GOBE NA (My Future)

By KhadeejaCandy

142K 16.8K 5.7K

Babu mace da zata labarta yadda wata macen take ji har sai ta taba kasancewa a cikin halin da wacan macen ta... More

00
GN-01
GN-2
GN-3
GN-4
GN-5
GN-06
GN-07
GN-08
GN-09
GN-10
GN-11
GN-12
GN-13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
37
38
39
40
41
42
43
44
45
46
47
48
49
50
51
53
54
55
56
57
58
59
60
61
62
63
64

52

2.4K 311 178
By KhadeejaCandy

Garin daukar cingan din naji na taba wani abu mai kamar karfe, da na ciro cingan din na duba da kyau sai nai arba da makullin mota.
  Ba shiri na mike tsaye ina dubawa duk da bani da motar ina kallon wannan makullin na san cewa na mota ne, wani irin faduwa gabana yai sai an rasa abunda zan yi kuma na kasa yarda cewar makulin motar ne, yana sane ya saka min shi ko? Ko dai ba da gangan yai ba. Maida makullin nai na dauki box din na nufi office dinsa.
  Tsaye na tararda shi jikin fridge ya kafa gorar ruwa a bakinsa yana sha, ganina yasa ya sauke ruwan ya juyo yana kallona.

“Ina....ina tunanin ka yi mantuwa a box din na ga wannan”

Na fada ina budewa na dauko makullin na nuna masa. Sake cika bakinsa yai da ruwan sannan ya aje ruwan ya rufe fridge din.

“No ina sane na saka, na yi ta tunanin abunda zan ba ki as birthday gift, sai na ga babu abunda ya dace a yanzu nai miki kyauta da shi kamar mota, saboda zuwa aikin da kike sai ki huta da hawan napep”

“No i can't accept this”

Na fada ina nufar teburinsa na aje makullin.

“Lims why”

“A'a Halima dan Allah, ranka ya dade kana min abunda ba a cikin dokikin kamfanin nan yake ba, ko da kana taimako ina tunanin kana taimako na ne saboda Allah, ba zan iya karba kyauta mai girma irin wannan ba, bana son alakar mu da wuce haka”

“Why? Kina tsoron an sake shiga rayuwarki? Saboda Aminu ya cuce ki? Abdulhamid ya juya miki baya? Abraham ya yaga rigar mutuncinki? Dukansu maza ne ko ba haka ba? Kina tsoron ki sake komawa wani hali ko? Kina tsoron kar wani yace yana son ki wata rana ya juya miki ba right? Kina da gaskiya kuma kina da hujja kuma dole ayi miki uzuri....”

Ya matsa kusa da ni sosai yana kallon cikin idona.

“Duk abunda nake miki, ina yi ne saboda na ga na faranta miki rai, ba ke kadai kika cancanci farinciki ba, nima na cancanci farincikin, amman na danne nawa na manta da nawa, na danne duk wani bakin rai da damuwa da suke raina, saboda ke na sama miki farinciki, daga lokacin da samu labarinki sai nai kokarin mantawa danawa kin san saboda me? Saboda tausayinki ya cika min zuciya”

Ya kara matsowa daf da ni.

“Dukan abunda nake miki ina yi ne saboda zan iya kuma saboda na fi karfin abun, ba zan taba yi miki wani abu dan kawai ya tambayi so daga gareki ba, zuciyata bata taba raya min na siye soyayya kowa ba, balle kuma ke, ban taba jin cewar nai miki wata kyauta ko wani abun jidadi dan na tambayi soyayyarki da shi ba, Lims ina son shiga rayuwarki na taimake ki na taimaki yayanki da yan'uwanki”

Na yi saurin kaucewa ina aje numfashi.

“Ni ban shiryawa aure ko soyayya a yanzu ba, duka mazan nan da suka yaudare ni babu wanda be nuna min so na gaskiya ba, amman daga baya komai ya canja, kai mai gidanane be kamata alakar mu da wuce haka ba, indan har da gaske taimako na zaka yi to ka taimake ni saboda Allah kawai”

Dayan hannunsa ya saka aljihu, ya juyo yana kallona.

“Ni ma ba zan bari kiyi yanka akan danye ciwo ba, ai baki gama warkewa daga ciwon ba, ke kike kokarin saka kanki a so ba ni ba, na kai ki a restaurant din da nake cin abinci ne har na zaunar da ke a kujerar da kike zargin wani abu ne saboda na yarda da ke, na daukeki yar'uwa ne shiyasa na tura miki sakon cewa I'm not just your friend, na aika miki da sakon birthday ne a gidanku saboda kina daga cikin mutane masu muhimmanci a rayuwata, dukan abunda nake miki saboda kawai ina tausayinki ne kuma ina son ki samu farinciki, idan zan siye soyayyarki ba ta wannan sigar zan biyo ba, shim fada min na taba furta cewar ina son ki? Ko na taba zuwa gidanku da sunan zance? Idan zan nemi aureki a gurin iyayenki zan tafi ba a gurinki ba, domin ni kallon budurwa nake miki yar 18, ba zan yi magana da ke ba har sai da izinin iyayenki, amman abubuwan nan da nake yasa kin fara tunanin son ki nake? Ashe son ki yana da arha da yawa”

Na kasa cewa komai sai hawaye nake, wani irin abu na rashin jindadi da kunya ya baibaye ni, tabbas be furta yana so na ba, amman ya nuna yana kokarin boyewa a yanzu saboda yana ganin kamar ba zan ba shi hadin kai ba, wata kila kuma na yi kuskuren fahimta taya babban mutum mai rufin asiri kamar Ahmad zai ce yana so na? Taya mutumen da ya san wani ya min fyade zai yarda ya zauna da ni? Taya mutumen da samu komai na jindadin rayuwar duniya zai ce yana so na?
      Matsowa ya sake yi kusa da ni ya mikomin tissue.

“Share hawayenki, babu kalmar da na fada dan na bata miki rai, babu kalmar da na fada dan na muzanta ki, ba zan ga wanda zai fada miki wata magana marar dadi ba na saurara masa, ba zan cilasta karbar abunda ba ki da ra'ayi ba, lokaci yayi da ya kamata ace kin samu jindadi rayuwa kin daina kuka, ko akan yara ko akan komai ma, shi nake kokarin nuna miki, ki kwantar da hankalinki ki sake jikinki”

Ya fada cike da nuna damuwar hawayen da nake zubarwa, da kansa ya janyo min kujera ya aje bayana.

“Zauna”

A take na zauna daman jikina ya dade da yin sanyi. Sai ya risina gabana yana kallon fuskata, fuskarsa na dauke da murmushi.

“Fada min gaskiya ko dai ke kike so? Dan kin ga ni kyakkyawa ne?”

Yanayin da kuma sigar da yai min maganar na san ya fada ne kawai dan ya saka ni murmushi, kuma na yi murmushi ina share hawayena.

“A yafe min hawayen nan da na saka kika zubar, seriously bana son naga kina kuka, bana son na ganki cikin damuwa, idan har ba zan iya cireki a ciki ba to be kamata na saka ki a ciki ba”

Ya karasa yana kama kunnesa kamar wani karamin yaro. Sannan ya mike tsaye ya nufi gurin kujerar.

“Idan kina son motar zaki iya dauka, idan kuma ba kya ra'ayi”

Na karasa yana daga kafadunsa alamar hakan be dame shi ba.

“A a na gode”

Na fada sannan na tashi na nufi office dina ina jin nauyi, zuciyata kuma babu dadi, kamar be dace nayi masa maganar ba, idan ma zan maida kyauta ba sai na nuna dan wani abu ya ba ni ba, sai a lokacin ne na ji wata kunyar ta kara baibaiyeni.
Cikin rashin kuzari na zauna na fara aikina ina jin jikina sai a hankali, haka ma rai, juyawa nai na kalli windows dakina dake rufe sai na mike tsaye na karasa gurin ya bude windows din, hangoshi nai tsaye yana kallona fuskarsa ba yabo ba fallasa, kamar kullum hannayensa na zube aljihu. Juyowa nai na dawo na zauna amman na kasa samun natsuwa lokaci zuwa lokaci sai na waiga na kalli windows a duk lokacin da zan kalli windows sai na ganshi tsaye yana kallona.
Tashi nayi naje na rufe windows din sannan na samu natsuwa, bugun zuciyata ya daidaita har na samu damar fitar da numfashi a natse.
Na cigaba da aikina amman sai na nemi natsuwata na rasa gaba daya na kasa tsayarda hankalina guri daya, kuma na rasa dalilin haka, after every two minutes sai na ji gabana ya fadi, ba faduwar gaba irin na tsoro ko fargabar faruwar wani abu ba, faduwar gaba ne irin wanda ban saba jin irinsa ba.
  Misalin sha biyu saura wayata tai ringing, sai na saka hannu a jakata na dauko wayar. Abun mamaki yau Abdullah ne yake kirana, abun ka da mai nema jiki na rawa na dauka ina doka sallama kamar yana gabana, da fari na yi zaton ko zai min murnar birthday na ne tunda na dora a status kuma na san zai gani, amman bayan mun gaisa sai ya bijiro min da wani batun na dabam.

“Abdulhamid ya bata yau kwana uku”

Da mamaki na ce.

“Abdulhamid ya bata kamar ya? Sai kace karamin yaro?”

“Nima ban sani ba, an nemi an rasa wayarsa kuma bata shiga, so na fada miki ne saboda ki kula saboda ina tunanin batansa baya rasa nasaba da Abraham”

“Abraham kuma?”

“Eh Abokinsa ne, so be careful”

Yana fadar hakan be tsaya komai ba ya kashe wayar, mamaki da al'ajab suka rufe ni, daman Abdulhamid yana da alaka da Abraham ne? Amman a cikin babu wanda ya taba nuna min cewar ya san wani, shi kansa Abdallah be tana nuna min haka ba duk kuwa da kasancewar na fada masa komai a game da Abraham din.
  To idan ma Abraham ya saci Abdulhamid me zai masa? Me zai saka ya sace shi? Hakan na nufi Abraham yana da alaka da Abdulhamid kenan shiyasa yai min fyade ko kuma me? Ko kuma shi Abdulhamid din ya san Abraham din ya min fyade? Amman kuma Abraham din ai shi police ne, sai dai a sigar da suka shigo gidan zuwan farko da kuma na biyu duka ta sigar fashi suka shigo, a zuwansa na farko ma ya bukaci kudi kuma ya tambayi ina Abdulhamid yake, ba kowa na sani a abokaninsa ba, amman be taba min labarinsa ba, ko da yake Abdulhamid ba mutum ne mai yawan magana ba dan baya son hayaniya.

Wani tunanin ne ya fado min a rai, ba ni ce kadai a cikin hadari ba har da Ahmad, domin kuwa Abraham yasan da cewar Ahmad ya san sirrinsa, idan har zai iya sace Abdulhamid to ba zai bar Ahmad ba, jiki na rawa na tashi da sauri na nufi office dinsa, domin gaba daya tsoro ya gama kamani, ko da na shiga na tarar yana waya, sai dai ganina yasa yayi saurin yanke wayar ya ta so ya nufo inda nake tsaye.

“Lafiya ya naga hankalinki tashe?”

“Yanzu Abdallah ya kira ni ya fada min wai Abdulhamid ya bata, kuma yana zargin da sa hannun Abraham”

Kansa ya daga kasa ya lumshe ido ya busar da iskar bakinsa sannan ya bude ya kalleni.

“Kin tada min hankali sosai na dauka wani abu ya same ki, to miye naki a batan Abdulhamid din ko Abraham”

“Zai iya cutar da kai, tun da ya san kasan sirrinsa, ko da yana da sanda, a lokacin da suka shigo min ta siffar yan fashi suka shigo min, zai yi maka komai, zai iya kokarin cutar da kai, idan wani abu ya same ka ta dalilina, ba zan jidadi ba, ban san inda zan saka kaina ba, ban yafewa kaina ba”

Na karasa cikin muryar kuka, kara matsowa yai kusa da ni ya kai hannunsa kamar zai taba ni sai kuma ya fasa ya juya bayansa, yana maida numfashi, can kuma ya juyo ya kalleni.

“Za ki iya zuwa gurin motata ki jira ni?”

Na gyada masa kai da sauri daman tuni hawaye sun wanke min fuska jikina rawa kawai yake kamar mazari.

“Good girl je ki yanzu”

Na juya ina share hawayen na fita na koma office dina na dauki jakata da wayata na nufi inda motarsa take. Kamin ya iso duk na matsu, sai dai na lura da mutane sun fara saka mana ido cikin har da blessed wacce idan ta gan ni na fito ba a lokacin tashi ba take ce min wai zan fita da oga ne ko?
Tun kan ya karasa ya matsa remote din motar ta fita key ni kuma na bude na shiga na zauna, yana shigowa ya tashi motar muka bar kamfanin.
Ganin muna ta tafiya ba tare da ya min magana ba yasa na ce.

“Ba ka ce min komai ba”

Kallon idona yai da ke cike da hawaye.

“Lims sarkin kuka, ki kwantar da hankalinki babu abunda zai same ki”

“Ba ni ba kai”

“Ni kuma ke ce damuwata”

“Haba ranka ya dade...”

Ya katseni

“Ahmad”

“Ahmad....”

Na maimaita cikin sautin kuka sannan na cigaba.

“Wannan ba abun wasa ba ne, Wallahi zai iya cutar da kai, duk mutunen da zai iya keta haddin aure ya lalata rayuwar wata to zai iya komai, ban san adadin abunda ya aikata ba, ban san iya abunda yai ma wasu ba, wata kila ya tana kisa, ban sani ba, zai iya cutar da kai, kana tunanin idan wani abun ya same ka ni zan jidadi? Zan iya walwala?”

“Duk wannan hawayen saboda ni? Mi kake nai?”

Ya tambaya yana faka motarsa gefen titi.

“Ka kwarara tsaro a gidan da kamfani, kuma ka fadawa police halin da kake ciki”

“Police ba za su iya ba ni tsaro ba, kuma ki kwantar da hankalinki babu abunda zai same ni”

Ya miko min ruwa.

“How ta yaya zaka ce babu abunda zai same ka bayan Abdulhamid ya bata kuma....”

“Abdulhamid yana hannun DSS”

“What....?”

Na masa wani irin kallo na mamaki.

“Yes su suka kama shi yana Abuja”

“Ho.. How.... Do you know kai kasa aka kama shi?”

Na nuna shi da yatsana.

“No bincike yasa aka kama shi, har Abraham din suna can tare”

“Miya faru? Fada min?”

“Nima ban sani ba”

“Then taya ka san an kama su?”

“Mataimakin DSS na jihar nan he's my friend, shi ya fada min”

“Miyasa aka kama su? Kai ka saka aka kamasu?”

“Saboda me? Idan ma zan saka a kama wani ai Abraham zan saka a kama ba Abdulhamid ba, na fada masa matsalar Abraham ne kawai ana cikin bibiyar sa ana bincike ta masa, sai ga wannan ya faru da Abdulhamid din, shi ya fadi Abraham aka kama su”

“Amman miyasa aka kama su din?”

“Kin san sana'ar da Abdulhamid din yake yi?”

“Yana saida mota kuma yana aiki”

“Ya taba baki labarin Abraham, ko kuma shi Abraham din ya taba baki labarin Abdulhamid”

“A'a”

“Shiyasana fada miki, Abraham din ba son gaskiya yake miki ba, ba zai bar abunda yake saboda ke ba, ba kuma zai fallasa miki sirrinsa ba, da dawo gareki ne kawai saboda yana son haihuwa, kamar yadda ya fada miki zai iya mutuwa a ko yaushe idan asirinsa ya tonu, ya taba fada miki cewar yana da mata?”

Na girgiza kai da sauri.

“A a”

“To yana da mata tana can garinsu enugu, dukansu su biyu suna wani business, kuma babu mai sanin alakarsu sai su i think basa yawan ziyarta juna ne saboda gudun kar a zarge su”

Bude motar nai na fita ina shakar iskar waje. Sai shi ma ya bude gefensa ya fito ya zagayo inda nake.

“Hakan na nufi Abdulhamid ya san cewa shi yai min fyade kenan?”

“Be zama lallai ya sani ba, domin ba kowa zai yarda abokinsa ya keta haddin matarsa ba, zai kuma iya yiyuwa ma shi ya saka shi, ko ma dai minene gaskiya zata bayyana”

Dana lumshe idona sai hawaye suka sauko min. Ina jin lokacin da Ahmad yaja dogon numfashi ya sauke.

“Sometimes, Allah yana jarrabar bawanaa ba dan baya son bawan ba, daga baya kuma sai ya kawo masa sauki, a yanzu ne zaki gane ba karamin taimakinki Allah yai ba da ya raba ki da Abdulhamid, shi kan shi uban yayanki da za ki bibiya tahirinsa wata kila za ki samu wani abun ya same shi, ko kuma zai same shi a gaba, shi kansa Abraham din da kin yi kuskuren aminta da shi kin aureshi da kin jefa kanki a cikin wata matsalar, trust me Allah yana son ki, and i think lokacin kukanki ya kare, wani jindadin nesa, wani za ki ga sai ya tsufa ta hanyar yaya zai samu, wani kuma sai ya sha wahala, wani kuma ya jidadin farko daga baya wahalar ta zo, ki gode Allah Allah ya kawo miki sauki tun a yanzu”

Bude idona nai na kalleshi, sai na ji ya kara kwanta min a rai, yana da gaskiya wani jindadin nesa yake, wani kuma ba za a taba jindadin ba har abada.

“Bana son ki saka kanki a damuwa, bana da tashin hankali a yanzu kamar damuwarki, Doc Nura ya fada min cewar idan zuciyarki ta sake bugawa zan a iya rasa ki, so bana tafar haka, kina bukatar ki rayu ko dan saboda yayanki da ni, ina ji a raina cewar ni kadai ne namijin da zan juya duniyarki ki jidadi, na baki abubuwan da kika rasa, na ranta ran mahaifiyarki da yan'uwanki, ba alfahari nake ba, ba kuma ina fada da wata manufa ba, dukan abunda zan yi a yanzu dan na saka ki cikin farinciki ne na mantar da ke damuwarki, a yanzu kam bana jin zan iya bari ko kuda ya cutar da ke lims, wahalarki ta yanke da izinin Allah”

Ji nai kamar ya daure ni, indai jin kalamai ne na sha jinsu daga bakin maza, amman baka gane gaskiyar kowa sai ka zauna da shi, sai dai idan na kalli Ahmad sai na ga kamar be yi kama da mutanen da za su iya wannan ba. Sai dai idan har kalamansa suna nufin soyayya ko aure to ban shirya ba a yanzu, bana jin akwai namijin da ya cancance ni a yanzu sama da Abdallah.

“Zamu iya komawa Gurin Aikin?”

“No na fito da ke nan waje ne saboda ki samu natsuwa and fresh air, yanzu kuma ki zan kai ki gida ki huta just for today daman yau birthday ki ne you're princess”

Na juya na shiga motar, shi ma ya zagaya ya shiga yai mata key.

“Kamin na hadu da ke, idan na tuna babu matata babu Baby Namra babu Mahaifina sai na ji duniya ta ta koma upside down, ammn daga lokacin kaddarar rayuwarki ta same ni sai komai ya canja, na zama jarumi na ji cewar nima zan sake samun farinciki, a duk lokacin da na tuna da yata sai na tuna ki sai na ji bakincikin rashinta ya tafi”

Kallonsa nai sai ya sakar min irin murmushin nan da ake cewa ya fi kuka ciwo.

“Ya isa a nan zan sauka sai na hau napep”

“Ba ki son a gan ki da ni ne ko? Fine”

“No bana son ina shiga motar mutane ne, yanzu sai ka ji ana magana”

“That's why na baki mota ai dan na dauke miki wahalar hawan napep, kuma tsakani da Allah ina jin bakincikin hawan Napep da kike saboda namiji ne zai tuka ki”

“Idan ka bani motar ka bude hanyar da za su kara zargina, a fara magana akai”

“To shikenan zan aje miki har lokacin da za ki bukata”

Har na bude motar da zimmar fita sai kuma na kalleshi.

“Baka fada min wani irin business suke ba?”

“Nima ban sani ba, amman ko minane idan sun gama bincike ai kowa zai ji”

Na fita daga motar sannan na rufe mishi motar sai ganin nai ya sauke gilashin motar.

“Ki kula min da kanki”

Ya fada sannan yai ma motar key ya hau titi, ba ni da abunda ya wuce na bi motarsa da kallo har sai da na daina hangota.

Continue Reading

You'll Also Like

31.1K 2.9K 27
အန်တီက မောင့်ရဲ့ထာဝရကြင်နာသူပါ။ အန္တီက ေမာင့္ရဲ႕ထာဝရၾကင္နာသူပါ။
38.8K 3.6K 94
An Interesting Love story
151K 16.7K 122
💥New BL ဒါဒါတို့ရေ... ရှေးခတ်ကျေးလက်တောရွာကို ကူးပြောင်းမှ ကြိုက်ပါတယ်ဆိုတဲ့ဒါဒါလေးတို့အတွက် အသစ်လေးလာပါပြီ .... ရှားပါးတဲ့ MC Gong ပါနော် Gp လေးက...
12.4K 2.4K 64
Ƙalubalen ZAWARCI a kasar hausa, da hanyan kawo gyara cikin kalubalen da ɗiya MACE take fuskanta kan ZAWARCI sanadin mutuwar miji ko kuwa kaɗdarar sa...