49

4.1K 375 60
                                    


Fiye da minti goma xaune a wurin ba wanda yayi magana a cikin su.

Tashi el'mustapha yayi ya fice daga office din a fusacce, Dr Merah yabi bayansa da kallo yana tabe baki.

Yana fitowa hajiya da anty yusrah suka tare sa,

Ya akayi ne el'mustapha? An nasara ko?

Ya bata fuska yana Jan tsaki mai cike da takaici,

Taya xan sani wannan likitan mai baqar sarautar tsiya yaqi yamin mgn ballantana naji halin da jiddah take ciki.

Hajiya tace oh Allah munga sun fito da ita a lullube, hankalina ya kasa kwanciya el'mustapha, kayi haquri kaje ka qara tambayarsa meke faruwa da yar'mu.

El'mustapha ya shafi sumar sa, baxai je ya qara tambayarsa ba ai komai mulki da sarautar likita baxaiyi akan patient din sa ba, sai ya koma fada yayi wannan mulkin amma baa asibiti ba, ya furxar da iska a bakinsa yana kallon hajiya.

Ina suka je da jiddah,

Wani daki suka ajiye ta cewar hajiya tana tafiya suna biye da ita a baya.

Ta window suke kallonta, baxasu iya gane komai a tare da ita ba kasancewar tana nesa dasu sosai.

Indai tana raye alhamdulillah, ba dole sai ta rayu da qafar ba, xan iya xama da ita a hakan, ya juya ya soma tafiya a hankali, anty yusrah tabi bayansa.

Hannunsa ta riqo bayan ta kira sunansa,

Juyowa yayi yana kallonta ga mamakinta idanunsa cike suke da kwallah,

Tace meyasa el'mustapha, jiddah xata tashi insha Allah kuma da qafafunta, ganinta haka kwance ba shi xai saka mu cire tsammanin daga gare ta ba, be a man pls, idan kai da kake namiji kayi kuka mu kuma muyi me?

Yace kin lura da jiddah bata motsi anty yusrah, baki ga yanda suka ajiye ta ba kamar gawa, meyasa suka ajiye ta anan, just tell me anty yusrah me suke nufi da jiddah, baxan yarda ba idan suka kashe min mata.

Gabanta ya tsananta faduwa, taja hannunsa da suka suka fito cikin asibitin ganin yanda mutane suke kallonsu, juyo dashi tayi hade da saka tafin hannuwanta ta riqo fuskarsa tana kallon sa.

Me yake damun ka el'mustapha? Yaushe ka canxa ka dawo haka mai xafin rai, da nasan jiddah da xafin rai da nace daga ita ne amma jiddah kowa ya san ta da sanyin rai, idan mutuwa jiddah tayi meyasa xakayi qarar su, meyasa baxakayi tawakkali a xuciyar ka ba, meyasa kake tunanin baxaka iya rayuwa sai da jiddah ba, ka manta wanda yayi ta yayi mu ya fimu son ta, baka tunanin lahirar ta fiye mata wannan duniyar da duk abinda ke cikinta, ko kana nufin baxaka yi imani da abinda Allah ya yanke akan ka ba, mama ta mutu ka haqura ballantana jiddah, wace irin shaquwa ce tsakanin ka da ita wacce bakayi da mama ba?

A hankali ya sauke ajiyar xuciya bayan ya janye fuskarsa daga riqon da tayi masa, kallon ta yayi,

But why wannan likit..... Tayi saurin katse sa,

Is ok ni xanje na tambayesa, wait for me, ta juya tana tafiya, binta yayi da idanu jikinsa a sanyaye kafin ya nemi guri ya xauna, mutane yake kallo dake shige da fice.

Assalamu Alaikum, tayi sallama cikin muryarta mai sanyi,

Batare da ya dago ba ya amsa sallama cikin isa da taqama,

Bata jira ixini ba ta shiga ta xauna tana kallonsa, duk abin nan da take ko sau daya bai kalle ta ba, ya maida hankali sosai akan laptop dinsa,

Ta tabe baki bayan taja numfashi,

Tace sannu da aiki, naxo ne kan maganar patient din da muka kawo Hauwa Ahmed, ko a wane hali take ciki.

Kallo daya yayi mata ya maida hankalinsa kan abinda yake yi batare da yayi magana ba kuma bashi da niyar yin haka.

El'mustapha Wo Geschichten leben. Entdecke jetzt