52

4.5K 387 99
                                    

EL'MUSTAPHA

Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers

Fertymerh Xarah💞

52

Bayan kwana biyu, jiddah ta warware sosai sai dai rashin kuxarin jiki,

'Anty ikram Ma sunxo tare da wani kawun jiddah.

Sosai dr merah ke kula da jiddah musamman qafarta, sun xama friends da el'mustapha ko da yaushe suna tare a office, har yake baiwa el'mustapha labarin sa da Afiya.

Hajiya bani ruwan tea na sha, cewar jiddah tana kallon ta,

Hajiya ta tashi goye da jaririyar ta hada mata bayan ta xauna kusa da ita,

Magana xamu yi jiddah ta fahimta, bana so naga abinda xai cutar dake ko kadan.

Jiddah ta tattara hankalinta da nutsuwar ta tana kallonta,

Hajiya tace meke tsakanin wannan yar aikin taki da mijinki?

Jiddah ta qara kallonta cikin faduwar gaba tana bude idanuwanta, ta ajiye Cup din tea tana fadin, me kika gani hajiya?

Tambayar ki nake yi kibani amsa,

Cikin rawar murya  jiddah tace nima ban sani ba hajiya,

Ba ina gayamaki bane dan ki tada hankali ki, amma kisani wannan karon ko mutuwa xakiyi baxan taba yarda ki aurawa wata mijinki ba, tun da na lura ke Sam baki san ciwon kanki ba sai haquri, ina ji ranar da xaa shiga dake aiki har kina bata amanar ya'yan ki da mijinki, meke damun kine jiddah.

Jiddah tace hajiya banan tana da kirki bana xaton xata cutar dani ko wani nawa shine dalilina na bata amanar yarana, amma maganar el'mustapha cikin xafin ciwo ne ban san na nata amanar sa ba kuma ba wai ina nufin ta so shi ba hajiya.

Koma dai menene na riga na gano banan tana son mijinki, kuma kinji na gayamaki wannan karon baki isa ba, kuka taso da uwani tun kuna yara ta cutar dake ballantana wata bare,

Jiddah taja numfashi a ranta tana cewa hajiya baxata gane ba wani bare yafi dan uwa kuma ba duka aka taru aka xama daya ba.

Amma hajiya meyasa kika ce tana son el'mustapha, ni na dauka shine kadai ke son ta.

Hajiya ta xare ido cikin mamaki, tace kina nufin wai el'mustapha yana son banan? Ya akayi kika yi wannan saken jiddah, taya xaki reni yarinya da hannunki ta aure maki miji, wai ke meke damun ki ne, wace irin mutum ce ke, ban taba sanin wata mace mai hali irin naki ba jiddah, kin fiye tausayi da sanyin xuciya wanda shine ke cutar dake kuma shine ya kawo ki matsayin da kike a yanxu.

Jiddah ta soma kuka tana fadin, ba laifina bane hajiya, bansan yaushe ya fara son ta ba, nagano hakan bayan dawowa ta daga batan da nayi kuma el'mustapha ya rantse min babu soyayyarta a xuciyarsa sai dai ban sani ba akan ita banan.

Hajiya tace to bari kiji ban san komai akan gidan ki ba amma a waya da naji banan nayi na fahimci komai, kin bata auren qanin aminiyar ki, tana waya naji tana bashi haquri akwai wanda take so tuntuni kuma yanxu tana da tabbacin xata same shi amma ya rufa mata asiri kada ya gayamaki dan bata son fushin ki ko kadan.

Bansan me yace da ita ba naji tana roqonsa da magiya cewa xai iya haqura da ita har ya sami wacce ta fita.

Ban taba kawo el'mustapha take so ba sai a jiya da dare, ta kwana kiran el'mustapha a barcinta wataqila ma yusrah ta ji ta ban sani ba, yau da safe ban mata mgn ba amma daga irin kallon da take wa el'mustapha daban ne da wanda take mana, na lura duk inda yayi idanunta na kansa bai Ma san tana yi ba.

El'mustapha Where stories live. Discover now