyata ta yi gayu”

Daker ta zo gareni shi ma da kuka, sai na rungume ta ina dariya. Sai dariyar da nake bata hana kawata kuma aminiyata fahimtar ina cikin damuwa ba.

“Halima kamar akwai damuwa ko?”

Dagowa nai na kalleta kamin na ce wani abun Namra ta fito daga dakinsu ta nufo inda nake.

“Momy ina abinci Maman su Salma ina wuni”

Hajara ta amsa mata ni kuma na fada mata inda tuwon yake.

“Ina cikin damuwa Hajara, damuwar da ta fi ta ko da yaushe kuma damuwar da zata dauwama a zuciyata har abada, ko da kuwa yan hukunta Sadi, ban taba jin na tsani Aminu ba sa yanzu, ban taba dana sanin auren Aminu ba sai yanzu, ban taba jin natsani rayuwa ba sai yanzu, ban taba mafarkin ko jin ina son mutuwa a kusa da ni ba kamar yau, Wallahi Hajara ji nake kamar na sha wani abu na mutu na huta, ina ma Allah be hallice ni ba da duk wannan rayuwar ban ganta ba, ita ba bata gan ni ba, da Aminu be aureni ba”

Da hawaye na ke maganar hawayen da ban yi zaton akwai sauransu ba. Cike da tashin hankali take kallona.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, Halima me ya same ki haka?”

Ban boye mata komai ba, tun daga zubin farko na fada mata komai ina kuka, ita ma fashewa tai ya kuka ta saka hannunta biyu ta dafe kanta.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, Allah ka tsayar mana wannan abun a nan”

Sannan ta dago ta kalleni.

“Ban taba ji uba kamar Aminu ba, taya za ayi ma yarka fyade kuma ka tsaya karyatawa, ai ko ubanka aka ce yayi ma yarka fyade ba zaka karyata ba saboda duniyar yanzu ta lalace, ammn ke yake dorawa laifin? Da ya tsaya ya kula da iyalinsa yadda ya kamata kuma ya tsare mutuncin kansa hakan zai faru ne? Ban taba goyon bayan ki yi ma Aminu komai ba ban taba goyon bayan ki kashe aurenki ba, a kullum ina cikin addu'ar Allah ya karkato miki da mijinki gareki, amman yau kam ba zan goyi bayan ki bar wannan maganar ba, gobe zan je nai magana da Mama zan fahimtar da su abunda kika kasa fahimta, kuma zan tsayawa Namra sai inda karfina ya kare saki ne dai ko? Aminu ya sake ki Abban Afrah zai aureki In-Sha-Allah, ko kin yi lalacewar da kika rasa mijin aure ba zaki rasa nawa ba”

Kallon yar'uwa nake mata ba kawa ko aminiya ba, na san a yadda Hajara ta dauke ni da kuma yadda yake jina zata iya min komai, ko da bana raye balle yanzu da take ganin idona. Sai dai na san abunda ta fada ta fada ne kawai a yanzu saboda ranta a bace yanke, domin ba wata macen da zata yarda mijinta ya auro mata kawarta da amincewarta. Hannuna na kai ya rika hannunta.

“Na gode Hajara kin karfafa min guiwa sosai”

“Wannan abun yayi yawa Halima Aminu yai miki yan'uwansa su rika ganin laifinki kina ganin kin maye komai na dan'uwansu sun dauki kiyayya sun dora miki, yanzu kuma abun ya wuce kanki ya koma har akan yaranki? Ace Kanen mijinki ya kai yana lalata da yaranki? Miyasa be yi da nasa ba sai na ki? Ko naki ne kawai yayan dan'uwansa, kai wannan tashin hankali da me nai kama? Kina cikin jarabawar aure kuma wani ya karo fado miki? Allah ya miki mafita Halima”

“Ameen”

Mun dade muna ta fira da ita tana ta kwantar min da hankali sannan ta tashi na rak har gurin gate ta wuce gidanta ni kuma na dawo cikin. Ina shigowa na shiga kitchen na debowa su Adnan na su tuwon na kawo musu sannan na dauko maganin Namra da ruwa na soma bata. Ina jin lokacin da mota ta tsaya da karfi har na daga labulen windows na leka waje sai na hango Hajiya tare da yayata mata uku wato mahaifiyar Aminu ce da kenensa. Ban ji komai a raina ba domin a yanzu zuciyata a dake kuma na san zuwan nata baya rasa nasaba da fadan da mukai da Aminu a waya dazun wata kila ya fada mata ne. Ashe kuwa na canka a dai dai domin ta shigo falon babu ko sallama tana shigowa cikin falon ta hau fadin.

“Halima mi kika fadawa Aminu a waya?”

Juyowa nai na kalleta na saba sauka na risina har masa na gaisheta idan ta zo gidan ko ni aje ko muka hadu da juna, sai dai yau bana jin zan iya yin haka.

“Hajiya sannu da zuwa”

“Ba sannu da zuwanki na ke so ba, wata magana na ji nake son ki sake maimaita min da bakinki”

“Indai har Aminu ya fada miki, to ba bukatar na sake maimaita miki, iya kar abunda ya kamata ki gane shine ba zan yi ma Sadi kazafi ba haka nan kawai”

“Kazafi ne mana, ai kin dade kina son raba kan gidan nan, kin rasa abunda za ki yi shine kika fake da wannan waya sani ko can gurin aikin naki kika kai yarinya aka lalata sai kuma ki zo ki fake da Sadi, wai ko baki san cewar ni na haifi Sadi ba? Kuma ni din mahaifiyar Aminu ce uba daya ya haife su nono daya suka sha”

“Ko tagwaye ne su Hajiya be dame ni ba, yayanki kike tsaye a nan kina karewa ni kuma na san zafin haihuwa kuma na san zafin keta haddi saboda ni ma mace ce”

Zakiya ta matso kusa da ni tana min tsawa.

“Halima karki ce zaki ma Hajiya rashin kunya Wallahi na ci mutuncin ki”

Ni kuma na mike tsaye ina nuna ga da yatsa a fusace.

“Ke Zakiya iskanci ya tsaya a kanki, karki sake saka min baki a magana ke kanwar mijina ce ba yarsa ba, idan baki da tarbiya Wallahi zan gyara miki zama”

Ta nuna kanta

“Ni din? Ai kece marar tarbiya mai son hada yan'uwa bawan Allah yana can yana nema muku abunda za ku ci kina nan kina tada mishi hankali da yan'uwasa, ko da ya kira har kuka yake yace yana gurin aikin Kaduna amman kin daga masa hankali da maganar fyade”

“Karya dan uwanki yake miki, ba aiki  yaje yi ba hutu ya samu ya dauki karuwarsa suka je can gurin hutu, abunda yake ne yaja akai wa Namra kuma aka rasa wanda zai mata sai dan'uwansa”

Hajiya ta nuna ni da yatsanta.

“Ke marar kunya, fitsararki ta tsaya kanki karki ce zaki min iskanci, ni danaba mazina ce bane, daman can baki da aiki sai kawo kararsa kullum cikin kawo kararsa kike baki taba gode abunda yake miki ba, ke da kike aiki ba ace miki mazinaciya ba sai shi? Tirrr Wallahi mugun abun ki ya biki, kuma Wallahi ki hada kayanki ki bar gidanan ko ke kadai ce mace a duniya ya gama aurenki, ki koma can cikin agolayen gidanku,kuma Yaya sai an kaiwa Sadi shi zai rikasu sai dai ki mutu, wannan zumuncin baki isa ki raba shi ba”

“Zan bar gidan nan Hajiya, amman idan Aminu ya damka min takardar sakina, ba zanje gidanmu na zauna da igiyar auren danki a kaina ba, kuma Wallahi ko ina za'aje sai na je sai na kwatowa yata hakkinta, ban san yayanki haka suke ba Hajiya da ban auri Aminu ba da Sadi be ganni ya ci zarafin yata ba, hakuri na ya kare indai aurena da Aminu na kare ko da kuwa hakan na nufin karshen rayuwata ne, tirr da ɗa irin na ki dan da za a cewa an yi ma yarsa fyade ya karyata ba tare da bincikar komai ba, ke kuma ki sako kafa ki zo ci mun mutunci ko? Kin zo ki shigarwa yayanki to Namra ma ƴa ce idan Aminu be san darajar ta da kimarta ba ni na sani kuma ba zan bar wannan maganar ba, kotu zata kwatar mana hakkinmu”

Tun da na fara maganar babu wanda ya sake cewa uffan ba kanensa kadai ba har Hajiya tsaye tana kallona, ni kaina na san na yi mata abunda ban taba ba, ko kusanyar magana bana iyawa da ita balle kuma har nai sa'insa da ita. A yadda nakr jin kaina a yau ko marina tai zan iya ramawa, domin ina jin babu wata sauran alaka tsakanina da dangin Aminu yanzu. Har Laweeza ta bude baki zatai magana sai Hajiya ta hana ta ta hanyar daga mata hannu sannan ta saka su gaba suka fice daga falon.
Faduwa nai zaune a gurin ina wani irin fuci kamar zakayan.

“Momy ni ce naja fada ko?”

Namra ta tambaya tana kallona tare da fashewa da kuka. Kallonta kawai nai sai na kasa cewa komai na mike tsaye tare da maganin da nake bata na nufi dakina, ina shiga na fada saman gadon a ruf da ciki, wani irin soya nake jin zuciyata na min bana jin kuma ba kuma za a kawo zancen dariya ko farinciki a tare da ni a yanzu ba, gaba daya bana jindadin komai ciki kuwa har da rayuwata. Ina yi awa daya a gurin sannan na mike tsaye na nufi bandaki amai nai bayan na gama na wanke bakina na fito ina shafa cikin da ke jikina, abunda be isa shigowa duniya ba na ke tausayawa wani abu na hade mai nauyi sannan na fito na nufo falo. Wani abun mamaki sai an samu Namra tana ta kuka har da shisshika kamar ranta zai fita, haka ne na nuna alamar ta ci kuka ta kenan sosai har ta gaji. Adnan da Aiman kuma suna zaune a guri daya kusa da ita sun rakube kasa kamar wasu marayu, Amal ce kawai ke ta sha'aninta da wayata da ke hannunta.

“Adnan kuje ku kwanta kunsan gobe akwai scul”

“To Momy”

Suka tashi a tare suka nufi dakinsu a natse kamar ba su ba, yaran da sai na yi da gaske suke zuwa su kwanta ko kuma su yi bachi a duk inda ransu ya so sai na dauke su na kai dakinsu. Kusa da Namra na zauna ya dago ta idonta har yayi ja tsababen kuka.

“Yar Kirki mi akai miki?”

Bata ce min komai ba sai na kwantar da kanta jikina ina ta shafa kanta a hankali. Amal na gani ta rugo a guje tana kuka, daman haka take bata kaunar wani ya taba min jiki ko ya kwanta a jikina sai dai ita kadai. Dagata nai na ajeta a gefena na rumgume ta sannan na karbi wayata. Ganin sako a saman wayar yasa na shiga messages box sunan Abban Namra ne a saman kamar yadda nai saving number. Wani irin fargaba da tsoron bude sakon ne ya kamani a lokacin. Saurin sauke Namra da Amal dake jikina nai na mike tsaye na nufi gaban windows falon rike da wayar ba tare da na bude sakon ba. Na hade yawu ya fi a kirga numfashi na ma har gargada yake zuciyata na raya min saki na Aminu yai. Cikin karfin hali na kai hannu na bude sakon.

_Ni Aminu Idrees na saki mata ta Halimatu Ibrahim saki daya a yau 4 ga watan 3, ya zama saki uku kenan babu gwara a tsakaninmu_

Ina gama karantawa na ji kamar ba a duniyar nan nake ba, ba dan bana bukatar sakin ba, sai dan saki abu ne mai kirma wanda ko baka kaunar mutum idan aka sake ka dole ne sai ka ji wani abun marar dadi ya ratsaka.

_Karki kara minti daya a cikin gidana! Karki yarda na dawo gobe na same ki a cikin gidana, kuma karki daukar min yara_

Shine sako na biyu bayan na farkon, ban san ta inda hawaye suka taru a idona har suka zubo min ba, sai jika screen din wayata suke.

“Zaki iya wannan Halimatu, wasu uwa da uba suka rasa balle ke da igiyar aure ce kawai kike rasa kuma auren mutumen da be san darajarki ba, akan yaranki ne right? Zaki iya yin komai akan yaranki, wannan be isa ya karya miki guiwa ba, be kamata ma hawaye ya ziyarci idonki ba saboda kin rabu da mugun mutum right?”

Ni kadai nake magana da kaina kamar wata tabbabiya da sauri na share hawayena, na nufi Namra dake kallona.

“Tashi muje gida”

Na fada ina daukar Amal, dakin su Adnan na shiga har sun fara bachi na taso su na saka Hijab dina na dauki jakata domin bana jin iya tsayawa daukar komai a yanzu, waje muka fito gaba daya na rufe kofar falon sannan na saka yarana gaba muka fita gate din.
   Misalin tara da rabi muka isa unguwarmu wato family house dinmu, tun a waje na san Abdallah na cikin gidan sakamakon ganin motarsa da nai a waje, bayan an sallame mai Napep di na ji kamar ba zan iya shiga cikin gidan ba saboda Abdallah. Sai da na sauke ajiyar zuciya sannan na saka kafata a cikin gidan, babu kwalla ko kadan a tare da ni a lokacin da na shiga cikin gidan sai dai ina shiga falon nai arba da Mama da kanena biyu da kuma Abdallah sai na ji kuka ya zo min marar misaltuwa.

“Lafiya dai Halimatu”

Mama ta tambaya tana kallona da yara hankalinta a tashe.

“Mama Aminu ya sake ni.....”

Na fada ina fashewa da kuka, kanwata Salma dake kwance kan kujera ta yi saurin tashi zaune tana zaro ido, Mama kuma ta dafe kai ita da Ummi.

“Wow..... ”

Shine abunda Abdallah ya fada yana mika dukan kallonsa a gareni fuskarsa da murmushi kamar ya manta a inda yake.

________________

Saki mace mai ƴaƴa huɗu saboda son zuciya 💔😪
  Anya akwai imani a zuciyar Aminu kuwa?
A matsayinki na mace ya kike auna abun nan ya kike ji a ranki?😪
 
Abdallah me yake yi ma murmushi? 🙄
Idan tawayensa Abdulhamid yaji ya zai yi 🤔
Anya Aminu zai barwa Halimatu yaranta kuwa?.

Continue Reading

You'll Also Like

24.8K 2.3K 52
#10 Hausanovel, 15 June 2020. #47 Nigeria june 2021. Duniya Labari, Duniya Makaranta, Duniya Kasuwa, Duniya wasan gidan yara idan suka tara kasa suka...
1.3M 40.1K 71
ယော.. ကျွန်တော်ကလူတော်..ဒါပေမယ့် လူကောင်းမဟုတ်ဘူး။ စာရေးသူ၏ စိတ်ကူးယဥ်မှုဖြင့် ရေးသောကြောင့် အပြင်လောကနှင့်ကွဲပြားနိုင်သည်ကို သတိချပ်ပေးစေလိုပါသည်။ လ...
59.6K 2.9K 46
ស្នេហាកើតចេញពីការជំនួសមនុស្សម្នាក់ដែលគេស្រឡាញ់ព្រោះតែមានមុខមាត់ប្រហាក់ប្រហែលគ្នា មុនដំបូងគិតថាយកមកលេងសើចតែចៃដន្យអីជាប់ស្នេហ៍គេមែនទែនដកចិត្តមិនរួច និព...
5.4M 719K 198
Main Story ( Completed ) ~~~~~~~°°°°°~~~~~~~ Title - Transmigrated into the film empreor's death-seeking finance (穿成影帝作死未婚夫) Author - Lin Ang Si (林盎...