ZARAHADDEEN

hijjartAbdoul द्वारा

1.6K 71 8

read and find out अधिक

1
2
4
5
6
7
8
9
10
11
12
13
14
16
15
18
19
20
21
22
23
24
25
26.
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
37
38
39
40
41
42.
43
44
45
46
47
48
49
50
51
52
53
54
55
56
57
58
59
60

3

33 2 0
hijjartAbdoul द्वारा

           ✨ *ZAHARADDEEN* ✨

                            3.

*****Ameer yace, "Yaya Deeni tare da kai zamu tafi fa".

Taufiq yace, "Yaya Ameer ka nace sai ka je Kanon nan".

Hajja tace, "A'a kaga bar shi yaje ya samu kuɗin sa, tunda ku kuna zaune a gida zaman kashe wando nima da kuke gani na nan ba'a zaune nake ba. Da idan Banda zamani ma goɗai-goɗai da ku kuke zaune sai an baku. Samu kuka yi ai".

Deeni yace, "Me zai je yayi acan ɗin?

Hafiz yace, "Rabu da shi dan Allah. Shirmen sa ne wai shi kasuwanci zai yi".

Murmushi Deeni yayi yace, "A'a idan har Baba ya yarda shikenan, sai mu tafi".

"Wai idan yaje me zai yi ɗin?

"Ka manta Sadiq yana nan yana cigaba da aikin su Baba ? To shima ba sai ya cigaba da kula da wajen ba. Kaga daman Sadiq ne kawai ɗan gida shi kuma yanzu service yake yi, dan Ameer yaje shima kafin ya tafi shi kuma Sadiq ya gama".

"Makarantar ma sai yayi acan idan ya samu".

Ya kuma faɗa.

"Ni Yaya Deeni ba zan yi makaranta ba, ta isa haka makarantar".

Hajja tace, "To mun ji wannan. Idan kayi kuma ka zo kana jin daɗi kada naji kada nagani".

"Kina ina lokacin? Ai lokacin ƙasa ta gama binni ki kuma ma ni ba zan yi ba. Kawai ayi ta karatu ana sake maimatawa?

"Yaro kenan, to ina nan sai naga auren ka".

Dariya kawai yayi ya rabu da ita. Yayin da suka cigaba da magana har Hafiz ya yarda akan cewa zai bishi ɗin. Sosai hakan ya yiwa Deeni daɗi. Ya roƙi kar a sanar da Baban ma kawai  idan ya dawo zai ji. Dake Baba da Umma sun tafi Umara idan suka dawo kuma za su tafi amma banda  Hafsah.  Daƙyar ya yarda zai kwana ana shima sai da Hajja tayi magana tukunna ya yarda, sosai Mamancy take ganin kimar yaron da kuma darajar sa, tun suna yara har yau be sauya hali ba daga wanda ta san shi da shi daga shi har Hafiz tana kuma yi masa addu'ar dacewa a rayuwar sa tare da yi masa addu'ar mace ta gari dan mace tsab zata iya sauya masa halin sa.

***"Ta jima tana gunguni ita ɗaya musamman  idan ta tuno amsar da ya bata 'ga wanda ban sani ba' haushi abin nan take ji kamar tayi kuka haka take ji. Ita kaɗai tayi ta ƙunci abinta. Ta gama, ba su ƙara haɗuwa ba sai washegari da ya zo tafiya ba kuma tasan da Ameer za'a yi tafiyar ba, kawai de ta gan su ne tare da ƴan gidan su za wai za su raka su airport, gaida su kawai tayi ta wuce kitchen. Tana ƙara tuno abinda yace mata. Wai ita aka faɗawa haka? Ƙwafa kawai tayi.

Deeni ne ya dubi Hafiz yace, "Zancen auren Ameera ka ƙara dubawa fa. Kar ka manta".

Murmushi Hafiz yayi yace, "Ka damu da auren nan har haka?

Sanin kan sa be taɓa damuwa da wani abu ba, koda ya na damun sa, shi kaɗai yake warware abin sa, amma wannan batun auren yasan rayuwar yarinya ƙarama za'a jefa a cikin garari duba da irin tarbiyyan shi kan sa yaron. Bama shi kaɗai ba duka gidan na su kowa da irin yarda yake rayuwarsa. Hakan yasa shi murmusawa kawai be kuma cewa komai ba. Har suka ajje su a airport be ƙara magana ba sai sune da suke maganar su.

*****Zarah ce a zaune a waje wurin ajje motar su an baza tabarma anyi mata ƙunshi ana mata kitso, Sadiq a kusa da ita yana aiki a system  kuma babu nepa dan indai da nepa ba abinda zaka ga Sadiq a waje yana ciki. Kallan ta yake yarda ake mata kitson, shi sam be yarda da zuwa gidan kitso da ƙunshi ba gwara su zo ayi mata, tun suna talaucin su ya tsani sallah ta zo ace su je su ɗauko su daga gidan ƙunshi wani lokacin sai karfe biyun dare za su je su dawo dasu wannan abun haushin sa yake ji sai dai be taɓa nunawa ba. Yanzu kuwa da ke ya kai kuma Allah ya hure musu kuɗin da za su biya su zo har gida ayi musu alhamdulillah sun gode Allah....

"Yayaaaa".

Ta faɗa da ƙarfi kamar ta  ta so ta gudu ta rungume shi, murmushi yayi sosai yana dosowa wajen ta tare da tsugunnawa yana kallan ta.

"Yaya sannu da dawowa".

"Sannu ya gidan?

"Alhamdulillah".

"Ameer?

Sadiq ya faɗa yana nuna farin cikin sa na ganin sa, shima murmushin yayi yana ƙarasowa suka gaisa.

"Yaya tare kuka zo?

Sadiq ya tambaya yana tashi domin miƙa masa hannu.

Ameer yace, "A'a daga sama na fito".

Dariya suka yi suna gaisawa.

Zarah tace, "Ina yini".

Ganin sa da tayi sangameme da shi ya cika mata ido dan ya kusa Sadiq sam batayi tunanin Ameer ne ba duk da cewar suna chat da shi, kuma bata fiye wani ganin hotunan sa ba a cewar sa wai baya hoto, shi kuwa Ameer ya sake ya amsa da lafiya.

Sadiq yace, "Ehh lalle su Zarah yaushe aka fara gaida ɗan sa'a kuma?

Ameer yace, "A'a Wallahi Yaya Sadiq na girme ta wannan yarinyar".

Deeni tashi yayi dan ba zai iya wannan musun ba, Zarah idan aka musu da ita ba'a taɓa gamawa sai ta ƙure mata, baya jin ita da Sadiq har yau Sadiq ya  taɓa cinye ta gashi ita ce bata da gaskiya amma idan ta haƙiƙance zaka rantse da Allah ita ce mai gaskiyar ta kuma yi nasara. To shima Ameer haka yake.

Tace, "Ya Sadiq bangane ba? Wai Sa'a na ne wannan ɗin? Harda wani ya girmeni?

Yace, "Baki gane shi ba wai? Ameer ne fa. Ɗan Baba shida Ameera".

"Ameer? Wai na Ameerah? Laaa kuma shine cib. Kai Ameer haka ka zama sangameme da fa wani ɗan firit da kai kamar a hure ka ka faɗi ƙasa "

"Lalle Yarinyar nan kin ga makwanci na shiyasa".

"Lalle yaron nan ka ga ka fini tsayi shiyasa".

Ta kuma faɗa tana kwankwayen muryan sa.

Yace, "ehh ɗin, yarinyar de ta gaida ni. Kuma daga yau Yaya Ameer zaki na cewa idan ba haka ba na daka ki a gidan nan".

"Ka daka wa?

"Ke".

Be rufe baki ba yaji tana wani abu. Sai ga geese sun fito daga wata ƙaramar ƙofa sun nufo wajen su. Ameer ganin jibga jibgan abubuwa sun nufo shi yasa shi ɓoyewa a bayan Sadiq, ganin sun biyo shi yasa shi arta da gudu zuwa cikin gida aikuwa suka rufa masa baya yana gudu suna bin sa. Me kuwa Zarah da Sadiq za su yi ba dariya ba.

Da gudu ya shige cikin parlourn su wanda yake da ɗauke da ɗaki huɗu abin su kowa daya sai na gwaggo dake tare da su har yau. Kallan sa Deeni yayi da ya fito jin ihu yana masa kallan lafiya?

Jin ana ƙwanƙwasa ƙofar ne yasa shi sanin geese ne ya biyo shi. Yasan kuma wannan ba kowa ba ne sai Zarah har ta fara nuna halin kenan kai kawai ya girgiza kan sa ya koma.

Gida ne madaidaici mai ɗauke da ɗaki huɗu da parlour sai kitchen ɗin su tsakar gidan babba ce ba irin can ɗin nan ba dan a ƙalla mota uku zuwa huɗu za su iya shiga. Daga can ta baya kuwa wata ƙofa ce ƙarama wanda idan ka buɗe ta zaka ga wurin kiwon su ne. Akwai dabbobi wurin su daban haka ma tattabaru suma na su wajen daban, sai talatalo da kuma geese sai shuke shuke wasu na ci wasu kuma na kwalliya da bishiyo wajen yayi kyau sosai. Geese ɗin masu bin mutane idan ba su san su ba sun riga sun riƙa gashi ba su fiye ƙyanƙyansa ba.

Sadiq ne ya shigo yana zama.

Yace, "Daga zuwan ka har an fara yi maka welcoming naka da wancan abubuwan ko?

"Wallahi Ya Sadiq ba kaji me naji ba caab wayyo Allah na".

Ya faɗa yana sauke ajiyar zuciya irin abun ya bashi tsoro sosai.

"Da ka tsaya ba abinda za su maka ai".

"Haba Ya Sadiq".

Murmusawa Sadiq yayi kawai yana tashi da jan jakar su da suka zo da shi, ya kai masa ɗakin sa shima Deeni ya kai masa nasa ɗakin dake kusa dana Zarah ya zamana sune suka sata a tsakiya sai na gwaggo itama nata a gefe. A dakin da ya kasance na Ummi shine Deeni ya koma da zama. Sai ya zamana kowa yana da ɗaki ɗaya.

"Ka taso mana Ameer ka shirya".

"Yunwa nake ji".

"Bari na zuba maka abinci".

Ya faɗa yana yin hanyar kitchen ɗin tare ya zubo musu ya zuba masa abin sanyin da aka haɗa sun rigada sun saba indai za su ci abinci to sai an haɗa wani lemu ko sun siyo. Suna cikin ci Deeni ya fito ya zauna lokacin an kawo nepa hakan yasa shi kunna TV yana kalla yana jin su suna hiran su, wanda daman sun rigada sun saba abin su.

"Nikwa ina wannan jarababbiyar nan ta gidan ku?

"Wai Anty?

"Da wata ne jarababbiya ne bayan ita?

Dariya Ameer yayi.

Yace, "Yaya Sadiq ina zata je? Tana nan mana".

"Tunda muka tashi da tsohuwa unguwanni mu muka dawo nan ku kuma kuka koma Abuja bamu ƙara haɗuwa ba kaga ko sanda naje bautar ƙasa na duk zuwan da zan yi bata nan".

"Yanzu daƙyar idan zaka gane ta ma dan ta sauya kama dukan ta".

"Ai wannan matar sai addu'a ga faɗa ga masifa. Ni naga mijin da zata aura".

"Yaya Sadiq kamar a kunnen ta".

"Rufa min asiri dan Allah ni yanzu bani da faɗa".

Girgiza kan sa Deeni yayi yana tuno masifar ta, baya jin zata iya sauyawa ita kam a rayuwar ta. Wannan masifa ta rigada ta zame mata jinin jiki.

***** Da daddare ya kira Sadiq yake sanar da shi game da zuwan Ameer da kuma abinda ya kawo shi. Ya ƙara da cewa.

"Sadiq ka jashi a jiki ya ji kamar nan ɗin ma gida ne, ba abinda zamu iya biyan Baba dashi kai kanka ka san da hakan".

"In sha Allah Yaya ba za'a sami matsala ba, zan kuma bi dashi na nuna masa komai zuwa gobe idan Allah ya kaimu".

Shiru suka yi hakan yasa shi kallan sa yace, "Da wani abu ne?

"Yaya daman ina da shawara ne".

"Tame fa?

Shiri yayi yana kallan ƙasa kafin kuma a hankali ya ɗago ya kalli inda yake ganin yana kallan sa yasa shi saurin maida kan sa zuwa ƙasa.

"Ina jin ka Sadiq".

"Ya..ya daman".

Tattara nutsuwar sa yayi ya dena abinda yake yi gaba ɗaya, ya tashi ya zaunar da shi a kan gadon kasancewar a ƙasa yake da zama.

Yace, "Ina jin ka".

Sunkuyar da kan sa yayi ƙasa sam be san ta ina zai fara ba.

"Sadiq kana da wani ne da ya wuce ni?

Girgiza masa kai yayi alamar a'a.

Yace, "To faɗa min wacce shawara ce?

Ya faɗa hakan duk da yasan ba wai shawarar ce a yanzun yake so ya faɗa akwai wani abu dake damun sa.

"Yaya nan bayan mu ne suke so su siyar da gidan nasu kuma sun rasa me siya shine nace mai zai hana mu siya idan ya so sai a gyara shi, kayi part ɗin ka daban".

Kallan sa yake har ya kai aya, sannan ya ɗago ya kalle shi.

"Inaji Sadiq".

"Shine kawai Yaya".

Ajiyar zuciya Deeni yaja yana mai tattara nutsuwar sa waje ɗaya sannan ya kalli Sadiq.

Yace, "Sadiq mene abinda kake ka sanar dani?

"Yaya so nake kayi aure?

Sosai abin ya bashi dariya har ya  kasa ɓoyewa ya ɗan dara kaɗan.

Yace, "Sadiq aure kake so kayi?

"Wallahi Yaya a'a kawai so nake naga matar ka Yaya. Ya kamata ace Yaya kayi aure koma ba komai Yaya zaman haka ba shine mafita ba".

Murmushi kawai yayi yana girgiza kan sa. Wai Sadiq ke ce masa yayi aure. 'ikon Allah '.

"To kai yaushe zaka yi aure?

"Nifa Yaya ba aure zan yi ba yanzu. Duka duka nawa nake".

"Kuma kake tara ƴan mata kake batawa kan ka lokaci?

Ya faɗa yana ƙure shi da kallan karka min ƙarya.

"A'a Yaya wallahi kaji rantsuwa ni ba wacce naje na ce ina so kawai sune suke cewa suna so na. Yaya fa har yaƙi aka taɓa yi akai na fa".

Murmushi kawai yayi masa. Be ce komai ba dan yasan da gasken yake abinda ya faɗa.

"Yaya".

Ya faɗa a hankali.

"Uhm?

Shima ya amsa masa.

"Dan Allah ka duba lamarin to ka gani. Ya kamata ace kayi aure. Nasan ko ban faɗa maka ba, Baba zai sanar da kai ko kuma baya san takura maka ne".

"Kaga Sadiq idan aure kake so. Idan ka kammala service ɗin ka zan yi maka aure, amma maganar aure na kar na sake ji, kar na sake ji ka min ita. Sanda lokaci ya yi zan yi. Tashi ka bani waje".

Ya faɗa yana cin serious. Haka Sadiq ya tashi jiki a mugun sanyaye, bakomai ne yasa Sadiq cewa yayi aure ba sai irin maganar da aka fara jifan su da ita a unguwa cewar  zaman kan su sune a gida ba uwa ba uba. Kamar ba'a unguwar Ummi ta rasu ba. Harda cewan ba su da ƴan uwa to su sai yaushe za su ga na su ƴan uwan?  Baya so maganar ta dawo kunnen Deeni shiyasa yayi masa zancen auren ko ba komai aure nasa wa aga kimar su da darajar su. Haka ya koma parlour suka cigaba da zama.

"Ya Sadiq lafiya?

"Bakomai".

Ya bata amsa a takaice yana kallan Ameer.

Yace, "Ka shirya gobe da wuri mu fito saboda hold up nan ba Abuja ce ba".

Dariya Ameer yayi.

Yace, "To Allah ya bani iko".

Dan yasan kullum shike makarar da su saboda bacci amma dake wannan aikin yana so ne shiyasa zai dage yaga be bawa kowa kunya ba.

"Amma ina so idan ka je, kada ka kuskura su san tare muke, kada su san ma cewar gidan mu ɗaya".

Jinjina kai kawai Ameer yayi, yayin da Sadiq ya cigaba da faɗa masa yadda abinda zai kasance.

*******Washegari da wuri suka tashi kafin su tashi kamar kullum an jera musu abinci a tsakiyar parlourn yarda suka saba ci. A kusan tare suka fito Deeni ne ya fara zama yana ajje jakar sa yana zuba shayi mai zafi yana kaiwa bakin sa. Sannan suka iso suka zauna suna sake gaisawa duk da cewar sun gaisa da aka fito da asuba. Duban sa ya kai wajen Ameer ya ci serious.

Yace, "Ameer bana san lattin Sallah ka  kiyaye".

Ameer be taɓa ganin sa a haka ba, hakan yasa jikin sa yayi sanyi ya gyaɗa.

"In sha Allah za'a kiyaye Yaya Deeni kayi haƙuri".

Jinjina masa kai kawai yayi yana cigaba da cin abincin sa ganin be ci komai ba. Wayar Ameer ce tayi ringing ganin sunan yasa shi nunawa Sadiq.

Yace, "Kai ne mai neman ta gata ta kira".

"Masifaffiyar gidan ku hala?

Jinjina masa kai yayi yace, "bari kaji masifa zata min tace dan uwarrka".

Ya faɗa yana ɗagawa tare da sa speaker. Aikuwa suka ji tace, "Dan uwar ka kana  ina? Ka zo ka bani tab ɗina".

"Anty bana nan fa. Ina Kano jiya muka  taho da Yaya Deeni".

"Mtsw".

Kawai tace ta kashe wayar ta.

Sadiq sosai abin ya bashi dariya.

Yace, "Amma kuna jin tsoron ta kai kaji muryan ka kuwa?

Ya faɗa yana ƙara tuntsirewa da dariya, murmushi kawai Ameer yayi alamar ba zaka gane ba shi yasa. Shima Deeni dariyar kawai yayi tunda da abinda tayi. Shine ya fara gamawa sannan ya tashi ya musu sallama yaje ya gano Zarah dake bacci sannan yayi gaba.


******Hashim A. Madaki ɗa ne ga Alhaji Madaki kowa yasan da zaman su a Nigeria su ɗin wasu irin mutane ne masu yalwar dukiya, da fari da siyasa ya fara sai kuma ya fanjama Black market daga nan ya shara sosai a faɗin duniyar Nigeria, ko ina sun san su ko da ba'a san su ba a fuska to tabbas an san sunan companies ɗin da suke da shi, ko da ba kasan sunan su ba to tabbas ba zaka taɓa tsallekewa ba tare da kasan ɗaya daga cikin kamfanonin su ba. Hakan yasa yaran sa suke abinda suka ga dama, sun kasance daga uwar su har Baban na su babu ɗaya dake kwabar su duk abinda suka yi daidai ne, yarinyar su kawai ƙwara ɗaya ita ce bata biyo dukkan halin su ba Maryam, Maryam ta fita daban a cikin su yaran gidan su biyar, dukka huɗun halin su ɗaya ne, hakan yasa bata taɓa musu maganar abinda suke yi ba dai-dai ne ba ta rigada tasan da cewar sun yi nisa basa jin jira, hakan yasa take kasancewa ita ɗaya a rayuwar ta, bata da ƙawa bata da kowa haka take rayuwar ta cike da burgewa da kuma waye, tana da ilimin addini sosai dan da kan ta tasa kan ta a islamiyya tun farkon dawowarsu  Abuja sanda suka fara facaka da kuɗin Al'umma wanda har yanzu suna yi ba wai denawa suka yi ba. Hashim shine babban ɗa ga Alhaji Mamman bashi da mutunci bashi da kirki, ba kuma ya ragawa kowa, akwai shi da san ƴan matan tsiya. Sai kuma na biyun su Dalhat shima baya jin maganin kusan halinsa ɗaya da Hashim, Maryam ita ce ta uku, da Safiyya, bata da kunya kowaye ya  shiga shirginta tsaf zata faɗa masa magana san ran ta ba ta ganin darajar kowa ga kuma yawon zuwa party sai kuma ƙaramin su Musaddiq shine karami shekarar sa goma sha biyar amma gagararreni na bugawa a jarida. Mahaifin su akan abu ɗaya ne baya ragawa yaran nasa shine wasa da duk wani cin nasarar da suka je nema, anan kawai ran sa zai ɓaci sosai da sosai amma baya ga haka takura yaran sa. Sannan kuma nasara ko ya take shine da ita, baya taba faɗuwa a cewar sa nasara ita ke bin sa ba shi ke bin ta. Haka kuma wata irin baiwa da Allah yayi wa ahalin sa suna da matuƙar ƙoƙari a komai su ne suke ɗaya hakan yasa shi yake ƙara ji da kan sa be ɗauki cuta a matsayin komai ba face cin nasara. Ya jima dakon samun hanyar da zai bi domin ya ci galaba a companyn FD wato fashion and design companyn da turawan suka dauki su Baba aiki yayin da Baba ne za'a ce ya kusan gina shi wanda har suka buɗe branch ɗin shi a Abuja har dawowarsa. Hakan yasa shi yin dabara ganin cewar ɗan uwan sa ne Uban su ɗaya ai kuma ba shi da wata matsala shiyasa ya shiga jikin sa ya ja ra'ayin sa da nemawa Ameerah auren ɗan Dalhat, abinda yasa ya ce Ameerah shine saboda ita ce bata da hayaniya ba kamar Hafsat ba, sai da ya tsaya ya karanci yana yin gidan tsaf da mutanen cikin sa ya yanke wannan hukuncin sannan ya fara tsari a kai.  Ya kuma sa Dalhat da cewar shi ya nuna yana so yayin da shima Dalhat ya nuna yana so ɗin, Wanda har aka sa rana anyi komaj lokaci kurum ake jira.

Hashim shine wanda yaje Anadyr a matsayin wanda yaje domin ɗaya daga cikin company ɗin su sai de ba su yi nasara ba karo na farko kenan a rayuwar su da hakan ta kasance, haɗuwar sa Hafsat ba ƙaramin ƙona masa rai yayi ba, tambayar da yake yiwa kan sa kawai wacece ita?? Dan shi gani yake kamar ya san fuskar shiyasa ya riƙe mata hannu domin ta dawo su yi magana, amma shine ta mareshi? Shi be ɗauka cewar riƙe hannu wata manufa ne ba daman da wani abu ba, tunda ai ba laifi ne ba dan a riƙewa mutum hannu amma shine ita zata daga hannu ta mare shi? To a'ina ma ya san ta? Tambayar da ya kasa nemo amsar ta kenan.

Dalhat shine wanda za'a aurawa Ameera. Hashim shine wanda Hafsat ta mara. Gashi kuma Deeni da Hasfat sun yi nasara wa companyn su yayin da na su beyi nasara ba. Shin tafiyar zata iyuwa a haka? Shin za su haƙura batare sun biya wannan* *nasarar ta su ba? Nasara a jinin su take kuma ita ke bin su? Bagwa ganin a wannan karon nasara ta* *juya musu baya? Sannan kuma yaya auren Ameerah da Dalhat yake? Za'a yi auren? Ko kuma ba za'ayi ba? To wanna kadan kenan* *daga cikin littafina mai suna "ZAHARADDEEN"*

*Kada ku manta littafina bana kuɗi ba ne ba, abinda nake so kawai* *shine comment ɗin ku shine burina bakomai ba, kuyi comment, kuyi* *min share sannan ga dukkan wanda yake son karatu a Wattpad yayi ba*

पढ़ना जारी रखें

आपको ये भी पसंदे आएँगी

15.3K 1.1K 47
Unrequited love. When a patient person reaches his limits what happens? He explodes. The true color of this wicked world and cruel life shows. When t...
73.6K 1.8K 22
Sans is brought to the world of BNHA. He wakes on the roof of UA.He'll meet new friends and enemies, old and new. But will he ever get over the jar...
23.3K 3.8K 75
Copyright ©2020 Heshma Nabayi All rights Reserved This is a story about a young girl named Najma Muhammad Farouk, whose dream is to become a pilot...
MOHABBAT-E-DIWAANGI Aanya_writess द्वारा

सामान्य साहित्य

297K 21.7K 26
Avantika Aadish Rajawat Aadi, with his fiery nature, adds intensity and excitement to their relationship, igniting a spark in Avni. Avni, like the ca...