23

3.9K 323 20
                                    

EL'MUSTAPHA

Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers

Fertymerh Xarah💞

23

Dogon Numfashi taja tana kallon bayansa har lokacin da ya fice,

Tana ganin Allah baxai kamata da laifin komai ba tunda alheri tayi niyar aikata, bata ga laifinta anan ba illah son xuciyarta da tagani, yes da gaskiyar el'mustapha da yace ta shiga haqqinsa ta tursasa xuciyarsa auren abinda baya so, insha Allah komai xai wuce kamar baa yi wannan rigimar ba, ta cigaba da duba wayar amma hankalinta baya jikinta.

*

Uwani ki shirya kije gida inda su hajiya ki roqi gafarar su, su sanyawa auren ki albarka domin kina buqatar hakan saboda babu mai goyon wannan auren naki.

'ni har sai naje na roqesu gafara sai kace mutuwa anti.

'baxakije ba kenan?
'A'ah ni bance haka ba,
'ki shirya yau kitafi, driver xai kaiki ya dawo shi kadai, kwana biyu xakiyi acan har dangi Ma kije, rayuwar aure da kike gani ba abin wasa bane.

Uwani bata qara mgn ba amma xuciyarta har wani tuqiqi take, haka taje ta hada kayan tana qunquni ko sallama batayi da jiddah ba ta fice,

'au inda ban fito ba ashe baxaki sanarda ni kin tafi ba, kina min wannan abin uwani kuma kike son mu xauna lafiya dake uwani? Tana jin haka tayi saurin russunawa,

Kiyi haquri anty jiddah, yanayin jikina ne kesani kuya akan komai amma xan kiyaye.

Ga wannan ki baiwa hajiya kuma ina gaida abba, uwani ta karbi saqon hade da jefawa cikin handbag din ta, murmushin yaqe tayi tana kallon jiddah.

'Anty jiddah na tafi kimin addua,

Allah ya kiyaye hanya ya kaiku lafiya,

Amin ta juya ta fice.

*

Sanda uwani ta iso gidan taga canji sosai wanda yayi matuqar bata mamaki daga iyayenta, ashe da gaske jiddah take mata basu farinciki da auren ta?

'Abba har da kai baka son auren ne? Ta tambaya tana kallonsa,

'tunda ke kina so kije kiyi, duniya ce uwani kije gaki gata wanda bai xo cikinta ba Ma jiransa take, duk kika cutar da rayuwar jiddah Allah baxai barki ba kuma xaki gani, Allah ya gani bana son auren nan bana farinciki dashi kuma baxan taba xama waliyyin daura shi ba, tunda bamu isa mu hanaki ba kije kiyi duk yanda kike so da rayuwarki, ya tashi ya fice ta bisa da kallon mamaki a xuciyarta tace banda abin abba shi kadai ne datijjo a duniya da xai xama waliyina, ko dashi ko ba dashi ba ai dama auren xanyi, a fili kuwa tabe bakinta tayi ta juya tana kallon hajiya tana cewa,

Iyayen yanxu idan baka nuna ka isa da kanka ba kwarar ka suke suci amanar rayuwar ka.

Kika ce me? Hajiya ta tambaya tana kallonta,

Uwani ta washe baki hade da gyara xamanta, aa hajiya wace ni d'iyar Malam Adamu addua ce kawai nake masa.

Addua indai daga gare kice bama buqata domin ba karbabbiya bace,

'hajiya kinsan gaibu kenan, gayamin dalilin da yasa baxata karbu ba tunda nidai musulmace, sallah biyar kike yi nima ita nake yi.

Jikin hajiya yayi sanyi, abin uwani ya soma bata tsoro da mamaki, a da uwani xata maida mata magana amma cikin qunquni ynxu kuma abin yayi tsauri ta kai ido da ido uwani xata iya gaya mata magana.

Ni dai kam uwani lafiya na gama rayuwata da iyayena har suka mutu kuwa,

'nima lafiya qalau xan gama daku, Allah ya nuna mana lokacin.

El'mustapha Where stories live. Discover now