GOBE NA (My Future)

By KhadeejaCandy

142K 16.8K 5.7K

Babu mace da zata labarta yadda wata macen take ji har sai ta taba kasancewa a cikin halin da wacan macen ta... More

00
GN-01
GN-2
GN-3
GN-4
GN-5
GN-06
GN-07
GN-08
GN-09
GN-10
GN-11
GN-12
GN-13
14
15
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
37
38
39
40
41
42
43
44
45
46
47
48
49
50
51
52
53
54
55
56
57
58
59
60
61
62
63
64

16

1.9K 240 31
By KhadeejaCandy

Milk shadda ce a jikinsa sai farar hula, fuskarsa na ta sheki kamar shi ne angon ga wani kamshin tutare da yake mai sanarda zuwansa tun kamin ya iso. Abu biyu ne babu a tare da shi walwala da sai kuma yar ramar da yai kadan. Da sallama ya shigo falon Hajiyarsa sannan ya zauna da bismillah, kamin ya mika mata gaisuwa daga inda yake zaune. Sai ta amsa masa tana ta kallon yanayinsa yanayin da ya sauya masa tun sati biyu da suka gabata.

“Hajiya ta sai yanzu ake karyawa?”

Ya fada yana kallon kofin tea da ke hannunta.

“Aa yau da dumamen tuwo na karya sai yanzu na ke shan tea”

Be sake cewa komai ba ya maida hankalinsa a gurin tv da ke kunne.

“Ba kaje aiki ba yau ko kuma ba a aikin ne yau?”

“Zan je yanzu, Suwaiba na kai gidan Abdulhamid, daman ta matsa min tun kwanaki baya tana son zuwa na hana ta sai yau dai na kai ta”

Har lokacin da yake maganar be kalli gefenta ba. Yana shirin mikewa tsaye ta ce.

“Jiya Mal Dalhatu ya zo nan”

Da sauri Abdallah ya juyo ya kalleta jin ta ambaci mahaifin Halimatu.

“Mi ya kawo shi?”

“Yace yana ta son ya zo yai mana godiya be samu dama sai yau saboda yanayin jikinsa”

Dan murmushi yai ya kawardar fuskarsa.

“Baba Karami akwai karfin hali, miye abun godiya a ciki ai yi wa kai ne”

“Yi wa kai ko kashe kai? Akan me za ka dauki nauyin irin wannan dawainiyar haka? Ya fada ko ruwan da aka sha a gurin wunin nan kai ka kawo su”

Cikin muryar da ke bayyana rashin jindadinta tai masa maganar hakan kuma ba karamin mamaki ya ba Abdallah ba, domin be taba ji ko ganin ta hana su yin wani aikin alheri ba musamman abunda ya shafi yan'uwa.

“Akan me mace zata nuna maka kiyayya kuma ka dauki nauyin hidimarta? Har da wani daukar yara ka saka su makarantar kudi ina ruwanka ba su da uba ne?”

A karon farko ta yi masa maganar a tsawace tana dire kofin tea da ke hannunta da karfi.

“Ban yi dan wani abun ba Hajiya, a gaban ki Alhaji ya bar mana wasiyar taimakon yan'uwa da mabukata, kuma tun ba yau ba idan za ayi biki a gidan Baba Karami mu na yi masa abu mai nauyi saboda mun tashi mun ga Alhaji na yin haka kuma ya mana wannan wasiyar, ba hidimar aure kawai ba har abincin da za su yi ke da kanki kin sha daukar abu daga nan ki aika musu balle kuma mu da muke jininsa”

“Ba alheri na ke hana ka yi ba, wannan karon ka yi alherin ne a gurbin da be kamata ka yi shi ba, akan me mace zata nuna maka kiyayya kuma ka nuna mata kula har da duniyarka”

“Hajiya idan Halimatu ta auri Abdulhamid kamar ni ta aura, ni da Abdulhamid duka daya ne kuma.... ”

Hannu ta daga masa.

“Na fika sanin wannan kai da shi duka ni na haife ku, ina magana ne kawai akan abunda yake bayyane ni na san Abdulhamid ba son Halimatu yake ba, ita ta janyo ra'ayinsa ba kuma saboda kowa ba sai dan kai”

“Haka ya fada miki?”

“Ba sai ya fada min ba, ni na san waye ďana, be taba zo min da maganar wata mace ko son yin aure a wannan yanayin da yake ciki ba sai a wannan lokacin, mutumen ma da neman lafiyarsa ya saka a gabansa? Rana tsaka ya zo min da zancen auren nan idan ba ita ta nuna masa ba taya za ayi ya kawo wannan tunanin a ransa? Kuma ya rasa mace aure sai Halimatu bazawara? Mai yaya hudu yana saurayinsa bayan kuma ba iya komai yake ba Allah yasa dai tsakani da Allah zata zauna da shi”

Murmushi Abdallah yai ganin yadda Hajiyarsa take ta bude wuta.

“Ban da abinki Hajiya Abdulhamid ai ba yaro ba ne da zata nuna masa hakan ya yarda idan har ya san baya son ta ko kuma zai cutu”

“Ko dai minene Husaini be dace Halimatu ta auri Hassan ba bayan ta san kana sonta ban goyi bayan Abdulhamid ya auri Bazawara ba a aurinsa na fari na kyale shi ne kawai saboda na lura da ra'ayinsa na son yin haka kuma bana son na karya masa guiwa saboda ya dade yana mafarkin aure be samu ba, kuma na tabbatar shi kansa be san kana son ta ba Wallahi ba zai aure ta ba, amman ita ai ba yarinya ba ce ya kamata tai tunani indan har ba zata aure ka ba to be kamata ta auri dan'uwanka ba, ko da kuwa shi ya nuna mata son da gaske sai da ta fasa aurenku duka, Hassan ya ji da wanne yayanta guda hudu ko kuma lalurar da take gabansa? Da gangan tai wannan saboda ta bata zumunci kuma ya batu”

Abdallah ya shafa kansa tare da hade yawu sannan ya kalli Hajiya a raunana ya fara magana muryarsa kasa kasa.

“Jikina yana yawan ba ni haka, ina yawan jin cewar kamar Halimatu ta jayo soyayyar Abdulhamid ne ba shi ya kai kansa ba, sai dai zuciyata ta kasa yardar da hakan, tun daga lokacin da kika fada min Abdulhamid ya zo miki da maganar auren, ko wane dare sai na lalubo na ga ko zan hango wani abu da zai saka na zargi Halimatu amman Wallahi Hajiya na kasa ganin laifinta, a maimakon haka sai tausayinta ya kara kamani saboda na san Abdulhamid ba kamar ni ba ne baya son yara a rayuwarsa, ko da ma yana son yara ba zai kaunace su a lokacin da yake saurayinsa ba ita kuma take a bazawara ta zo masa da yara, ga mahaifinsu be kula da su ba, and yan gidansu gaba daya mata ne mazan uku duka kanane da ba su yi wani wayo da za su iya kula da tattalin kanensu ba, balle ma yayan yayyu, abu ne mai wahala ta samu mai kula mata da yaranta yadda ya dace”

“Can ta matse mata ina ruwan wani? Ita yarinya ce da ba zata yi tunani ba kamin ta aikata abu? Ni Wallahi da tausayi take ba ni amman yanzu na natse ko ganinta bana son yi, ba dan kuma komai ba sai dan wannan wawanci da ta aikata, ni Wallahi bana son Abdulhamid ya auri bazawara kuma bazawarar ma wacce dan uwansa yake so kuma ita ta san hakan amman ta yarda”

Wannan karon wani dogon numfashi yaja ya sauke.

“Hajiya akwai wani kuskure da na aikata a can baya, wanda na ke tunanin wata kila saboda shi Halimatu take son hukunta ni kuma na cancanci haka”

“Haba Husaini wani irin laifine da zai saka ta auri dan'uwanka saboda kai? Ni ban ga cancanta aurenta da Abdulhamid ba Wallahi na san waye ďana”

“Hajiya na yi kuskuren furtawa Halimtu cewar ina sonta a lokacin da take da aure, tun da na dawo kasar nan na ganta sai ta ga ta canja min kamar ba ita ba sai Allah ya dauki son ta ya saka min a rai, a lokacin na yi ta kokarin ganin na haka zuciyata abunda take son cusa min amman na gagara, Wallahi Hajiya har ta kai idan zan kwanta ko ina wani abun sai tunaninta ya fado min a rai, musamman da na samu labarin yadda mijinta yake da kuma irin yadda take hakurin zama da shi, a lokacin shaidan ya yaudare ni kuma yayi galaba a kaina zuciyata tai ta nuna min cewar Halimatu bata dace da auren Aminu ba, ni ta dace ta aura a lokacin akwai good understanding tsakanina da ita, hakan yasa na fara nuna mata irin halayen mijinta da abubuwan da yake marar kyau, daga lokacin muka fara samun matsala da ita, a lokacin ne na fada mata kai tsaye cewar ina son ta.... ”

Shiru yai for few seconds ya shafa fuskarsa sannan ya sake sauke numfashin a karo na biyu.

“Na fada mata zan iya aurenta idan har zata iya kashe aurenta ta fito, kuma na yi ta aikata abubuwan da nake sa ran za su iya zama silar mutuwar aurenta, Astagafurullah ....Abubuwa da yawa Hajiya har ta fara fada min bakar magana tana min kallon wani shaidani yes ni kaina a ynzu ina jin na aikata ba daidai ba, amman a wacan lokacin sai na kasa gane hakan duk da na san bata dace da auren Aminu ba amman ai he dace na yi sanadin mutuwar aure ba ko?”

Hajiya ta gyada masa kai. Sai ya maida kansa kasa yana taba agogon hannunsa

“Yes i know... Kuma na san shi ya janyo min wannan matsalar a yanzu, so ko da ma ita ta janyo soyayyar Abdulhamid batai laifi ba inda dai ta hukunta ni tai i deserve it, and Abdulhamid ya fi ni bukatar aure a yanzu saboda yana a situation din ba ko wace mace zata iya aurensa a yadda yake ba sai mai hakuri da jajircewa kamar Halimatu”

“Babu wanda ya san da wannan matsalar sai mu, sai kuma ita a yanzu waya sani ko ta gagara zaman ta fita ta tona mana asiri kuma ta bayyana ma duniya halin da Hassan yake ciki bayan a da yana cikin rufin asirin Allah? Na fi tausayin Hassan fiye da kai na dade ina jiran zuwan ranar da zan ga Hassana yayi auri yana rayuwa ta farinciki kamar kai kamar kowa, amman na bana farinciki da auren nan, saboda yayi auren a lokacin da be dace ba kuma da wacce ba ta dace ba”

Mikewa tsaye Abdallah yai yana jin wani abu na rashin jindadi yana kawo masa ziyara.

“Haka Allah ya kaddara”

“Haka Allah ya kaddara kuma da son ranta ba, idan ma wannan hukunci ne take tunanin ta yi to kuskure ne babba”

“Zan je gurin aikin Hajiyarmu ba wani abun ko?”

“Babu”

Sai da ya kalli yanayinta sannan ya sa kai ya fice ransa ya susuwa zuciyarta na konuwa.

HALIMATU POV.

Al-hamdulillah shine abunda na ke yawan maimaitawa tun daga lokacin da na saka kafata a gidan Abdulhamid, duk wani abun na jindadi rayuwa da mace zata nema a gidan miji Abdulhamid ya tanadar min shi, tun daga na ci har na sakawa a jikin har na kallo, kamar wata kwai haka yake tarairaiya ta a yadda yake nuna min kulawa da soyayya ban tsamanci samunta a gurinsa kamar haka ba. Yana yawan nanata min cewar ina da wani irin girma da daraja a idonsa saboda aurensa da nai alokacin da yake dauke da lulurar da ba ko wace mace ce za ta yarda ta aure shi a haka ba, wannan dalilin yasa yake da kara gwarjini a idonsa. Ya kara maida hankalinsa gurin neman magani fiye da da, ni ma kuma ina kokarin yi masa abubuwan da zasu taimaka duk dai bana ganin wani alamu na warkewar sai ban taba gajiyawa ba ko na fitar da rai domin na san babu cutar da bata da magani. Ina samun kwanciyar hankali a aurena da Abdulhamid fiye da wanda nai a baya da Aminu, ko ba komai zai nuna min kulawa zan kwanta a kirjinsa na farka a gefensa mu ci abinci tare mu yi fira mu yi hara mu yi nishadi, ba kamar a gidan Aminu ba da ba shi da lokaci na.
Bana da wani fargaba ko tunani a gidan aurena bayan ta mutum biyu yayana da kuma Hajiya wato mahaifiyarsa domin na lura a duk zuwan da muke gaishewa kamar bata na'am da ni, bayan a baya kuma ba haka na santa ba, duk dai ba wani zuwa muke sosai ba amman a duk lokacin da muka je gaisheta ko kuma muka fito daga wani gurin muka biya sai ta yi min tarba ba a baya da kai ba, ko kuma ta bar a nan a falon ba ita kadai ba har yayanta mata biyu na lura haka suke min basa son fira da ni balle kuma irin wasar nan ta matar yaya, namijin ne kawai babu ruwansa shi kan idan muka tarar da shi a gida mu yi ta fira abun kamar ba kanen mijina ba, amman bayan wannan bana da wata matsala da Abdulhamid idan ka cire na kyamar yayana da yake yi, domin na lura ko zancensu baya son ina yi idan aka kira waya da sunan za mu gaisa da su a lokacin da yake kusa da ni da a take yanayinsa zai canja, be taba siye ko da biscuit din maira goma ya mika min ko ya bawa wani yace a kai musu balle kuma har ya tambayi lafiyarsu ko karatunsu, sai dai ina masa uzuri da wannan ganin cewar shi din be taba aure ba sai yanzu kuma daman can ba mutum ne mai son yara ba, ballanta na san yadda wasu mazan suke basa son yayan wasu a kusa da su, musamman Abdulhamid da na lura da alamar yana ďan da kishi ba kamar wasu ba, tun daga lokacin da yai kokarin hana ni aikina na lura da hakan ga kuma ya hana yin ko. Wane irin social media saboda kar na hadu da maza, yana yawan fada min cewar na rike masa kaina na tsare masa kaina kar na bar shaidan ya rinjaye ni, wani lokacin na kan amsa masa da to ko nai masa alkawarin haka ba wani lokacin kuma sai dai na yi dariya, domin a tunani babu abunda zai kai ni na aikata wani alfama ko da bana da aure balle ina da shi, ba wai na fi karfin shaidan ba ne, kawai dai ina tuna baya ne a lokacin da Aminu zai iya shafe wata da watannani ba neme ni ba kuma babu kulawa da magana mai dadi ga shi ina zuwa aikin ina ganin mazan amman ban aikata ba, balle yanzu da nake auren mutumen da ya san darajar aure kuma bana ganin mazan ma, to mi kam Allah na tuba wace tsiyar ce zata saka ni aikata hakan.
  A zaman aure da Abdulhamid wani abun da zai baka mamaki shine rashin iya girki, wanda ni kaina yake bani mamaki kuma ya ba ni tsoro, tun da na zo gida ban taba dora girki ko da ruwan zafi ne ya tafasa ba, idan na dora miya yadda na hada ta haka zan zo na tararda ita haka tuwo ma, shiyasa ban taba yin jalof ba lalle shimkafa da wake, indai har za mu sha tea sai dai Abdulhamid ya dora mana, indai har ni na dora ba zai tafasa ba ko da kuwa a gas ne ko electric kettle. Sai dai be taba sakawa Abdulhamid ya min fada ko nuna bacin ransa a hakan hakan ba, kullum safe shi zai dora mana ruwan da za mu amfani da su da rana kuma yai mana take away haka ma da dare, na kuma rasa gane dalilin haka bayan a can baya na iya girki na kamar ko wace mace, amman tun da na tsinci kaina a gidan Abdulhamid sai komai ya lalace.
  
Ranar wata labara da misalin sha daya da yan mintuna na ji an buga kofar falona, na yi tsamammi ko daya daga cikin yan matan gidan mu ne hakan yasa na tashi da kuzari na bude, abun mamaki sai nai arba da Suwaiba matar Abdallah kuma uwar yayansa mata guda biyu, na yi mamakin maganinta domin ta dade tana min waken zuwa amman bata zo ba sai yau, mun sha fira a ranar daman can Suwaiba mace ce mai son fira da far'a da haba haba da jama'a, ban yi zaton Abdallah ya kawo ta ba har da ta labarta min cewar shi ya kawo ta amman ya aje ta gurin gate wai yana sauri jaye gurin aiki.
Ta labarta min abubuwa da yawa a ciki har da na rashin son yara da Abdulhamid yake da shi, sannan ta dora min da cewar yawanci maza basa son yayan da ba na su ba, balle kuma Abdulhamid da yake saurayi, tana ta nanata min cewar sai na yi hakurin haka kamar ta san abunda ya fi damu na kenan, duk kuwa da kasancewar ban taba fadawa kowa ba.
  Ganin na dauki waya na kira Abdulhamid na ce yai mana takeaway sai abun yai ta bata mamaki.

“Kar dai ace har yanzu baki fara girkin ba, ko kuwa amarcin ne ya motsa kike jin ba za ki iya dafawa ba?”

Dariya nai kamin na bata masa.

“Wallahi ba haka ba ne, idan na dora girkin baya dahuwa yadda na saka shi haka zan tararda shi kuma ga wuta ga komai amman ba ya yi”

“Too kar dai ace Abdulhamid ma yana da kohi kamar Abban Suhaima, ni ma idan nai masa wani laifin ko kuma na bata masa rai haka zan dafa abinci a ranar ba zai dafu ba sai na bashi hakuri”

Ta fada tana dariya... Ni ma dariyar nai sai dai ba irin ta ta domin ni wani tunanin ne ya zo min, kar dai ace Abdallah ne yai min kohi nake ta samun wannan matsalar?

“Ko da yake shi ma a tawaye ne dole za a samu dukansu suna yi, wata kila wani abun kika masa sai kin ba shi hakuri sannan za ki daidaita, amman fa ni kin san da na dauka ko Abdulhamid ba shi da kohi”

Zancenta ne ya dawo da ni daga duniyar tunani sai na sake yin murmushi a karo na biyu.

“Haka ne ai wani ba a iya ganewa sai idan wani abun ya faru”

“Haka ne”

Sai guraren karfi biyu ya kirata a waya yace ta fito bakin gate yana jiranta, a lokacin Abdulhamid be dawo ba, sai na saka Hijabina na rakata har gurin motarsa bayan na deba mata wasu abubuwan daga turaruka na da kayan kwaliya, gilashin motarsa a sauke yake amman ko da wasa Abdallah be dago ya kalleni ba da na gaishe ma sai ya amsa min a gajarce kamar be san ni ba, bayan sun wuce na dawo ciki gidan ina ta nazarin kalamanta. Daga karshe na yanke shawarar kiran Abdallah nai masa magana, haka kuwa akai bayan Abdulhamid ya dawo mun ci abinci mun yi fira ya fita sallah la'asar ni kuma na nemo number Abdallah ya aika masa kira, ringing tai kamar zata katse sannan ya daga, ban tsaya yi masa sallama ba balle gaisuwa kai tsaye na ce.

“Abdallah magana na ke son mu yi”

Sai na yi shiru bayan na fada masa hakan ina jiran na ji amsar da zai ba ni kamin na dora amman be ce min komai ba har sai da nai zaton ko wayar ta katse ne.

“Idan ka kullace ni da wani abun dan Allah ka kwance, tun da na zo gidan nan kullum nai girki ba ya yi”

“Babu hannuna a ciki”

Ya amsa da muryar da na jita kamar ba ta shi ba.

“Wata kila kana jin haushina ne, ko kuma kana jin bacin rai a kaina ne”

“Ban taba jin haushinki ba, kuma ba ki bata min rai ba, abunda kika aikata ne kawai idan na tuna ina jin babu dadi ne”

“To ka daina jin babu dadin, shiyasa bana iya girkin idan na yi ba yayi, dan Allah ka kwance Kohin da kai min”

Ina iya jiyo saukar numfashinsa kamin ya ce.

“Ban kullace ki da komai ba Halimatu, ke yanzu yar'uwata ce kawai kuma matar dan'uwana, yan'uwanta ta fi gaban wasa ko babu Abdulhamid babu abunda zai shiga tsakanin mu”

Yana fada min hakan ya kashe wayar, a take wani abun marar dadi ya kawo ma zuciyata ziyara. Har na gabatar da sallah la'asar ban daina jinsa ba, bayan sallah isha'i ina kwance saman kujera falo Abdulhamid ya fito daga bedroom ya nufo inda nake kwance, sumbatar kaina yai kamin ya daga ni na tashi zaune sai ya zauna sannan ya kwantar da kaina saman kijinsa yana shafa fuskata.

“Gobe fa ina tunanin zanje Abuja”

Dagowa nai na kalleshi sai na ga murmushi a fuskarsa.

“I know za ki yi mamaki ai, ni ma zuwan dole ya zame min kuma i think idan na samu yadda na ke so zan dawo ranar da na tafi”

A take na marairaice fuska kamar zan masa kuka.

“Mi zaka je yi Abuja?”

“Wallahi wasu takardu ne na ma'aikatar mu da ake son su jibi kuma dole sai an kai su Abuja an saka hannu shiyasa zan je, idan an saka hannu za a ba mu kudi masu dan dama sai mu juya su”

“Tare za mu je?”

“Na so haka amman be samu ba dole mi kadai zan je, amman a promise you idan ban dawo ranar ba washe gari zan dawo”

Har cikin raina na ji babu dadi sai na ji kamar tafiyar shekara zai yi, a ranar na kwanta a jikinsa sosai yadda kasan wata jaririya haka na zama.
Washe gari daga ni har shi mun tashi da wuri, shi ya hada mana abun karyawa ni kuma na shirya masa komai na tafiya, a tare muka karya ina ta narke masa a jiki tun yana daujar abun wasa har shi ma ya so ma jin babu dadi.
Na masa complaining din rashin mai gadin mu sai ya ba ni hakuri ya ce za a samu idan ya dawo bayan yayi min izinin zuwa gida na gaishesu ganin duk na bata rai ya san idan naje zan dan sake sosai, har gurin mota na rako shi nai masa addu'a sosai ta neman tsari da kuma alherin hanya, saboda na san yanayin kasar ana cikin halin fargaba balle tafiyar a mota zai je ba a jirgi ba.
  Bayan tafiyarsa da awa daya na shirya na nufi gidanmu, yan gidan mu sun yi murnar ganina sai zolayata suke wai ina ta shining. A yanayin dana tararda Amal be min dadi ba, wai zawo take da amai yau kwana uku amman basu fada min ba ganin ba su gaza mata a komai ba, na san suna bata kulawa sosai ammn dai ai ya kamata ace sun sanar da ni a matsayinta na yata kuma karama, ko da yake na lura sukansu yanzu yaran idan suka gan ni sai su yi kamar ba su gan ni b babu ruwansu da nuna son zuwa ganina in banda Amal da ta kasa sabawa da kowa har yanzu. Wata kila Mama ta ki ta fada min ne ganin kamar zan iya daga hankalina ga shi kuma Abdulhamid ba son yara yake ba kamar yadda kowa ya lura da hakan.

A ranar Amal a jikina ta wuni lokaci zuwa lokaci sai ta kalleni ta sauke ajiyar zuciya abun har ya soma ba ni tsoro, na so na kaita asibiti duk kuwa da Mama ta fada min sun kai ta ga kuma da aka rubuto mata na gani amman hankalina zai fi kwanciya idan na kaita da kaina. A ranar nai deciding na dauko ta na dawo da ita gidan aurena tare da ni ba in yado washe gari sai na kira Abdulhamid na fada masa cewar na zo da ita saboda bata da jindadi kuma na nemi izininsa na kaita asibiti.
  Bayan magariba na baron gidan da ita na debo wasu daga cikin tufafinta, har na iso gida babu komai a zuciyata sai tausayinsa, wata kila har da kewata ta sakata wannan ciwon saboda yadda ta saba da ni sosai. A gaskiya ranar na ji babu dadi marar misaltuwa, wani abun mamaki da muka dawo gida tare sai ta dan sake Allah ya kawo mata sauki har ta labari take ba ni wai Adnan ya dake ta ya zageta, sai dai idan an taba jikinta ina jin zafi a can gidan bata cin komai amman a nan da na bata abaya sai ta ci ta kwanta a jikinta ta tafe sosai kamar wata kyanwa.
  Misalin tara da rabi na shiga kitchen na gwada dora indomie, wani abun Allah sai gashi ta dahu kamar yadda na saba dafata, ban san lokacin da na daka tsalle na dibe ba dan murna. Ta window kitchen na hango dorowar mutum ta gate, ta hanyar hasken fitulun da ke cikin gidan ne na iya gane wanda ya diron yana sanye da bakaken kaya fuskarsa ma a rufe da bakin fuska. A furgice n rugo da gudu na yo falo sai an samu Amal har ta yi  bachi da sauri n rufi kofar falon na rufe zuciyata na bugawa kamar zata fado, abunda ban sani ba ashe na rufe falon da daya daga cikinsu ba, ban lura da hakan ba sai bayan an rufe kofar na yi baya sai na hango mutum ya fito bayan labule rufe da fuska kamar wacan yana nuna ni da bindigar da ke hannunsa.


Khadija Abubakar Alkali

Continue Reading

You'll Also Like

5.5M 723K 198
Main Story ( Completed ) ~~~~~~~°°°°°~~~~~~~ Title - Transmigrated into the film empreor's death-seeking finance (穿成影帝作死未婚夫) Author - Lin Ang Si (林盎...
378K 17.3K 65
Love is a thing that if you'll find, never can see it but you will meet this nearly or by chance.
123K 14K 103
transition novel
12.4K 2.4K 64
Ƙalubalen ZAWARCI a kasar hausa, da hanyan kawo gyara cikin kalubalen da ɗiya MACE take fuskanta kan ZAWARCI sanadin mutuwar miji ko kuwa kaɗdarar sa...