14

3.5K 167 1
                                    

*EL_MUSTAPHA*


HASKE WRITER'S ASSOCIATION
(home of experts and perfect writers)

Fertymerh Xarah 💞

13

Suna tsaka da firar su sai ga Uwani taxo dauke da qaton tire a hannunta, dawowar ta daga School kenan lokacin tana S.s.2,

Har qasa ta gaida sa cikin satar kallon sa, tana yaba sa a xuciyarta, cikin sakin fuska yake amsa mata yana kallonta kafin ya maida dubansa ga jiddah,

Gwiwoyinta sukayi sanyi, xuciyarta ta karaya, duk wata soyayya da Allah ya halitta a xuciyarta ta haďu ta tattare waje ďaya taji ba wani wanda take so a duniyar nan sama dashi batasan dalilin hakan ba amma haduwar idanun su ne sila.

bayan ta fito ta nufi cikin gida.

Hajiya kinga mijin anty jiddah kuwa?

'me akayi? Hajiya ta tambayeta bayan ta tsaida idanunta akanta.

Babban mutum ne fa, ya hadu amma da ganinsa baxai rasa mata da ya'ya ba.

Alhaji yace baida mata, police ne ai, nima yanxu yake gayamin.

Police fa hajiya? Me anti jiddah xatayi da 'Dan Sanda, mtsewwwww.

Bana son kinibibi da iyayi, d'an sanda ba mutum bane kinsan shi wane irin muqami ne atare dashi? Kar na qara jin wannan mgnr a bakinki.

Ta tabe bakinta batare da ta qara mgn ba, uniform na jikinta ta soma cirewa amma har lokacin xuciyarta fuskarsa take hasko mata, duk ta tuna dashi sai gabanta ya fadi har lokacin da jiddah ta dawo bayan ya tafi.

Kallo daya xakayiwa jiddah ka tabbatar tana cikin farin ciki, sai murmushi take, hajiya nayi mata dariya tana tsokanarta, Matar dan sanda.

Ranar jiddah da el'mustapha baxaa ce komai ba sai faman juye juye suke a gado tare da kewar juna, suna jin wani sabon al'amari a tare dasu.

A gurguje pls

Ana gab da bikinsu lokacin uwani ta jewa hajiya tana kuka, ita a duniyar ba wanda take so kamar el'mustapha.

Batare da tunanin komai ba hajiya ta dauke ta da Mari.

Kina da hankali kuwa Aisha, kinsan me kike mgn akai, mijin yar uwarki kike so, kul na qara jin wannan mgnr ko kika nuna wata alama da jiddah xata gane kina son mijinta wlhy da ni da ke ne a gidannan kuma har abban ku sai na fadawa.

'kiyi haquri hajiya, bansan yanda xanyi ba tun farkon ganina dashi na kasa cire sa a xuciyata ki taimaka hajiya kisa baki ya aure ni tare da anty jiddah tun..... Saukar Marin da taji a kuncin tane ya hanata qarasa mgnr ta, kallonsa take cikin mamaki bayan ta dafe kuncinta da tafin hannunta.

'Ashe baki da hankali ban sani ba Uwani? Mijin jiddah kike so yar uwarki? Wallahi na qara jin wannan maganar a bakin ki ban yafe maki ba, ni ba mutumin banxa bane da xanci amanar marainiyar Allah, kin manta dani dake da mahaifiyar ki a inuwar ta muke, dukiyar tace fa, bani da buri a duniyarnan na ganin na aurar da jiddah ga miji nagari kuma alhamdulillah na samu, ke baxaki sani jin kunyar idon duniya ba, kuma ki kiyayeni wlhy, ya juya ya fice da sauri.

Hajiya ma bata qara magana ba ta barta nan cikin qunci.

Ranar uwani tayi kuka kamar me, el'mustapha ya riga yayi mata nisa ta riga ta rasa shi a karo na farko amma bata debe tsammani da cewa watarana sai ta xamo matar el'mustapha.

Jiddah tayi juyin duniya tana tambayar uwani meya kumbura idanunta kukan me take gashi harda bakinta ya kumbura taqi magana,

Taje ta tambayi hajiya cikin nuna damuwa da halin da take ciki
Me akayiwa uwani ne take kuka tun daxu hajiya, kinga yanda fuskarta ta kumbura kuwa?

El'mustapha Where stories live. Discover now