GOBE NA (My Future)

بواسطة KhadeejaCandy

142K 16.8K 5.7K

Babu mace da zata labarta yadda wata macen take ji har sai ta taba kasancewa a cikin halin da wacan macen ta... المزيد

00
GN-01
GN-3
GN-4
GN-5
GN-06
GN-07
GN-08
GN-09
GN-10
GN-11
GN-12
GN-13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
37
38
39
40
41
42
43
44
45
46
47
48
49
50
51
52
53
54
55
56
57
58
59
60
61
62
63
64

GN-2

2.4K 224 21
بواسطة KhadeejaCandy

Sai da na jika mata kanwar ta sha na shiga dakina nai sallah isha'i, ina sallamewa nai saurin mikewa tsaye na nufi inda wayata take tana ringing na duba na yi zaton ko Abban Namra ne da farko sai dai ganin bakuwar number yasa ni aje wayar har sai na koma saman carpet har sai da na gama tasbihina nai addu'a ma mijina nai ma kaina da iyayena sannan na nemawa yara na shiriya. Daga bisani na mike tsaye na nufi inda wayar take aje na dauka na sake kiran layin da aka kirani da shi.

“Assalamu Alaikum”

Ni na fara mika sallamar kamin wanda na kiran ya fara min sallamar.

“Wa'alaikissalam Halimatu”

“Na'am Ranka ya dade”

Na gane cewar ogana ne na gurin aiki wato oga Dahiru.

“Ki yi kokarin hada document dinka kamin gobe ina da bukatarsu”

“To ranka ya dade”

“Kuma ki yi saving din wannan number ita ma number ta ce”

“To ranka ya dade”

Daga haka ya kashe wayar be sake ce min komai ba, ni ma kuma ban ce ba, daman kuma me zan ce masa, bayan kiran da yake min ma yana damuna balle kuma har nai wata magana da shi, zauna nai bakin gadon ina ta mamakin dalilin kiran da oga Dahiru yake yawan min a duk lokacin da yake bukatar wani abun, shin yana manta cewar ni ma ina da aure da iyali kamar shi, ban san miyasa yake son kira akan abunda be kai ya kawo ba, ba kira kadai ba har wasu abubuwna da yake min bana jindadinsu, domin duk abunda na ke ina kokarin kare mutuncin aure da kuma na yayana da mijina.

“Momy ni dai gobe idan mun dawo daga scul gidan zan dawo ba zan je gidan Baba Sadi ba”

Namra ce ta shigo tana wannan maganar tana wani bata fuska kamar zata fashe da kuka.

“Saboda me?”

“Bana son zawa can Momy dan Allah”

“Ki yi hakuri Mamana, idan kun dawo nan gidan ba wani abun za ku yi ba, kuma kin ga ba girki balle ku ci, amman can Momy Hassana tana girkawa, za ku samu ku ci”

“Momy to ki daina zuwa aikin nan pls ko kuma mu rika zama a gida a haka muna jiranki ki dawo”

“Mamana akwai abunda ake miki a gidan ne da baki so?”

Ta girgiza kai alamar aa sannan ta kwantar da kanta jikina.

“Cikin ya daina ciwo?”

“Eh amman yana min kadan-kadan ba sosai ba”

“Zai daina In-Sha-Allah, na zubo miki abinci za ki ci?”

“Za mu ci tare Momy zan wanke hannuna ba zan saka miki datti ba”

Murmushi nai mata sannan na mike tsaye na fito daga dakin na sauko downstairs. Ban samun Abban Namra a falon ba, daman kuma ban saka rai ba domin ba kasafai yake dawowa da wuri ba, idan kuma har ya dawo to sai idan wani abun zai yi ko zai dauka amman dai ba haka nan kawai zai dawo gida da wuri ba ko kuma ya wuni ba. Tuwon da na girka dazun kamin na fita na zubo miyar kuka sannan na fito bakin kofar kitchen rike da abincin ina kiran Adnan domin bana son sai na zauna ya zo yace min zai ci abincin.

“Adnan Aiman za ku ci abinci yanzu?”

Babu wanda ya amsa ni a cikinsu balle kuma har su sauko kasan da sunan cin abincin, sai Amal da ban kora ba.

“Ommy Ommy zan ci abinci”

“To zo ki ci yar autana”

Na fada ina karasa fitowa falon sannan na zauna kasan carpet din na zaunar da ita saman kafafuwana na soma bata.

“Namra zo ga abincin”

Da sauri ta sauko ta shiga kitchen ta wanke hannunta sannan ta saka min a plate, loma uku zuwa hudu kawai tai ta cire hannunta wai ta koshi.

“Cikin ne har yanzu Namra?”

“Eh ciwo yake min”

Ya fada tana yamutsa fuska sannan ta kwanta a gurin ba tare da ta wanke hannunta ba, ni kuma ban matsa ba ganin gata jindadi har sai da na gama sannan na dauke plate din na kai kitchen na wanke hannuna da na Amal a can sannan na dawo na dauki Namra na shigar da ita dakinsu na cire mata tufafin jikinta na nai mata wankan dare kamar yadda na saba musu na saka mata kayan bachi sannan na kwantar da ita, Adnan nan kam sai da nai kamar ina yi sannan ya bar gabar system din ya tafi yai wanka nai ma Aiman suka kwanta, ni kuma na dauke system dina na fito na baro musu dakin.
Dakina na dawo na kwanta gefen gadon Amal ta haye min kafafuwa tana kokarin fara kukanta na banza. Wayata na dauka na kunna data dama bana samun hawa online sai da dare idan yara sun yi bachi kuma na gama komai, grps din muna na Nothen Women's Advice na fara budewa na duba chat din sannan na shiga na Salma pre-order na duba abubuwan da ta turo cikin har da injimin wanki wanda na fi kowa bukatarsa a cikin gidan nan saboda wanki da nake na yaran nan gashi kwana biyu sun lalata.  Ban bar online din ba sai kusan sha daya da rabi na dare, sannan na tashi Amal wacce a lokacin ta dade da fara bachi a take ta saka min kuka daman ta saba ko ba ai mata komai ba tana kuka balle kuma an yi da dalili. A haka nai mata wanka na saka mata tufafin bachinta na goyata saboda na samu ta daina min kukan.
Dakin yaran na koma na ciro musu dayan set din uniform dinsu na dora musu a inda na saba aje musu sannan fito na shiga kitchen din n dauko abincin Abbah Namra na kai masa dakinsa duk kuwa da na san ba lallai ne ya ci ba domin ba ko da yaushe yake cin abinci a gida ba. A falo na fito da laptop dina na duba document din da oga Dahiru yace na shigo da su na fida su dabam a cikin wata folder sannan na rufe laptop din na koma dakin yara na kwantar da Amal. Na shiga nawa dakin nai wanka na saka kayan bachi na dawo dakin Abbah su na kwanta a take bachi yai gaba da ni abun ka da wanda ya gaji. Can cikin bachin nawa ina jin lokacin da Abbansu ya shigo duk yadda na so na dago nai masa sannu da dawowa sai na kasa saboda bachin da ya ci idona.

Washe gari tun da asuba na tashi, sallah ce farkon abunda na fara yi sannan gabatar da addu'o'ina suma ba duka ba daman idan ba weekend ba bana samun tsayawa nai yi su gaba daya, ina saukowa kasa na shiga kitchen na shiga shirya musu abincin makaranta da kuma na karyawarmu, bayan na firaye dan na fasa kwai sannan na shiga dora ruwan zafin, Amal ce farkon tashi daman haka take tafi kowa rigima ko a dare idan ta motsa bata ji ba, indai yan rigimar suna nan sai ta saka kuka ta dawo dakinmu ta kwana.

“Ommy Ommy”

Ta fada tana murja ido cikin kuka.

“Minene Amal?”

“Bachi”

“Je ki dauko zane”

Sai kawai ta fashe da kuka, haka yasa dole na cire dankwalina na goyata da shi na cigaba da aikina. Ban tashi su Adnan ba sai da na tabbatar na shirya musu komai na makaranta sannan na tashe su nai musu wanka suka sauko kasa na hada musu tea kawai suka sha suka hau sama suka shirya cikin uniform dinsu kasancewar yau monday. Ni kuma na shiga cikin dakina na dauko kudin napep na saka hijab dina na fito na saka yarana a gaba muka fito har Amal muka nufi titi ina kokarin taron napep sai ga makocinmu kuma mijin kawata Hajara ya faka gefenmu tare da yaransa a cikin motar ya sauke gilashin motar yana miko min gaisuwa, sai da muka gaisa sannan ya ce da su Adnan su shigo motarsa suka shiga da saurin ganin yaransa daman can makarantarsu daya kuma yana yawan wucewa da su idan zai kai nasa yaran, wani lokacin ma har gida yake aikowa yace su fito zai kaisu makaranta. Sai da suka shiga motarsa sannan na juyo na dawo ni da Amal ina yanje da hannunta muka shigo cikin gida. Tea ta na dazun da bata karasa shanyewa ba na mika mata sannan na nufi dakin Abbansu, tufafin daya cire na jiya na fara dauka dan hade su da waendan kayan daudan nashi, al'adata ce duba aljihun rigarsa da wando kamin na saka su a kayan dauda saboda cire masa duk wani abu nasa da yake cikin aljihu. Rigar na fara dubawa sannan na saka hannuna a aljihun wandonsa, sai na ji abu kamar kwalin wani abu ina cirowa na ga kwalin kwandon sai dai ba cikakke ba da alama an yi amfani da shi. Ni a
Kadai na san abunda na ji a wannan lokacin a take jikina na dauki rawa kamar dai yadda zuciyata ma take ta bugawa da karfi idanuwa na cika da hawaye. Juyawa nai ina rike da kwandon din a hannuna na kalli Abbah Namra da yake kwance saman gado yana ta sharar bachinsa hankalinsa kwance ni kuma nawa hankalin a tashe da kwandon a hannu. Dayan hannuna na saka na share hawayena da suka zubo na dauke kayan na fita da su, sai dai har nai aikin da nake na shirya Amal nai wanka nai shirin aikina hawayen ba su daina min zuba ba, ni kuma ban fasa sharewa da hannuna ba. Kamar yadda na saba yau ma na hada masa komai nasa na karyawa na shigar masa da shi dakinsa na kai masa, sai dai ban same shi a kwance ba sai na samu ya shiga bandaki da alama yana wanke baki ne, a can na baro Amal na fito na sauko kasa na nufi dinning na hadawa kaina tea amman sai na kasa sha saboda bacin rai da ke cikin raina, i decided na aje tea din na dawo saman cushion na zauna na dafe kaina. Wannan karon ba hawaye na ke ba wani abun ya ke jin ya tsaya min a zuciya marar misaltuwa daker na ke iya hadeye yawu da numfashi. Na kai minti talatin a haka sannan na tashi na koma dakina na dauko kwalin condom din na nufi dakinsa, kamin na kai hannu na tura kofar dakin na jiyo sautin dariyarsa hakan ya tabbatar min ko dai yana magana da Amal da take dakin ko kuma waya yake, ban yake dayan biyu ba na ji yana fadin.

“Na samu hutu satin nan ina kike son muje?”

Hakan yasa ni dauke hannuna daga jikin kofar daman can rikawa kawai nai ban tura ba.

“Kaduna? To yayi ba matsala zan shirya mana komai, amman kamin na turo account dinki zan saka miki wani abu sai ki yi siyayyar da kanki kin san ni ba zan iya zuwa siyayya yanzu ba, kuma kin san idan ina fita da ke yau da gobe za a iya fara cewa wani abu”

Kadan kadan yake maganar amman hakan be hana ni ji ba, domin mutun ne mai daga murya idan yana magana da wani ko da kuwa kadan-kadan yake yi. Ji nai kamar ba zan iya sauraren firarsu suka ba hakan yasa na murda kofar dakin na shiga ina kokarin maida hawayen da suka cika min ido.

“Oh Okay Faruk sai na shigo”

Shine abunda ya fada sannan yai hanzarin kashe wayar, ya gyara zamansa yana kokarin fara cin abinci, ko da wasa ban bar wata alama da zata nuna cewar na fahimci da mace yake waya ba, duk kuwa da kasancewar bana iya sauya yanayi na rashin jindadi da walwala dake tare da ni a yanzu. Zaunawa nai gabansa.

“Ina kwana”

Na fada ba tare da na kalleshi ba. Shi ma bana tsammani ya kalleni kamin ya amsa min sai Amal kawai yake wasa da ita yana bata abincin shi ma yana ci.

“Jiya Hajiya ta sake min maganar kudin ac”

“Ai sai ki ce mata kin fada min magana, ni Wallahi na manta amman yau zanje na fada kudin In-Sha-Allah”

“To Allah ya bada iko”

Be amsa min da amin ba sai ya dago ya kalleni.

“Ya akai kin san bana son ana tsare ni idan ina cin abinci akwai wani abun ne?”

Har zan mishi maganar condom din sai kuma na hade yawu na gabatar masa da abunda na san ba lallai ne yai min ba.

“Jiya ne naga wani injimin wanki da ake order daga waje shine na ce ko zaka saka min wani sai na hada da abunda yake hannuna sai na siya na huta da kai wanki”

“Ba ni da kudi yanzu, ina albashinki? Ko aikin kawai kike ba a biyanki?”

“Ana biyana mana kai ma ai ka sani domin da su na ke rage wasu abubuwan nawa”

“To ki siya da shi ni ba ni da kudi yanzu, da kin ga mutun ya zauna kin fara masa maganar kudi kenan shiyasa ko zama gidan nan bana son yi kuma baki da lokacin magana sai lokacin da nake cin abinci”

“Irin wannan lokacin kawai nake samun damar magana da kai Abban Namra, baka dawowa da rana sai idan wani abun zaka yi da dare kuma sai 12 ko 1 kake dawowa”

“To ni dai ba ni da kudi yanzu”

Ya fada yana wani kara hade fuska. Sai na aje masa condom din da ke hannuna murya a sanyaye na ce.

“Ga wannan na gani a cikin kayan da ka cire jiya”

“Oh jiya Bala ya bani ajiyarshi na manta na bashi abarsa”

Ya fada kai tsaye kamar gaske ba tare da ya kalleni ba. Idanuwana cike da kwalla na ce

“Ko dai na wanene Allah ya sani kuma yana jiran kowa a madakata”

Ina fadar hakan na mike tsaye sai dai kamin na kai tsayen ya rigani yana daka min tsawa.

“To me kike nufi? Zagin kike ko kuma Allah ya isa za ki min? Wai mi yake damunki ne Halima? Daman munanan mata kun fi komai bakin hali ku ba kyau ba sai sakawa mutum damuwa da bakin zargin tsiya”

“Ba ni n hallici kaina ba Abban Namra, kuma saboda bana da siffar da kake so a jikin mace ba shi yake nufi ka bi wasu matan ba, kai kanka kasan ba haka ka aureni ba, auren shekara goma sha biyu bana kwana biyu ba ne, dole wani abu a jikina ya canja, na haihu har hudu dole jikina ya bude, ka dinga jin tsoron Allah Abban Namra....”

Kamar jira yake na kare a take ya wanka min wani mahaukacin mare mai zafi kamar garwasun wuta, kamin nai ihu Amal ta fara fashewa da kuka ta rike masa kafa damn ta saba masa haka ida da su Namra da Adnan idan yana dukana, ni kuma ban tsaya komai ba ya juya da sauri na fice daga dakin ina kuka.

“Dacan bana tsoron Allah aka ce miki? Wawuya kawai”

Shine kadai abunda na ke iya jiyo yana fada bayan na baro dakin, da gudu na dawo dakina na zauna kasa na fashe da wani irin kuka mai ban tausayi da taba zuciya.

واصل القراءة

ستعجبك أيضاً

43.6K 2K 11
Karka nuna dan yatsa akan kalar rubutun da Alkalamin kaddara yaima waninka. Baya tsallake kowa, naka a rubuce yake tun kamun samuwarka. Karkace zakai...
12.4K 2.4K 64
Ƙalubalen ZAWARCI a kasar hausa, da hanyan kawo gyara cikin kalubalen da ɗiya MACE take fuskanta kan ZAWARCI sanadin mutuwar miji ko kuwa kaɗdarar sa...
53.5K 7.2K 67
Original Title Saving the Tragic Adonis •Associated Names 拯救美强惨反派[穿书] •Type Web Novel (CN) •Genre Comedy School Life Shounen Ai Slice of Life •Author...
27.7K 3.9K 42
Love Crossing Sheikh lovely daughter with mafia badass King, how comes destiny and passionate met