38

4.5K 395 90
                                    

EL'MUSTAPHA

Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers

Fertymerh Xarah💞

38

Ba abinda ke tashi a gidan sai sautin kida da raye raye, abokansu daga wani gu sai xuwa suke, kowane da makamin sa hannu, suna tafe suna shan giya wasu na xuqar sigari.

Ko taron me suke yi yau? Kurma yaci gayu cikin wasu qananan kaya, wando three quarter na black jeans, rigar farar mai qaramin hannu, sai qafafunsa dake sanye da sneakers👟, baqin glass ne sanye a idanuwansa, sai wata shegiyar hula da ya dora akan sa, ya gogu fa sai Ma kun ganshi😀

Yana riqe da qugun wata budurwa tashi, bra ce kawai sanye a jikinta sai wani guntun buje ko pant babu a cikinta, tunda yasa hannu qasan bujen nata hankalinsa ya nemi gushewa,

Ta qara banqaro kirjinta tana xuqar sigari, hannunta daya na kan hannun kurma dake cikin bujen nata,

Baxan jure kallon wannan shashanci ba gwanda naje nayi kallon masu d'an kamfai🤧.

Har lokacin jiddah na rungume da arham, kanta yayi nauyi sosai, ga jiri da take gani idanunta sunyi jawur saboda kuka kuma har lokacin bakinta bai mutu ba wajen kiran wanda xai taimake ta.

Tana jin hayaniyar su, tana jin yanda suke shewa,

Help... Somebody help shine abinda goga yaji jiddah na furtawa lokacin da ya shigo da tashi budurwar.

Bai san wainar da ake toyawa ba ya qarasa yana fadin,

Ina kika sami yaro, ta bude idanu da kyar tana kallonsa, tana ganin goga ne jikinta ya dauki rawa saboda yana matuqar tausaya mata da taimakonta.

Yaro nane ya kashe min shi, ka taimaka ka kaimin shi asibiti, dan Allah ka taimakeni kada ya mutu.

Ya taba arham yana kallon inda kurma ya harbesa,

Shi wannan yaron menene laifinsa, meyasa kurma yake marar imani ne,

Numfashinta ya soma sama sama,

Tace ka taimakeni, ka kaimin shi asibiti kada ya mutu, dan Allah ka taimakeni.

Ina je dashi asibiti xaa iya kamani ai is very risk idan baki sani ba, bari naje na kira maki likitan dake duba mu a duk lokacin da aka harbi wani a cikin mu, ki kwantar da hankalin ki yanxu xan dawo.

Bai jira cewar ta ba ya tashi ya fice da gudu ko budurwarsa bai waiwaya ba cikin tausayin jiddah.

Jiddah ta qara rungume arham banda sumbatar sa ba abinda take sai kuka.

*

Suna qoqarin saka uwani motar sai ga su hajiya da abba, sunxo yiwa el'mustapha gaisuwar mama, sunyi masa a waya basu sami damar xuwa ba sai yanxu.

Hajiya ma jiki yayi nauyi, ciwon qafafu take fama dashi.

'Abba yace lafia el'mustapha na ganku haka.

El'mustapha bai yi magana ba, akwai kunya sosai tsakanin sa da surukin sa, ibrahim ne yayi masu bayanin komai.

Inna lillahi wa Inna ilaihir raji'un, iyayen suka juya suna kallon uwani tana tsaye abinta ba alamar nadama ko wani dana sani a tare da ita, ta dauke kanta gefe daga kallonsu tana tunxuro baki.

Hajiya kam har da kuka,

Tace duk yanda nayi dake uwani akan idan kina da sa hannu a batan jiddah kika musa, kika bar baiwar Allah da ciki cikin uquba, anya uwani xaki ga annabi kuwa, kwata kwata babu imani a xuciyarki, baxan taba yafe maki ba kije gaki ga duniya.

El'mustapha Tahanan ng mga kuwento. Tumuklas ngayon